HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano
Published: 19th, March 2025 GMT
Wata gobara da ta auku safiyar wannan Larabar ta laƙume kasuwar ’yan gwan-gwan da ke unguwar Dakata a Ƙaramar Hukumar Nassarawa ta Jihar Kano.
Kasuwar wadda ake kira da Kwalema tana nan a kan titin Zango, daura da gidajen man Dominion da kuma Mobil da ke makwabtaka da ofishin Hukumar WAEC.
Cire Gwamna Fubara ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki — Lauyoyi DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen GwamnaMai magana da yawun hukumar kwana-kwana Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa jami’ansu na ci gaba da ƙoƙarin kashe gobarar da ke neman wuce gona da iri.
Sai dai ya bayyana cewa duk da bincike ya soma gudana, amma kawo yanzu ba su gano musabbabin tashin gobarar ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara Gwangwan Jihar Kano Kwalema
এছাড়াও পড়ুন:
Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano
Wani jirgin sama mallakin kamfanin Flybird, ya yi hatsari yayin sauka a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano.
Jirgin ya taso daga Abuja, kuma lamarin ya faru ne a lokacin da yake ƙoƙarin sauka a filin jirgin saman Kano, a ranar Lahadi.
Tsaro: Abba ya kafa runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota a Kano An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a OstireliyaMajiyoyi daga filin jirgin saman, sun bayyana cewa babu wani fasinja ko ma’aikacin jirgin da ya ji rauni.
Wani jami’in filin jirgin ya shaida wa Aminiya, cewa hukumomin sufurin jiragen sama ko Hedikwatar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Tarayya (FAAN) ne, kaɗai za su iya yin ƙarin bayani kan lamarin.
Wata majiya kuma ta tabbatar da cewa fasinjoji 11 ne ke cikin jirgin a lokacin da lamarin ya faru.