Harin Jirgin Yakin Sojoji Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 18 A Kasuwa
Published: 19th, March 2025 GMT
Majiyar ‘yan aware ta kasar Mali ta sanar da cewa wani hari da sojojin gwamnati su ka kai a arewacin kasar ya yi sanadiyyar kashe mutane 18 a arewacin kasar Yemen, sai dai sojojin gwamnatin ta ce, ‘yan aware ta kai wa hari.
Kungiyar Azbinawa ‘yan aware ta ce sojojin gwamnatin kasar sun kai hari ne a garin Lerneb mai nisan kilo mita 50 daga birnin Timbuktu, a ranar Litinin da ta gabata kuma bayan mutane 18 da su ka kwanta dama, wasu 7 sun jikkata.
Kungiyar ta Azbinawa ta bayyana abinda ya faru da cewa; “Dabbanci” ne irin na zamanin jahiliyya.
Sai dai sojojin gwamnatin kasar ta Mali sun wallafa a shafinsu na X cewa; sun kai harin ne akan wata tunga ta ‘yan ta’adda tare da kashe 11 daga cikinsu.
Fiye da shekaru 10 kenan kasar ta Mali tare da makwabtanta, Burkina Faso da Nijar suke fada da kungiyoyi masu dauke da makamai da su ka hada al’ka’ida da kuma “Da’esh”.
Bayan juyin mulkin da aka yi a cikin kasashen uku, da korar sojojin Faransa, kasar ta Mali ta gayyato mayakan kungiyar “Wagner” daga kasar Rasha, domin taya ta fada da masu dauke da makaman.
Sai dai a wasu lokutan ana samun kuskure irin wannan da wajen kai wa masu dauke da makamai hari, ake kai wa fararen hula.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
Sojojin kasar Iran sun cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan HKI a dazuda nan nan, wayo yau lahadi a ci gaba da musayar wauta da suke yi da sojojin HKI kwanaki uku da suka gabata.
Kamfanin dillancin labaran kare kai na kasar Iran Tasnim ya nakalto sojojin kasar na cewa sun cilla makamai masu linzami da Drones a karon farko da rana ido na ganin ido a kan HKI kuma tuna makaman sun fada a inda yakamata su fada a cikin haramtacciyar kasar.
A safiyar ranar jumma’a ce sojojin HKI suka kai hare-hare kan birnin Tehran inda suka kai manya-manyan jami’an sojojin kasar ga shahada, sannan suka kashe mutane fararen hula wadanda basu da laifi.
Bayan haka ne sojojin JMI suka fara maida martani a daren Asabar da daren lahadi, amma a wannan karon sun kai hare haren ne da ranar Lahadi ido na ganin ido.
Hare-haren wadanda aka basu suna “Alkawalin gaskiya Na 3 zasu ci gaba matakar HKI ta ci gaba da kaiwa Iran hare hare.