’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a Borno
Published: 7th, July 2025 GMT
An kashe mutane tara tare da jikkata wasu huɗu a wani da mayakan Boko Haram suka kai yankin a Malam Fatori da ke Jihar Borno.
Gwamna Babagana Zulum, wanda baya kasar a halin yanzu, ya tura tawaga ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Ƙananan Hukumomi, Sugun Mai Mele, domin jajanta wa waɗanda abin ya shafa da kuma tantance halin da ake ciki.
Mai Mele ya jaddada aniyar Gwamna Zulum na jajircewa wajen tabbatar da tsaron Malam Fatori saboda muhimmancinsa.
Ya sanar da shirin tura manyan injina domin tona ramuka a kusa da hedikwatar ƙaramar hukumar don hana hare-hare nan gaba daga Boko Haram da ISWAP.
Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato Sarkin Ibadan ya rasu yayin da ake shirin bikin cikarsa shekara guda a mulkiHaka nan kuma ya gargaɗi mazauna yankin kan haɗin gwiwa da ’yan tawaye, inda ya yi barazanar “sakamakon Ubangiji” ga duk masu haɗin gwiwa.
An bayar da tallafin kuɗi, inda aka bai wa duk gidan da suka asa yan uwa ₦500,000, yayin da waɗanda suka jikkata huɗu kowannensu ya samu ₦250,000.
A halin yanzu, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Tsaro na Cikin Gida, Usman Tar, ya sanar da shirin sake tsugunar da ƙarin iyalai 3,000 da suka rasa matsugunansu a Malam Fatori, wanda hakan zai kai ga jimlar gidaje 5,000 da aka sake tsugunar da su.
Tar ya tabbatar wa mazauna yankin ci gaba da ƙoƙarin gwamnati na samar da matakan tsaro da kayan aiki don dawwamammen dawowar su, yana mai kira gare su da su ci gaba da kasancewa a faɗake tare da kai rahoton duk wani abu da ba a aminta da shi ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram
এছাড়াও পড়ুন:
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar Sin ya gudanar da taron manema labarai da misalin karfe 10 na safiyar yau Litinin, inda kakakin hukumar kididdiga ta kasar, kuma babban masanin tattalin arziki, kana daraktan sashen kididdigar tattalin arziki na kasar, Fu Linghui ya yi karin haske kan ayyukan tattalin arzikin kasar cikin watan Agustan bana, tare da amsa tambayoyin manema labarai.
A cewar bayanan da aka gabatar a yayin taron, ayyukan tattalin arzikin kasar a watan Agusta sun samu ci gaba ba tare da tangarda ba. Kuma hakan ya bayyana ne ta hanyoyi daban-daban kamar haka: masana’antu sun habaka cikin sauri, masana’antar kera kayayyakin aiki da masana’antar fasaha sun samu ci gaba mai kyau. Kana ayyukan bayar da hidima su ma sun bunkasa cikin sauri. Baya ga haka, an samu ci gaba mai kyau a bangaren bayar da hidimomi na zamani. Harkokin kasuwanci sun samu ci gaba cikin natsuwa, inda harkokin sayar da kayayyaki ga masu sayayya suka kara habaka. Har ila yau, kadarorin jari sun ci gaba da karuwa, jarin masana’antu ya habaka cikin sauri, harkokin fice da shigen kayayyaki sun ci gaba da girma, tsarin kasuwanci ya ci gaba da ingantuwa, kana yanayin samar da guraben aikin yi, ya kasance kan wani mataki mai daidaito. Sai dai kuma saboda yanayin da ake ciki, adadin marasa aikin yi a birane ya karu, ma’aunin Core CPI ya ci gaba da hauhawa, kana faduwar farashin kayayyakin masana’antu ya ragu.
Bayanan sun kara da cewa, akwai bukatar lura da cewa, ana fuskantar yanayin rashin tabbas a waje, kuma tattalin arzikin kasar Sin yana fuskantar kalubale da hadari da yawa. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp