Rahotanni Daga Gaza sun ce adadin Falasdinawan da su ka yi shahada da safiyar yau sun haura 200

Wata sanarwar da ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta fitar a yau Talata ta ce; Adadin shahidan sanadiyyar sabbin hare-haren HKI sun kai  244.

 Sai dai har yanzu ba a kammala tantance adadin adadin shahidan ba, da kuma wadanda su ka jikkata.

Gabanin wannan harin na safiyar yau, an bayyana cewa fiye da Falasdinawa 150 ne su ka yi shahada tun bayan tsagaita wutar yaki.

Babban jami’i mai kula da harkokin watsa labaru a yankin Gaza Isma’ila Sawabita ya sanar da cewa; Tun daga tsagaita wutar yaki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa yanzu adadin Falasdinawa da su ka yi shahada sun haura 150, daga cikinsu har da na bayan nan su 40.

Wannan sanarwar dai ta biyo bayan kisan gillar da ‘yan mamaya su ka yi wa wasu Falasdinawa su 3 a gabashin sansanin ‘yan hijira na “al-Burj’ dake gundumar tsakiya.

Al-sawabita ya kuma tabbatar da cewa; Abinda ‘yan mamaya suke yi, shi ne keta tsagaita dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar tsagaita wutar yaki,ta hanyar ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi.

Haka nan kuma jami’in na watsa labaru a Gaza ya ce; A lokacin da ‘yan mamayar suke ci gaba da yin kisa, suna kuma kirkiro karairayi domin kare abinda suke yi,amma abinda yake faruwa a kasa yana tabbatar da aniyarsu ta tafka laifuka.

Al-Sawabita ya kara da cewa; Dukkanin Falasdinawan da ‘yan mamayar ya kashe ba su yin wata barazana ta tsaro  ga sojojinsu.”

 A wani gefen, jami’in watsa labarun na Gaza ya yi gargadin cewa da akwai gine-gine masu yawa da suke gab da rushewa saboda farmakin da ‘yan mamaya su ka kai musu a lokacin yaki. Ya kuma kara da cewa; wadannan gine-ginen suna a matsayin barazana ga dubban  mazaunan cikinsu a halin yanzu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Na Shirye-Shiryen Aikewa Da Sojoji Guda 1000 A Iyakar Isra’ila Da Yankin Gaza

Rahotanni sun bayyana cewa kasar Amurka tana shirin kafa sanssanin soji  don aikewa da dubban dakaru zuwa iyakar Isra’ila da yankin Gaza, adaidai lokacin da ake fargabar wata sabuwar kasada da kuma sha’awar taimakawa gwamnatin mamaya wajen karbe ikon kula da yankin a nan gaba.

Masharhanta na ganin wannan shirin yana zuwa ne saboda irin bakin jini da Isra’ila ta yi a duniya bayan kisan kare dangi da ta yi a yankin Gaza, da ta fara tun daga watan Oktoban shekara ta 2023, wannan yasa telaviv ta bukaci abokiyarta ta ci gaba da aiwatar da aniyarta.

Ana sa bangaren jami’an gwamnatin falasdinu sun yi gargadin cewa duk wani mataki da zaa dauka na kokarin canza wani dan mamaya da wani, kwai canza sojojin isra’ila ne da na kasashen waje, idan ana iya tunawa tun a watan nuwamba ne baban jami’I a kungiyar Hamas musa abu marzuk ya bayyan cewa ba za su amince da irin wadannan matakai ba.

A baya bayan nan Washington ta mika wani daftarin kudiri ga kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya na nemana kafa wata runduna mai suna ISF da zasu zauna a yankin gaza a kalla na tsawon shekaru biyu

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Iran Ya Aike Da Wasika Ta Musamman Zuwa Ga Yarima Mai Jiran Gado Na Saudiya November 12, 2025 Gwamntin Nijeriya tace Za ta Kare Sojojinta Da Ke Bakin Aiki November 12, 2025 Iran Da Pakistan Sun yi Kira Da Yin Aiki Tare Don Tunkarar  Makiyansu November 12, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Kan Rikicin Yankin November 12, 2025 Gabon: An Daure Mata Da ‘Dan  Tsohon Shugaban Kasa Bongo Shekaru 20 A Gidan Yari November 12, 2025 Tanzania: MDD Ta Yi Kira Da A Yi Bincike Akan Daruruwan Mutanen Da Aka Kashe Sanadiyyar Rikcin Zabe November 12, 2025 Iran Ta Zama Memba A Kungiyar Tattara Bayanai Na  Ilimomi Da Kere-kere Ta Duniya ( ISKO) November 12, 2025 Iran: Ta’addanci barazana ce ga dukkan yankin November 12, 2025 Araghchi: Matsalar Yammacin duniya ita ce ci gaban kimiyyar Iran ba makaman nukiliya ba November 12, 2025 Sheikh Qassem: Kawar Da Hizbullah Ne Babban Burin Isra’ila A Lebanon November 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
  • Ina girmama sojojin Nijeriya — Wike
  • Gaza: Hamas Ta Nemi Kawo Karshen Kisan Kiyashi Da Lamunce  Shigar Da Taimako
  • Amurka Na Shirye-Shiryen Aikewa Da Sojoji Guda 1000 A Iyakar Isra’ila Da Yankin Gaza
  • Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro
  • Tanzania: MDD Ta Yi Kira Da A Yi Bincike Akan Daruruwan Mutanen Da Aka Kashe Sanadiyyar Rikcin Zabe
  • UNICEF ta ce Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza
  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu da wasu mutum 4 a Sakkwato
  • Gaza : Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau 282 tun bayan aiwatar da ita