Rahotanni Daga Gaza sun ce adadin Falasdinawan da su ka yi shahada da safiyar yau sun haura 200

Wata sanarwar da ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta fitar a yau Talata ta ce; Adadin shahidan sanadiyyar sabbin hare-haren HKI sun kai  244.

 Sai dai har yanzu ba a kammala tantance adadin adadin shahidan ba, da kuma wadanda su ka jikkata.

Gabanin wannan harin na safiyar yau, an bayyana cewa fiye da Falasdinawa 150 ne su ka yi shahada tun bayan tsagaita wutar yaki.

Babban jami’i mai kula da harkokin watsa labaru a yankin Gaza Isma’ila Sawabita ya sanar da cewa; Tun daga tsagaita wutar yaki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa yanzu adadin Falasdinawa da su ka yi shahada sun haura 150, daga cikinsu har da na bayan nan su 40.

Wannan sanarwar dai ta biyo bayan kisan gillar da ‘yan mamaya su ka yi wa wasu Falasdinawa su 3 a gabashin sansanin ‘yan hijira na “al-Burj’ dake gundumar tsakiya.

Al-sawabita ya kuma tabbatar da cewa; Abinda ‘yan mamaya suke yi, shi ne keta tsagaita dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar tsagaita wutar yaki,ta hanyar ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi.

Haka nan kuma jami’in na watsa labaru a Gaza ya ce; A lokacin da ‘yan mamayar suke ci gaba da yin kisa, suna kuma kirkiro karairayi domin kare abinda suke yi,amma abinda yake faruwa a kasa yana tabbatar da aniyarsu ta tafka laifuka.

Al-Sawabita ya kara da cewa; Dukkanin Falasdinawan da ‘yan mamayar ya kashe ba su yin wata barazana ta tsaro  ga sojojinsu.”

 A wani gefen, jami’in watsa labarun na Gaza ya yi gargadin cewa da akwai gine-gine masu yawa da suke gab da rushewa saboda farmakin da ‘yan mamaya su ka kai musu a lokacin yaki. Ya kuma kara da cewa; wadannan gine-ginen suna a matsayin barazana ga dubban  mazaunan cikinsu a halin yanzu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki

Gwamantin Nigeria ta aike da jiragen yaki zuwa kasar Benin domin taimaka wa gwamnatin farar hula domin dakile yunkurin juyin mulkin da aka yi a kasar.

Aikin da jiragen yakin su ka fara yi, shi ne shimfida ikonsu a sararin samaniyar kasar Benin a ranar Lahadin da ta gabata,adaidai lokacin da sojoji da suke biyayya ga shugaba Patrice Talon su ka fafatawa da sojojin da suke kokarin mayar da doka da oda.

Ofishin shugaban kasar ta Nigeria, Ahmad Tininu ya kuma yi bayanin cewa; Daga cikin ayyukan da sojojin na Najeriya su ka yi a tare da hadin gwiwar takwarorinsu na Benin masu biyayya ga gwamnati, shi ne sanya idanu da kuma zama cikin ko ta-kwana domin aikewa da sojoji a kasa.

Ana kuma sa ran cewa sojojin kasashen Saliyo, Cote De Voire da Ghana za su isa Benin domin tabbatar da kare gwamnatin farar hula a karkashin  kungiyar tattalin arziki ta yammacin Afirka ( Ecowas).

A mataki na karshe da sojojin Najeriya su ka tsoma baki a wata kasa ta yammacin Afirka shi ne 2017, yayin da shugaban kasar Gambia Yahya Jami’u, ya ki amincewa ya sauka daga karagar mulki duk da cewa bai ci zabe ba.

A duk lokacin da aka yi juyin mulki a cikin kasashen nahiyar Afirka,musamman a yammacinta, kasar Nigeria tana zama ta gaba wajen yin tir da shi. Juyin mulkin da ya gabata na kasar Guinea Bissau, ya sa gwamnatin Bola Ahmad Tinibu ta yi tir da shi, tare da yin kira da a mayar da kasar kan turbar demokradiyya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan  Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko  Da  ‘Yan Ta’adda December 9, 2025  Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025  Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF  A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu December 8, 2025 Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki December 8, 2025 IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12 December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne
  • Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon
  • Najeriya: Jirgin Sojojin Kasar Yana Kan Hanyarsa Ta Zuwa Portugal, Amma Ta Sauka A Burkina Faso
  • Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  •  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada