Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-07@13:51:02 GMT

Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano

Published: 7th, July 2025 GMT

Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano

Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya reshen jihar Kano, ta bayyana cewa Fursunoni 58 suna rubuta Jarrabawar Kammala Sakandare ta Kasa NECO ta shekarar 2025.

Wannan ci gaba ya samu ne bayan biyan kudin rajista da gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta yi.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Musbahu Kofar-Nasarawa, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai a Kano.

Ya ce wannan karamci na gwamnatin jihar Kano shaida ce ta jajircewarta wajen kula da walwalar fursunoni, gyaran dabi’unsu da kuma dawo da su cikin al’umma yadda ya kamata.

Biyan kudin rajistar jarrabawa da gwamnatin Kano ta yi alama ce ta jajircewarta wajen samar da dama ga fursunoni domin su gyara rayuwarsu su koma cikin al’umma, in ji shi.

Hukumar ta bayyana godiya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa goyon bayansa da hadin kai da yake bayarwa ba kakkautawa.

Ya ce wannan mataki zai karfafa gwiwar fursunoni wajen daukar karatu da muhimmanci tare da ba su wata sabuwar dama ta samun ilimi da kyakkyawar makoma.

Musbahu Kofar-Nasarawa ya kara da cewa, hukumar gyaran hali ta Kano ta kuduri aniyar samar da kyakkyawan yanayi domin gyaran hali da ilimantar da fursunoni.

Muna alfahari da samun goyon bayan gwamnatin Kano a wannan kokari,” in ji sanarwar.

Ya kuma ce jajircewar hukumar wajen gyaran hali na bayyana ta hanyoyin da take bi wajen samar wa da fursunoni damar samun ilimi da sauran damammaki da za su taimaka musu su gyara rayuwarsu su koma cikin al’umma.

 

Abdullahi Jalaluddeen 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ƙalubalanci jagoran ’yan bindiga Bello Turji, wanda ke neman sulhu, da cewa idan da gaske yake yi, to ya sako duk mutanen da ya yi garkuwa da su, ya daina kai hare-hare, kafin ta zauna da shi.

Mashawarci na musamman ga gwamnan Sakkwato a kan sha’anin tsaro, Kanar Ahmed Usman ne ya bayyana hakan baya yaɗuwar wani bidiyo da Turji ya saki, wanda a ciki yake neman a yi tsakaninsa da gwamnati.

Ɗan ta’addan wanda ya addabi yankunan jihar da makwabta ya saki bidiyon ne kwanaki kaɗan bayan jami’an tsaro sun kashe wasu gaggan kwamandojinsa da Faransa sama da 100.

Kamar Ahmed, a cikin wata sanarwa ya bayyana cewa babu yadda za a tabbatar cewa neman sulhun Turji ba ta fatar baki ba ne, sai idan ya dakatar da kai wa al’ummo hare-hare saki duk mutanen da ya sace ba tare da ɓata lokaci ba.

Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a?

“Idan har da gaske yana neman sulhu, to sai ya nuna a aikace, ya dakatar da hare-hare kan ƙauyuka tare da sakin duk mutanen da ke hannunsa ba tare da sharaɗi ba,” in ji Kanar Ahmed, wanda ke jaddada muhimmancin tsaron rayuka da lafiyar da kuma dukiyoyin al’umma ga gwamnatin Jihar Sakkwato.

Don haka ya, “Ba za a iya yin wata sahihiyar tattaunawar sulhu da za a yi a samu a yayin al’ummomi suke zaune cikin tsoro kuma ’yan ta’adda suke yin garkuwa da mutane.

“Matakin farko na samun zaman lafiya shi ne gina yarda ta hanyar ɗaukar ƙwararan matakai a aikace,” in ji jami’in gwmanatin.

Ya jaddada aniyar gwamnatin ga tabbatar da tsaro da zaman lafiya, amma ba za ta lamunci ta’addancibda sauran miyagun laifuka ba.

Sa’annan ya yi kira ga al’ummomi da shugabannin addini da sarakunan gargajiya da ƙungiyoyin faren hula su mara wa shirye-shiryen zaman lafiya baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato
  • Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
  • Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu
  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano
  • Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano
  • Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus