Malamin Addinin Musulunci Yayi Kira Da Ayi Gaggawa Gyaran Hanyar Zamfara
Published: 7th, July 2025 GMT
Wani malamin addinin musulunci a jihar Zamfara, Sheikh Mohammed Tukur Sani Jangebe, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar Zamfara da su gaggauta gudanar da kananan gyare-gyare daga mahadar Maru –Mayanchi – Maradun, da ke kan hanyar zuwa wani yanki na karamar hukumar Talata Mafara.
Ya ce mummunan yanayin hanyar yana ci gaba da haifar da babban kalubale ga matafiya tare da fallasa su ga hare-haren ‘yan bindiga a kan hanyar.
Sheikh Jangebe ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake zantawa da wakilin gidan rediyon Najeriya a Gusau babban birnin jihar Zamfara.
Ya bayyana cewa babbar hanyar Maru zuwa Talata Mafara ta samar da ramuka sama da dari, wadanda ke hana zirga-zirgar ababen hawa.
A cewarsa, hanyar ta zama hanya mai hatsarin gaske saboda yawaitar ‘yan fashi da garkuwa da mutane.
Malamin ya bayyana cewa, duk da cewa gwamnatin tarayya ta bayar da kwangilar tagwayen hanya na titin Zaria zuwa Funtua zuwa Gusau zuwaTalata Mafara zuwa Sokoto amma har yanzu aikin bai kai ga tsallaka babbar hanyar Maru zuwa Talata Mafara ba.
Sheikh Tukur Jangebe ya bayyana cewa, dubban matafiya sun dogara ne da hanyoyin sufuri, kasuwanci, kiwon lafiya, noma, ko sauran muhimman ayyuka yayin da hanyar ita ce babbar hanyar da ta tashi daga Zamfara zuwa Sokoto har zuwa jihar Kebbi.
“Abin takaici, hanyar da ta tashi daga Bungudu ta bi ta Maru, Mayanchi, mahadar Maradun, har zuwa wani yanki na Talata Mafara, gaba daya ta lalace.
Sheikh Jangebe ya jadadda cewa, rashin kyawun hanyar yana haifar da fasa-kwaurin manyan motoci a lokuta da dama da kuma kara yawan yin garkuwa da mutane, domin masu aikata laifuka suna amfani da jinkirin da aka samu wajen yi wa matafiya kwanton bauna.
A cewarsa, direbobin ‘yan kasuwa da sauran masu ababen hawa na iya shaida rashin kyawun hanyar.
“Ina so in yi amfani da wannan damar in yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta hannun Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya da ta gaggauta gudanar da kananan gyare-gyaren gaggawa a kan hanyar domin saukaka radadin mutanen da ke tafiya a cikinta a kullum.”
Sheik Tukur Sani Jangebe ya kuma ce shigowar damina ta bana ya kara ta’azzara yanayin hanyar, tare da samar da karin ramuka da kuma sanya tafiye-tafiyen da ke da hadari.
Malamin ya kuma yi kira ga Gwamnonin jihohin Kaduna, Zamfara, Katsina, da Sokoto da su hada kai tare da gyara duk wani bangare na babbar hanyar da ke bukatar kulawa cikin gaggawa, har sai an kai ga aikin da ake yi a bangaren domin sake gina shi na karshe.
Ya bukaci ma’aikatar ayyuka ta tarayya da ’yan kwangilar da ke tafiyar da aikin hanyar da su hanzarta gudanar da aikin domin ganin an kammala shi a kan lokaci.
AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: gyaran Hanya Zamfara babbar hanyar Talata Mafara
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato
Al’ummar yankin sun bayyana cewar matsalar tsaron ta gurgunta tattalin arzikin yankin musamman ayyukan noma wanda ya sa ɗaruruwan mutane da dama neman mafaka a sansanin gudun hijira a Sakkwato da makwabtan jihohi.
Dasuki ya bayyana cewar a ranar 12 ga Augusta 2025, ‘yan ta’adda sun shiga mazaɓar Fakku a karamar hukumar Kebbe tare da kashe mutane biyar da garkuwa da mutane 28 da satar shanu 37.
“Haka ma a ranar 15 ga Agusta, ‘yan bindigar sun kai farmaki mazaɓar Sangi tare da tilastawa jama’a neman mafaka a Kuchi da Koko a jihar Kebbi. Bugu da kari a ranar 18 ga Agusta ‘yan ta’adda sun afkawa mazabar Ungushi tare da kisan mutane biyu da garkuwa da mutane bakwai tare da asarar dabbobi.”
Dasuki ya kuma bayyana cewar, mazaɓun Jabo a karamar hukumar Tambuwal da Tambuwal/Shimfiri suna fuskantar kalubalen tsaro da ke bukatar agajin gaggawa.
Dan majalisar ya bayyana halin kuncin da al’ummar yankin ke ciki, ya ce munanan hare- haren sun tarwatsa kwanciyar hankalin al’umma, jama’a sun kauracewa garuruwa, haka ma yara sun daina zuwa makaranta, a yayin da manoma sun dakatar da zuwa gona a bisa ga tsoron ta’addancin.
A bisa ga amincewa da kudirin, majalisar ta bukaci rundunar sojin Nijeriya da rundunar ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su gaggauta tura jami’an tsaro domin karfafa kai hare- hare a yankin Kuchi a karamar hukumar Kebbe da yankunan karamar hukumar Tambuwal domin kare rayuka, dukiyoyi da gonaki.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA