Aminiya:
2025-11-12@20:48:24 GMT

DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna

Published: 19th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A karshe dai abin da wasu ke hasashen zai faru a Jihar Ribas ne ya faru inda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya saka dokar ta baci a jihar kuma ya dakatar da zababben gwamnan da mataimakiyarsa da kuma ’yan majalisar dokokin jihar.

Sai dai bayan wannan doka da shugaban kasar ya ayyana ne al’umma da dama ke ta bayyana mabanbantan ra’ayoyin kan wannan batu.

A yayin da wasu ke bayyana cewa dama tuni abin da shugaban kasar yake bukata ke nan, wasu kuwa ke bayyana cewa shugaban kasar ma ba shi da ikon dakatar da zababben gwamna.

NAJERIYA A YAU: Yadda Mai Karamin Karfi Zai Mallaki Muhalli Da Kudi Kalilan DAGA LARABA: Asalin Tashe Da Tarihinsa A Ƙasar Hausa?

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan shin ko Dokar Kasa ta bai wa shugaban kasa karfin ikon dakatar da gwamnan jiha dama ’yan majalisar dokokin ta?

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dokar Dokar Ta Ɓaci siminilaye Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Abdulmumin Jibrin ya koma APC wata 2 bayan NNPP ta dakatar shi

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Ƙiru da Bebeji daga Jihar Kano, Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ya sauya sheƙa zuwa Jam’iyyar APC, wata biyu bayan jam’iyyar NNPP ta dakatar da shi.

A safiyar Litinin ɗin nan ɗan majalisar ya sanar da sauya sheƙarsa tare da magoya bayansa daga Jam’iyyar NNPP zuwa APC tare da goyon bayan neman wa’adi na biyu na Shugaba Tinubu a zaɓen 2027.

Abdulmumin Jibrin ya sanar ta shafinsa cewa sun ɗauki matakin ne bayan tattaunawar al’ummar mazaɓarsa. “Na samu kyakkyawar tarba daga dubban al’ummar mazaɓata ta Kofa, Bebeji, da ke Jihar Kano.

“Taron ya yi ittifaƙin ficewa daga NNPP/Kwankwasiyya, mu koma APC, tare da goyon bayan Shugaba Tinubu ya yi wa’adi na biyu.

An ƙara rage kuɗin aikin Hajjin 2026 a Najeriya Mahaifiyar Minista Balarabe Lawal Abas ta rasu

“Kafin nan, malamai kimanin 2,000 daga mazaɓarmu sun gudanar da addu’o’i na musamman ga Shugaban Ƙasa da neman samun zaman lafiya da ci-gaban Ƙiru/Bebeji, Kano, da ma Najeriya baki ɗaya.”

Idan ba a mata ba, Jam’iyyar NNPP ta dakatar da ɗan majalisar ne bisa zargin yi mata zagon ƙasa da kuma rashin kuɗin ƙa’ida na jam’iyya.

Tun bayan lokacin ba a ji daga gare shi ba game da makomar siyasarsa, duk da cewa makusantansa sun bayyana cewa yana ɗasawa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC, wanda ya kawo hasashen yiwuwar komawarsa APC.

A safiyar Litinin ɗin nan ɗan majalisar ya sanar ta shafinsa cewa ya sun ɗauki matakin ne bayan tattaunawar al’ummar mazaɓarsa.

A ɗaya daga bidiyoyi daya wallafa, an ga ɗan majalisar yana jawabi ga magoya bayansa da cewa zai sauya sheƙa tare da magoya bayansa domin kauce wa kuskurensa na baya na sauya sheƙa shi kaɗai.

“Na yanke shawarar zuwa da wannan taron jama’a domin gyara kuskuren da na yi a baya. Kada daga baya wani ya zo yana cewa ai ba Ni da magoya baya.”

Daga nan ya tambaye su ko sun yarda su fice daga NNPP da Kwankwasiyya zuwa APC, inda suka yi ta shewa suna cewa “APC.”

Daga nan ya tambaye su wanda za su zaɓa a 2027, sai suka amsa cewa “Tinubu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki
  • Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma
  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu da wasu mutum 4 a Sakkwato
  • Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe
  • Sarkin Musulmi ya ba wa makarantu tallafin N1.3bn a Kebbi
  • An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 
  • Matar tsohon Shugaban Ƙasa Shagari ta rasu
  • Abdulmumin Jibrin ya koma APC wata 2 bayan NNPP ta dakatar shi