Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Jigawa (JISEPA) ta yi kira ga al’umma da su ba da hadin kai wajen tabbatar da tsafta da kuma bayar da rahoton duk wani da ake sayarwa da ba bisa ka’ida ba, ko kuma cikin rashin tsafta.

Babban Daraktan Hukumar, Alhaji Adamu Sabo ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.

A cewarsa, wannan kira ya zama wajibi sakamakon nasarar da hukumar ta samu na kwace gurbatattun kayayyakin na sama da naira miliyan 14 a lokacin sintiri da binciken kayayyaki a fadin jihar daga watan Janairu zuwa Yuni na shekarar 2025.

Alhaji Adamu Sabo ya kara da cewa, mafi yawancin kayayyakin da aka kwace na ci ne da suka lalace, ko kuma wadanda aka adana ba bisa ka’ida ba, ko kuma suka lalace har suna barazana ga muhalli da lafiyar jama’a.

Ya bayyana cewa wann

an sintiri na tabbatar da tsafta yana cikin ayyukan hukumar domin inganta lafiyar jama’a da tabbatar da tsaron muhalli, tare da tabbatar da ka’idojin tsafta.

Sabo ya ce dukkan kayayyakin da aka kama an kaddamar da su bayan an bi dukkan matakan doka, an tantance su, sannan aka amince da lalata su bisa dokokin kiwon lafiya na jama’a.

“Wannan aikin an gudanar da shi ne bisa tsarin doka kamar yadda sashe na 5(1)(2) na Dokar Kariya ta Muhalli ta Jihar Jigawa ta shekarar 2009 (wanda aka gyara), da kuma sashe na 125(1) na Dokar Tsaron Lafiyar Jama’a ta Jihar Jigawa ta shekarar 2024 suka tanada”. In ji shi.

Ya jaddada cewa, wannan mataki  rigakafi ne na kare lafiyar jama’a da tabbatar da tsaron muhalli da tsaftar Jihar Jigawa ba don kuntatawa wani ba.

Ya kara da cewa, hukumar za ta ci gaba da yin aiki tare da kungiyoyin kasuwa, ‘yan kasuwa da shugabannin al’umma domin tabbatar da cikakken bin dokokin muhalli da na lafiyar jama’a.

 

Usman Muhammad Zaria

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa ta Jihar Jigawa lafiyar jama a tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Tsohon Gwamnan Jihar Ribas ya yi gargaɗin cewa dogaro da soja kaɗai, ba tare da inganta rayuwar jama’a ba, zai ƙara haifar da rikice-rikice.

Ya ƙara da cewa ingantacce  tsaro na ƙasa yana farawa ne idan gwamnati ta ƙirƙiro damarmakin samun aiki da kuma mayar da amincin jama’a ga gwamnati.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa October 14, 2025 Manyan Labarai Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan October 14, 2025 Manyan Labarai Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026 October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu
  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa