Munanan Hare-hare Sojojin HKI A Gaza Da Safiyar Yau Talata Sun Yi Sanadiyyar Shahadar Fiye Da Falasdinawa 200
Published: 18th, March 2025 GMT
Rahotanni Daga Gaza sun ce adadin Falasdinawan da su ka yi shahada da safiyar yau sun haura 200
Wata sanarwar da ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta fitar a yau Talata ta ce; Adadin shahidan sanadiyyar sabbin hare-haren HKI sun kai 244.
Sai dai har yanzu ba a kammala tantance adadin adadin shahidan ba, da kuma wadanda su ka jikkata.
Gabanin wannan harin na safiyar yau, an bayyana cewa fiye da Falasdinawa 150 ne su ka yi shahada tun bayan tsagaita wutar yaki.
Babban jami’i mai kula da harkokin watsa labaru a yankin Gaza Isma’ila Sawabita ya sanar da cewa; Tun daga tsagaita wutar yaki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa yanzu adadin Falasdinawa da su ka yi shahada sun haura 150, daga cikinsu har da na bayan nan su 40.
Wannan sanarwar dai ta biyo bayan kisan gillar da ‘yan mamaya su ka yi wa wasu Falasdinawa su 3 a gabashin sansanin ‘yan hijira na “al-Burj’ dake gundumar tsakiya.
Al-sawabita ya kuma tabbatar da cewa; Abinda ‘yan mamaya suke yi, shi ne keta tsagaita dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar tsagaita wutar yaki,ta hanyar ci gaba da yi wa Falasdinawa kisan kiyashi.
Haka nan kuma jami’in na watsa labaru a Gaza ya ce; A lokacin da ‘yan mamayar suke ci gaba da yin kisa, suna kuma kirkiro karairayi domin kare abinda suke yi,amma abinda yake faruwa a kasa yana tabbatar da aniyarsu ta tafka laifuka.
Al-Sawabita ya kara da cewa; Dukkanin Falasdinawan da ‘yan mamayar ya kashe ba su yin wata barazana ta tsaro ga sojojinsu.”
A wani gefen, jami’in watsa labarun na Gaza ya yi gargadin cewa da akwai gine-gine masu yawa da suke gab da rushewa saboda farmakin da ‘yan mamaya su ka kai musu a lokacin yaki. Ya kuma kara da cewa; wadannan gine-ginen suna a matsayin barazana ga dubban mazaunan cikinsu a halin yanzu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa Hamas ta bayyana cewa za ta mika makamanta ne kawai ” idan Isra’ila ta kawo karshen mamaya, tana mai jaddada cewa ba za a iya kwance damarar makamai ba a cikin yanayin da ake ciki na zaluncin soja da siyasa.
Babban jami’i a ofishin siyasa na Hamas kuma babban mai shiga tsakani na kungiyar, Khalil al-Hayya, ne ya bayyana hakan inda yake cewa idan mamayar ta kare, za a sanya wadannan makaman a karkashin ikon gwamnatin kasar Falasdinu.”
Ofishinsa ya fayyace cewa kalmar “ƙasa” tana nufin “ƙasar Falasɗinawa mai zaman kanta” mai cikaken iko.
“Har yanzu ana ci gaba da tattaunawa game da kwance makamai tsakanin kungiyoyi daban-daban da masu shiga tsakani, kuma yarjejeniyar tana cikin farkon matakanta ne kawai,” in ji shi.
“Mun yarda da tura sojojin Majalisar Dinkin Duniya a matsayin dakarun masu sa ido kan iyakokin da kuma tabbatar da kare yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza,” in ji Khalil al-Hayya.
Ma’aikatar Lafiya ta Falasdinawa a Gaza ta sanar a ranar Lahadi cewa tun lokacin da yarjejeniyar tsagaita wuta ta fara aiki, gwamnatin Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 367 tare da raunata wasu 953.
Sojojin Isra’ila sun kuma karya yarjejeniyar tsagaita wuta akalla sau 591 tsakanin 10 ga Oktoba zuwa 2 ga Disamba, ta hanyar hare-haren sama, manyan bindigogi da kuma harbi kai tsaye, a cewar ofishin manema labarai na gwamnati a Gaza.
Tun bayan fara kai hari kan kisan kare dangi da Isra’ila ta yi wa Gaza a ranar 7 ga Oktoba, 2023, akalla Falasdinawa 70,354 ne aka kashe, yawancinsu mata da yara, yayin da sama da 171,030 suka jikkata.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci