HausaTv:
2025-12-14@23:56:32 GMT

Harin Jirgin Yakin Sojoji Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 18 A Kasuwa

Published: 19th, March 2025 GMT

Majiyar ‘yan aware ta kasar Mali ta sanar da cewa wani hari da sojojin gwamnati su ka kai a arewacin kasar ya yi sanadiyyar kashe mutane 18 a arewacin kasar Yemen, sai dai sojojin gwamnatin ta ce, ‘yan aware ta kai wa hari.

Kungiyar Azbinawa ‘yan aware ta ce sojojin gwamnatin kasar sun kai hari ne a garin Lerneb mai nisan kilo mita 50 daga birnin Timbuktu, a ranar Litinin da ta gabata kuma bayan mutane 18 da su ka kwanta dama, wasu 7 sun jikkata.

Kungiyar ta Azbinawa ta bayyana abinda ya faru da cewa; “Dabbanci” ne irin na zamanin jahiliyya.

Sai dai sojojin gwamnatin kasar ta Mali sun wallafa a shafinsu na X cewa; sun kai harin ne akan wata  tunga ta  ‘yan ta’adda tare da kashe 11 daga cikinsu.

Fiye da shekaru  10 kenan kasar ta Mali tare da makwabtanta, Burkina Faso da Nijar suke  fada da  kungiyoyi masu dauke da makamai da su ka hada al’ka’ida da kuma “Da’esh”.

Bayan juyin mulkin da aka yi a cikin kasashen uku, da korar sojojin Faransa, kasar ta Mali ta gayyato mayakan kungiyar “Wagner”  daga kasar Rasha, domin taya ta fada da masu dauke da makaman.

Sai dai a wasu lokutan ana samun kuskure irin wannan da wajen kai wa masu dauke da makamai hari, ake kai wa fararen hula.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani

Da yake bayani dangane da jirgin sojan Nijeriya da kasar Burkino Faso ta kama, ya ce babu wani dalilin kama jirgin sojan Nijeriya, yana mai cewa duk wata kasa ta san cewa idan jirgi ya samu matsala yana iya yada zango a kasarta daga bisani idan aka gano matsalar sai ya tashi ya tafi. Akan hakan ya gargadi mahukunta kasar da su gaggauta sakin jirgin sojan Nijeriya ba tare da wani bata loka

ci ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi December 13, 2025 Labarai Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum December 13, 2025 Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman December 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano
  • Hafsan sojin ƙasa ya buƙaci sabbin dakaru su zama masu kishin ƙasa
  • Buɗe cibiyar horas da sabbin sojoji a Kudu zai taimaka — Janar Shaibu
  • Me Ke Kawo Yawaitar Juyin Mulki A Nahiyar Afirka?
  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • Yadda Rashin Bincike Ke Haifar Da Yawaitar Mutuwar Aure
  • Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’