Leadership News Hausa:
2025-11-13@21:03:02 GMT

WSCIJ Ta Naɗa Farfesa Umaru Pate A Kwamitin Amintattu

Published: 19th, March 2025 GMT

WSCIJ Ta Naɗa Farfesa Umaru Pate A Kwamitin Amintattu

Da wannan sabon matsayi, Farfesa Pate, zai haɗa kai da sauran ƙwararru da ke aiki domin tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida da inganta shigar da al’umma cikin harkokin shugabanci, wanda ake kyautata zaton ƙwarewarsa za ta taimaka wajen tsara sabbin hanyoyi da cibiyar WSCIJ za ta amfana.

 

WSCIJ, wacce an sanya mata suna daga fitaccen marubuci kuma masanin adabi, Farfesa Wole Soyinka, cibiya ce mai zaman kanta da ke amfani da binciken ƙwaƙwaf a aikin jarida domin ƙarfafa dimokuraɗiyya da inganta tsarin shugabanci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi

Daga Bashir Meyere

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da bukatar Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, na neman rancen Naira Tiriliyan 1.15 domin cike gibin kasafin kudin shekarar 2025.

Amincewar ta biyo bayan gabatar da rahoton kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da lamuran bashi na cikin gida da na waje.

Yayin da yake gabatar da rahoton, shugaban kwamitin, Sanata Aliyu Magatakarda Wamako, wanda mataimakinsa Sanata Haruna Manu ya wakilta, ya bayyana cewa kasafin kudin shekarar 2025 na Naira tiriliyan 59.99 da Majalisar ta amince da shi, ya karu da Naira tiriliyan 5.25 idan aka kwatanta da Naira tiriliyan 54.74 da gwamnatin tarayya ta fara gabatarwa.

Ya ce an riga an amince da Naira tiriliyan 12.95 a cikin kasafin, wanda hakan ya bar gibin  Naira tiriliyan 1.147, abin da ya haifar da bukatar wannan shirin neman rance.

Kwamitin ya bai wa Majalisar shawarar  amincewa da rancen cikin gida na Naira tiriliyan 1.15 domin cike gibin da ya samo asali daga karin kudin kasafin.

Kwamitin ya kuma bukaci Ministar Kudi  da Ofishin Kula da Lamuran Bashi su tabbatar da cewa an aiwatar da rancen cikin tsari, tare da bin ka’idojin gaskiya,  da sharuɗɗan da suka dace.

Majalisar Dattawa ta kuma umurci kwamitinta mai kula da bashin cikin gida da na waje da ya rika sa ido kan yadda za a aiwatar da amfani da kudin da aka ciwo bashi.

Haka kuma, Ministar Kudi za ta rika mika rahoton kowane watanni uku kan halin da ake ciki, da amfani da kudaden, da yadda ake biyan basussuka, yayin da za a kai duk wani rahoton sabawa tsarin  ga Majalisar Dattawa domin daukar matakin doka da ya dace.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Nasarawa Ya Ce Za Su Samar da Masana’antu Don Ayyukan Yi
  • Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
  • Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi
  • Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • Kano Ta Kaddamar da Kwamitin Jagoranci Don Shirin Tarayyar Turai na Ilimi da Ƙarfafa Matasa
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfado Da Filin Jirgin Sama Na Kano
  • Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna
  • Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
  • Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika