HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano
Published: 19th, March 2025 GMT
Wata gobara da ta auku safiyar wannan Larabar ta laƙume kasuwar ’yan gwan-gwan da ke unguwar Dakata a Ƙaramar Hukumar Nassarawa ta Jihar Kano.
Kasuwar wadda ake kira da Kwalema tana nan a kan titin Zango, daura da gidajen man Dominion da kuma Mobil da ke makwabtaka da ofishin Hukumar WAEC.
Cire Gwamna Fubara ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki — Lauyoyi DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen GwamnaMai magana da yawun hukumar kwana-kwana Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa jami’ansu na ci gaba da ƙoƙarin kashe gobarar da ke neman wuce gona da iri.
Sai dai ya bayyana cewa duk da bincike ya soma gudana, amma kawo yanzu ba su gano musabbabin tashin gobarar ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara Gwangwan Jihar Kano Kwalema
এছাড়াও পড়ুন:
Sanatan Enugu ya mutu a Birtaniya
Majalisar Dattawa ta shiga cikin jimami a ranar Laraba bayan mutuwar Sanata Okey Ezea, mai wakiltar mazabar Enugu ta Arewa.
Bayanai sun nuna marigayin ya rasu ne a kasar Burtaniya inda yake jinya.
‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’ Mai taɓin hankali ya kashe soja a LegasEzea, wanda aka zaɓe a ƙarƙashin jam’iyyar LP, shi ne kaɗai Sanatan da ya ci zabe daga Enugu karkashin jam’iyyar a Majalisar Dattawa ta 10.
Rasuwarsa ta sa ya zama sanata na biyu daga yankin Kudu maso Gabas da ya rasu cikin shekaru biyu, bayan mutuwar Sanata Ifeanyi Ubah daga Jihar Anambra, wanda shi ma ya rasu a Landan a watan Yuli 2024 yana da shekara 52.
Da labarin rasuwarsa ya isa Majalisar, abokan aikinsa sun yi ta’aziyya, suna bayyana shi a matsayin ɗan majalisa mai tawali’u, mai jajircewa, da kuma sadaukarwa, wanda rashin sa ya bar gibi a zauren majalisar.
Sanata Orji Uzor Kalu, wanda ke wakiltar Abia ta Arewa, ya ce ya yi matukar kaduwa da samun labarin, inda ya bayyana marigayin a matsayin ɗan’uwana kuma abokinsa.
Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan daga Kogi ta Tsakiya, ita ma ta yi jimami, tana bayyana Ezea a matsayin aboki mai hikima da natsuwa, wanda shawarwarinsa da addu’oinsa suka taimaka mata a lokutan da ta shiga ƙalubale.
Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta yi magana a hukumance kan rasuwarsa a zaman majalisa, tare da yin shiru na minti ɗaya don girmamawa, kamar yadda al’ada ta tanada.