Aminiya:
2025-09-17@23:08:31 GMT

Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a Jos

Published: 7th, July 2025 GMT

Wata babbas bas din haya kirar Macarpollo dauke da fasinjoji  ta yi hatsari a garin Jos, hedikwatar Filato.

Motar mai daukar fasinjoji 56 ta yi hatsari ne bayan isowarta Mahadar Vom da Anguldi da ke Jos, daga Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas.

Hatsarin ya auku ne kimanin milomita 10 kafin motar ta isa inda za ta tsaya bayan doguwar tafiyar mai nisan kilomita.

Wakilinmu ya gano cewa hatsarin ya auku ne da misalin karfe 4 na asubahin ranar Litinin din nan, inda motar ta lalata kusan daukacin shagunan da ke wurin da ta yi hatsari.

’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a Borno Turji: Gwamnatin Sakkwato ta ba da sharadin sulhu da ’yan ta’adda

Wani mazaunin yankin da ke sana’ar sayar da kifi ya bayyana cewa ba a samu asarar rai ba, kuma mutum daya ne kadai ya samu rauni a motar.

Jami’in Wayar da Kan Jama’a na Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) a Jihar Filato, Yakubu Lonsan, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya kara da cewa hukumar tana yin duk abin da ya kamata domin kawar da motar da ma cunkoso a wurin da abin ya faru.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hatsari Macarpollo motar ta yi hatsari

এছাড়াও পড়ুন:

Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Gwamnan Jihar Neja, Umar Mohammed Bago, ya janyo ce-ce-ku-ce a fadin Najeriya bayan da ya sake jaddada cewa duk wani malamin addini da ke shirin yin wa’azi dole ne ya gabatar da rubutaccen wa’azinsa domin tantancewa kafin ya gabatar da shi ga jama’a.

A cewar gwamnatin jihar, wannan mataki na da nufin daƙile kalaman ƙiyayya, tsattsauran ra’ayi da barazanar tsaro da ke tasowa daga wa’azin da ba a tantance ba.

Da yake jawabi a shirin Politics on Sunday na gidan talabijin na TVC, Gwamna Bago ya musanta zargin cewa dokar ta hana wa’azi gaba ɗaya, yana mai cewa matakin na da nufin tabbatar da zaman lafiya da hana tayar da fitina.

Gwamnan ya ce:

“Ban hana wa’azi ba. Duk wanda zai yi wa’azi a ranar Juma’a, ya kawo rubutaccen wa’azinsa domin tantancewa. Wannan ba sabon abu ba ne. A Saudiyya ma haka ake yi. Ba za a bar malami ya yi wa’azi da ke cin mutuncin jama’a ko gwamnati ba, yana mai cewa ba da damar yin wa’azi ba yana nufin a yi amfani da damar wajen tayar da hankali.”

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnati na aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro kamar DSS, ’yan Sanda, Sibil Difens da sojoji domin sa ido kan wa’azin da ka iya tayar da hankali.

Matakin ya fara jawo ce-ce-ku-ce ne bayan da Darakta Janar na Hukumar Kula da Harkokin Addini ta Jihar Neja, Umar Farooq, ya sanar da cewa duk wani malami dole ne ya nemi lasisin wa’azi cikin watanni biyu ko ya fuskanci hukunci.

“Abin da ake bukata shi ne su zo ofishinmu, su cike fom, sannan su fuskanci kwamitin tantancewa kafin su fara wa’azi,” in ji Farooq.

Wannan sanarwa ta haifar da martani iri-iri daga shugabannin addini da ƙungiyoyin fararen hula, inda da dama ke nuna fargabar cewa dokar za ta iya zama hanyar danne ’yancin faɗin albarkacin baki.

Babban Limamin Jami’ar Fasaha ta Minna, Sheikh Bashir Yankuzo, ya bayyana ra’ayi mai sassauci, yana mai cewa duk da cewa gwamnati na da haƙƙin daƙile kalaman ƙiyayya, ba za ta hana wa’azi na gaskiya ba.

Sheikh Yankuzo ya ce:

“Wa’azi umarni ne daga Allah, kuma gwamnati ba ta biya kowa albashi don yin wa’azi. Amma idan akwai masu tayar da hankali ko amfani da kalaman batanci, to gwamnati na da ikon dakile hakan don tabbatar da zaman lafiya.”

Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Jihar Neja ta bakin Sakataren ta, Raphael Opawoye, ta ce ba a sanar da su hukuncin ba.

“CAN ba ta da masaniya kan dokar. Za mu fitar da sanarwa idan an sanar da mu a hukumance,” in ji Opawoye.

Sai dai wani malamin addinin Musulunci, Ustaz Uthman Siraja, ya soki dokar kwata-kwata, yana mai cewa ta take ‘yancin addini da ibada.

Ya bayyana cewa:

“Hana wa’azi cin zarafin ’yancin addini ne. Mafi alheri shi ne gwamnati ta gayyato malamin da ya tayar da hankali ta hukunta shi, ba wai a tantance wa’azi gaba ɗaya ba.”

Gwamna Bago ya kare dokar da cewa matakin tsaro ne na rigakafi, musamman ganin tarihin jihar na fuskantar hare-haren ’yan bindiga, rikicin addini da tsattsauran ra’ayi.

Yayin da wa’adin cike fom da samun lasisi ke ƙara matsowa, idanu sun karkata zuwa Jihar Neja don ganin ko dokar za ta kawo zaman lafiya ko kuma ta ƙara dagula al’amura tsakanin gwamnati da al’ummar addini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara