Aminiya:
2025-07-07@17:25:14 GMT

Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a Jos

Published: 7th, July 2025 GMT

Wata babbas bas din haya kirar Macarpollo dauke da fasinjoji  ta yi hatsari a garin Jos, hedikwatar Filato.

Motar mai daukar fasinjoji 56 ta yi hatsari ne bayan isowarta Mahadar Vom da Anguldi da ke Jos, daga Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas.

Hatsarin ya auku ne kimanin milomita 10 kafin motar ta isa inda za ta tsaya bayan doguwar tafiyar mai nisan kilomita.

Wakilinmu ya gano cewa hatsarin ya auku ne da misalin karfe 4 na asubahin ranar Litinin din nan, inda motar ta lalata kusan daukacin shagunan da ke wurin da ta yi hatsari.

’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a Borno Turji: Gwamnatin Sakkwato ta ba da sharadin sulhu da ’yan ta’adda

Wani mazaunin yankin da ke sana’ar sayar da kifi ya bayyana cewa ba a samu asarar rai ba, kuma mutum daya ne kadai ya samu rauni a motar.

Jami’in Wayar da Kan Jama’a na Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) a Jihar Filato, Yakubu Lonsan, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya kara da cewa hukumar tana yin duk abin da ya kamata domin kawar da motar da ma cunkoso a wurin da abin ya faru.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hatsari Macarpollo motar ta yi hatsari

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara

Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce an samar da isassun matakan tsaro domin kawar da wasu gungun miyagu da ke aikata munanan laifuka a jihar.

 

AbdulRazaq ya bayyana hakan ne yayin da ya bayyana wa masu ruwa da tsaki daga yankin Lafiagi na jihar Kwara ta Arewa kan dimbin kokarin gwamnatin jihar a wani taro da aka gudanar a Ilorin.

 

Gwamnan ya amince da damuwar al’ummar tare da tabbatar musu da matakin da gwamnati ke jagoranta kan lamarin.

 

Ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kai hare-hare a dazuzzukan da aka gano a matsayin sansanin ‘yan ta’adda a Kwara ta Arewa da Kudu.

 

Gwamna AbdulRazaq ya ce ayyukan za su hada da sabbin jami’an tsaron dazuzzukan da aka horas da su a wuraren da aka kebe.

 

Ya kara da cewa, ayyukan za su fatattaki ‘yan ta’addan daga maboyarsu tare da dawo da kwanciyar hankali a yankunan da abin ya shafa, ya kuma kara da cewa za a yi taka-tsan-tsan don hana ’yan ta’adda yin katsalandan a wasu wurare.

 

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin jihar na hada hannu da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro domin kawar da barazanar da ake fuskanta a sassan jihar, musamman ma kauyukan da aka gano a kananan hukumomin Ifelodun, Edu da Patigi.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza
  • Wata bas kirar Macarpollo dauke da mutane da yi hatsari a Jos
  • Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
  • Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara
  • Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad
  • Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC
  • Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • Matashi ya kashe mahaifinsa da sanda a Jihar Bauchi