Munanan Hare-hare Sojojin HKI A Gaza Da Safiyar Yau Talata Sun Yi Sanadiyyar Shahadar Fiye Da Falasdinawa 200
Published: 18th, March 2025 GMT
Rahotanni Daga Gaza sun ce adadin Falasdinawan da su ka yi shahada da safiyar yau sun haura 200
Wata sanarwar da ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta fitar a yau Talata ta ce; Adadin shahidan sanadiyyar sabbin hare-haren HKI sun kai 244.
Sai dai har yanzu ba a kammala tantance adadin adadin shahidan ba, da kuma wadanda su ka jikkata.
Gabanin wannan harin na safiyar yau, an bayyana cewa fiye da Falasdinawa 150 ne su ka yi shahada tun bayan tsagaita wutar yaki.
Babban jami’i mai kula da harkokin watsa labaru a yankin Gaza Isma’ila Sawabita ya sanar da cewa; Tun daga tsagaita wutar yaki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa yanzu adadin Falasdinawa da su ka yi shahada sun haura 150, daga cikinsu har da na bayan nan su 40.
Wannan sanarwar dai ta biyo bayan kisan gillar da ‘yan mamaya su ka yi wa wasu Falasdinawa su 3 a gabashin sansanin ‘yan hijira na “al-Burj’ dake gundumar tsakiya.
Al-sawabita ya kuma tabbatar da cewa; Abinda ‘yan mamaya suke yi, shi ne keta tsagaita dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar tsagaita wutar yaki,ta hanyar ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi.
Haka nan kuma jami’in na watsa labaru a Gaza ya ce; A lokacin da ‘yan mamayar suke ci gaba da yin kisa, suna kuma kirkiro karairayi domin kare abinda suke yi,amma abinda yake faruwa a kasa yana tabbatar da aniyarsu ta tafka laifuka.
Al-Sawabita ya kara da cewa; Dukkanin Falasdinawan da ‘yan mamayar ya kashe ba su yin wata barazana ta tsaro ga sojojinsu.”
A wani gefen, jami’in watsa labarun na Gaza ya yi gargadin cewa da akwai gine-gine masu yawa da suke gab da rushewa saboda farmakin da ‘yan mamaya su ka kai musu a lokacin yaki. Ya kuma kara da cewa; wadannan gine-ginen suna a matsayin barazana ga dubban mazaunan cikinsu a halin yanzu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Zata Gamu Da Maida Martani Mai Tsanani Idan Ta Kuskura Ta Sabonta Yaki Da Iran
Babban hafasan hafsoshin kasar Iran Major General Abdolrahim Mousavi ya bayyana cewa idan HKI ta kuskura ta sabonta yaki da kasar Iran ta zata fuskanci maida martani mafi tsanani.
Janar Musawi ya bayyana haka ne a jiya laraba a lokacinda yake hira da tashar talabijan ta almayaden ta kasar Lebanon
Ya kuma kara da cewa a yakin da ya gabata wato wa’adussadik na ukku na watan da ya gabata, sojojin Iran basu fitar da dukkan makamansu su. Ko kuma dukkan karfinsu ba. Don haka idan yahudawan sun kukura sun sake farfado da yaki da JMI sai sun hadu da martani wanda ya fi na farko zafi,
Janar Musavi ya kara da cewa HKI ta dauki shekaru tana tanajin ranar da yaki zai hadata da JMI, kuma ta ga inda tanadinta yak are. Ya ce abinda yake gaba gareta ya fi muni idan bata sani ba ta sani.
A wabi bangare Janar Musawi ya bayyana cewa kasashen yamma da kuma HKI sun son amfani da shirin makamashin nukliya na kasar Iran don raba kasar Iran da kuma maida ita fiye da yadda take a zamanin nsarki sha. Amma tare da taimakon All..sun kasa yin haka.