HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano
Published: 19th, March 2025 GMT
Wata gobara da ta auku safiyar wannan Larabar ta laƙume kasuwar ’yan gwan-gwan da ke unguwar Dakata a Ƙaramar Hukumar Nassarawa ta Jihar Kano.
Kasuwar wadda ake kira da Kwalema tana nan a kan titin Zango, daura da gidajen man Dominion da kuma Mobil da ke makwabtaka da ofishin Hukumar WAEC.
Cire Gwamna Fubara ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki — Lauyoyi DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen GwamnaMai magana da yawun hukumar kwana-kwana Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa jami’ansu na ci gaba da ƙoƙarin kashe gobarar da ke neman wuce gona da iri.
Sai dai ya bayyana cewa duk da bincike ya soma gudana, amma kawo yanzu ba su gano musabbabin tashin gobarar ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara Gwangwan Jihar Kano Kwalema
এছাড়াও পড়ুন:
A Shirye Nake Na Kare Nasarar Da Na Samu A Zabe – Tchiroma Bakary
Ɗan takarar jam’iyyar adawa a zaɓen shugaban ƙasar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary wanda ya ayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zaɓen, ya shaida wa BBC cewa a shirye yake ya kare abin da ya bayyana “nasara ƙarara” da ya samu.
Yayin da al’ummar ƙasar ke ci gaba da dakon sakamakon zaɓen da za a bayyana a ranar Litinin mai zuwa, Bakary, wanda shi ma tsohon jami’in gwamnatin Paul Biya ne, ya ce zai amince ne kawai da sakamako na gaskiya.
Wannan kalami nasa dai zai ƙara rura wutar zaman ɗarɗar da ake yi a ƙasar ta yankin tsakiyar Afirka.
Tun daga farkon makon nan ne mutane, musamman magoya bayan Bakary suka riƙa fita kan tituna domin yin gangamin kira ga gwamnati ta tabbatar ta fitar da sakamako daidai da zaɓin al’umma.
A baya an tsara cewa za a bayyana sakamakon zaɓen ne ranar Alhamis, sai dai wata sanarwa daga gwamnati ta ce an ɗage bayyana sakamakon zuwa ranar Litinin ɗin mako mai zuwa.
Wasu alkalumman da kafofin yada labaran kasar suka ruwaito sun nuna cewa akwai yiyuwar shugaba Paul Biya ne zai zarce kan mulkinsa na shekara 43.