Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ce, “A daren yau mun koma yaƙi a Gaza.”

Hamas ta zargi Isra’ila da karya yarjejeniyar tsawon kusan wata biyu, tana mai cewa hakan na barazana ga lafiyar fursunonin da ke tsare a Gaza.

Amma Isra’ila ta ce Hamas ce ke ƙin sakin fursunonin tare da bijirewa yarjejeniyar sulhu.

A lokacin yarjejeniyar, an yi musayar wasu fursunonin Isra’ila da Falsɗinawa da ke tsare a gidajen yarin Isra’ila.

Sai dai har yanzu kimanin mutum 59 daga cikin fursunonin Isra’ila suna hannun Hamas, kuma ana zargin rabinsu sun mutu.

Rahotanni sun nuna cewa Amurka ta amince da harin da Isra’ila ta sake kai wa Gaza, inda ƙasashen biyu suka sha alwashin yaƙar Hamas, ‘yan tawayen Houthi na Yemen, da sauran ƙungiyoyin da suka ɗauki makamai.

Kakakin fadar White House, Karoline Leavitt, ta yi gargaɗin cewa, “Hamas da Houthi za su fuskanci sakamako mai tsanani. Duniya za ta girgiza.”

A cewar Ma’aikatar Lafiya ta Gaza, aƙalla Falasɗinawa 48,577 ne suka mutu, yayin da Ofishin Yaɗa Labarai na Gaza ya ce adadin ya haura 61,700, ciki har da waɗanda ke birne a ƙarƙashin gine-ginen da aka rushe.

Yaƙin ya fara ne bayan harin da Hamas ta kai kudancin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba, 2023, wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla Isra’ilawa 1,139 tare da tsare da sama da mutum 200.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Hare Hare Isra ila yaƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama

A farkon wannan shekarar da ta gabata, Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, a wani taro ya bai wa kungiyoyin na Sufurin Jiragen Sama tabbacin cewa, Gwamnatin Tarayya za ta tabbatar da bi ka’ida wajen sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman kasa.

Keyamo ya kuma bai wa shugabannin kungiyoyin tabacin cewa, suma a sanya kan batun na yarjejeniyar ta sayar da hannun jarin Tashoshin Jiragen Saman.

Kazalika, ba su tabbacin cewa, zai umarci hadiminsa domin ya ci gaba da sanar da shugabannin kungiyoyin kan abinda ke tafiya game da yarjejeniyar.

Sai dai, a jawabin da shuwagabbin kungiyar da kuma na ma’aikatan suka gabatar a wani babban taronsu a shalakwar Tashar Jiragen Sama da ke a jihar Legas, sun soki Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, bisa zagaye shugabannin kungiyoyin kan batun na jarjejeniyar.

A jawabinsa shugaban kungiyar ma’aikatan zirga-zirga ta jiragen sama na kasa NUATE Kwamarade Ben Nnabue ya yi kira da sake sabon lale kan batun na yarjeniyar musamman domin a bai wa sauran masu ra’ayin shiga cikin yarjejeniyar.

“Ya kamata a sake faro yarjejeniyar tun daga farkonta, domin a bai wa sauran ‘yan Nijeriya damar shiga cikin yarjejeniyar,”Inji Shugaban.

Nnabue ya ci gaba da cewa, a matsayinsu na shuwagabannin kungiyoyin sam ba su da wata masaniya game da wannan yarjejiniyar da da Gwamnatin ta kulla.

Ya kara da cewa, hatta shuwagabannin kungiyoyin kwadago ba a sanar da su, game da yarjejiniyar ba, amma sai kawai muka ji, Ministan Sufurin Ma’aikatar Jiragen Sama Festus Keyamo, sanar da cewa, Majalisar Zartwar kasar ta amince da wannan yarjejeniyar, musamman ta Tashar Jirgin Sama na jihar Enugu.

“Muna son mu sanar da duniya cewa, dole kafin a gudanar da duk wata yarjejniya a fara tattaunawa da shuwagabbin kungiyoyin kwadago tukunna, ” A cewar Kwamarade Ben.

Ya sanar da cewa, hanyoyin da ake bi na gudanar da wannan yarjejeniyar, cike take da kura-kurai domin ba mu da wata masaniya ko an bayar da talla ga manyan Jaridun kasar nan kan batun na yarjeniyar.

“Tashoshin Jiragen Sama na kasar nan, mallakin ‘yan Nijeriya, a saboda haka ba za ta sabu kawai a cikin dare daya mu ji an yanke shawarar cewa, akwai wasu ‘yan lele da ake so su kadai a yi yarjejeniyar da sub a, domin kamata ya yi ba bar abin a bude domin suma ‘yan kasar, su gyada ta su sa’ar, a saboda haka, muna bukatar a soke wannan yarjejniyar har sai idan an bi ka’idar da ta dace, “ Inji shugaban.

Shi ma a na sa bangaren shugaban kungiyar kwarru ta ANAP Kwamarade Alale Adedayo, ya yi tir da hanyoyin da Ministan ya bi domin yin wannan yarjejeniyar ba tare da janyo shugabannin kungoyoyin ba kamar yadda ya yi masu alkwari a baya.

Kwamarade Adedayo ya bukaci da sake sabon lale kan batun wannan yarjejeniyar, musamman domin a tabbatar da an bi ka’aida da kuma yin gaskiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani
  • Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi
  • Sin Ta Soki Lamirin Amurka Dangane Da Wanke Japan Daga Laifukan Da Ta Tafka Yayin Yakin Duniya Na Biyu
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
  • Hamas ta aike da wasikar yabo ga Yemen kan goyon bayan Gaza
  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida 
  • Wakilan Hamas sun isa a Alkahira don tattaunawa kan sabuwar shawarar tsagaita wuta a Gaza