Aminiya:
2025-12-02@11:52:53 GMT

Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce

Published: 7th, July 2025 GMT

A ƙarshen makon da ya gabata ne fitacciyar ’yar TikTok wacce aka fi sani da Babiana ta fitar da wani sabon bidiyo tana rusa ihu tana kira ga Shugaba Bola Tinubu da wasu mawaƙan kudancin Najeriya da su shiga tsakaninta da ’yan Arewa a kan abin da tace suna yi mata na cin zarafi tun bayan bayyanar bidiyo tsiraicinta a shekarar 2024.

Babiana ta yi bidiyon ne cikin harshen Ingilishi inda ta ce ba a yi mata adalci a Arewa kuma ana barazana da rayuwarta.

Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a Jos

Ta bayyana cewa tsawon shekara ɗaya ta yi tana raɓe-raɓe saboda ba ta son maganganun da mutane ke mata tun bayan bayyanar bidiyon tsiraicin nata a soshiyal midiya.

“Ina cikin halin ƙunci da damuwa, ’yan Kudu ku taimaka min Musulman Arewa na son ganin bayana” a cewar Babiana cikin harshen Ingilishi.

Yar TikTok ɗin ta ƙara bayyana cewa tun bayan ɓullar bidiyon tsiraicin nata ta shiga cikin damuwa inda kusan kullum cikin kuka take kwana, kuma har yanzu ’yan Arewa suna mata barazana da bidiyon.

Sabon bidiyo nata ya tayar ƙura, inda wasu ke ganin kalaman nata ba su kamata ba, kuma babu adalci a ciki, kuma ba ta ɗauko hanyar shawo kan matsalar ba.

Nasiru Salisu Zango, sharhi ya yi akan lamarin inda ya ce “ko da yake a cikin bidiyon Babiana ta yi maganganu na ɗora alhaki kan al’ummar Arewa Musulmai wanda hakan rashin adalci ne, amma fa duk da haka akwai buƙatar jan hankalin masu yaɗa bidiyon kan suji tsoron Allah.”

Ya ƙara da cewa “ya kamata a tausaya mata tun kafin ta faɗa wani yanayin na daban, mun sani tana da ’ya’ya da ’yan uwa da wannan yaɗa bidiyon zai iya rikita wa rayuwa.”

Shi kuwa Bilyaminu Ayuba, cewa ya yi ai dama alhaki kuikuyo ne kuma Babiana ba ta ɗauko hanyar da ya kamata ba wajen gyaran wannan matsalar duk da ya bayyana cewa abin da ake matan bai dace ba.

“ A ganina Babiana ba ta ɗauko hanyar gyara matsalar ba saboda shi mutumci madara ne, idan ya zube shi ke nan kuma har yanzu tana son shisshigi da aibanta mutane shi ya sa kullum za a dinga sukar ta da wannan bidiyon nata na marke.

“Idan har tana son zaman lafiya a rayuwarta, to dole ta daina jifa da shisshigi wa mutane, wannan shi ne. Allah Ya sa mu dace.”

Jamilu Sani a nasa ɓangaren cewa ya yi “a cikin lamarinki akwai wa’azi. A baya kece mai yaɗa bidiyon waɗansu idan sun yi irin wannan abin da kika kira kuskure, yau sai Allah Ya kama ki domin ki ji yadda kika jiyar da ’yan uwanki mata marasa tarbiyya da tunanin gobe.”

Ya ƙara da yin kira ga sauran mutane cewa Babiana da ire-irensu marasa “hangen nesa, sun yi aiki marar kyau a ɓoye. Sun yi wa kansu bidiyo, idan suka tuba , tuba na gaske, sai Allah Ya yafe musu.”

Hafsat Muhammed cewa ta yi, “Ita har ta manta duk abubuwan da ta yi wa mutane, kuma har yau ba ta nemi yafiyarsu ba har tana ma kanta kirari da ‘Queen of Update.’”

Abdulwahab Sa’id Ahmad a shafinsa na Facebook wallafawa ya yi cewa: “Wanda yake da cutar Depression ba shi yake ganewa ba sai dai a gane masa.

“Mahaukaci bai san yana hauka ba sai dai a ba shi labari bayan ya warke

“Ki bar nunawa cewa Musulmi sun yi watsi da ke da ’yan Arewa, ke ce ki ka zaɓi ki zauna a yadda ki ke.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165

165-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa, shiri wanda yake kawo maku, kissoshi wadanda suka zo cikin Alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Mrtada Muttahari, ko kuma cikin littafan Mathnawa na maulana Jalaluddeen Rumi. Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

////… Ma dalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-Haddan dan Aliyu (a) dan Fatimah (s) diyar manzon Allah (s) da muke kawo maku, a cikin shirimmu da ya gabata, mun yi maganar cewa Imam Al-Hassan ya rasa samun amintattun sojojin da zasu goya masu baya don yakar Mu’awiya dan Abusufyan. Saboda yadda suka ga cewa Mu,awiya yaudari kwamandojin sojojinsa da cin hanci da rashawa.

Amma su Ahlulbaiti musamman Amirulmuminina shugabansu, ma’abuta addini ne wadanda basa sabawa Allah ko da na kebtawar ido ne. Amma mutanen Iraki sun rena abinda suke samu a karkashin ikonsu na kudade da dukiyoyi. Da sun yi hakuri suka bisu, da sunci ta sama da kasansu ba tare da ganimar yaki ba.

Saboda Allah yana arzuta muminai ta sama da kasa hanyoyi daban-daban, musamman ta hanyoyin raya kasa. Da sun yi hakuri suka yi biyayya a gareshi da sai sun isa wani lokacinda basa bukatar yaki don samun ganimar dukiya. Zaman lafiya da za’a samar zai bude masu hanyoyin samun kudade da dukiyoti masu yawa.

Amma sun ki biyayya a gareshi, a duk lokacinda ya kirasu zuwa jihadi don tabbatar da zaman lafiya a cikin al-ummar musulmi basa bada hadin kai.

Imam Ali (a) yana sifinta mutanen Kufa a cikin khudubobinsa, inda yake bayyana rashin bada hadin kansu a duk lolacinda ya kirasu zuwa ga jihadi da kuma yakar mutanen sham kamar inda yake cewa.

{Na kirasu a asirce da bayyana, na kirasu na sake kiransu, daga cikinsu akwai wadanda suke amsa kira amma ba da son ransu ba, daga cikinsu akwai wadanda suke kariyar rashin lafiya, daga cikinsi akwai wadanda suka zauna bas u fitoba ba tare da dalili ba. Ina rokon Allah mai girma da daukaka yayi mani mafita daga garesu da gaggawa. Na rantse da Allah, ba don ina kodayin samun shahada a lokacin haduwa da abokan gaba ba, da kuma tanajin kaina don mutuwa da na so ace ban hadu da wadan nan ba ko da na kwana guda, kuma b azan sake haduwa da su ba har abada}.

A wani wuri Imam Ali (a) yana fada dangane da mutanen Kufa yana cewa {Wallah, wanda aka yaudara, shi wanda ya rudu da ku, wanda ya sami nasara da ku, wallahi shi ne ya sami nasara da mafi tabewar rabo. Wanda ya yi jifa da ku kamar wanda yayi jifa da kibiyan da bai da wurin harbawa, Kuma na kasance bana gasgata zancenku, bana kodayin samun taimakonku, ba zan gargadi makiyi da ku ba, me ya sameku ne? menene maganinku ne? menen waraka a gareku ne?}.

Khudubobin Amirul muminina (a) dangane da sojojinsa suna da yawa a cikin littafin Nahjulbalagha. Inda yak e bayyana yadda suka tabar da shi, suka bakanta ransa, kuma sun ci gaba da hakan har zuwa shahadarsa.

A lokacinda al-amura suka koma hannun Imam Al-Hassan (a) sai al-amarinsu ya kara bayyana, da mafi muninsa. Saboda a lokacinda ya bayyana masu abinda Mu’awiya ya kirashi zuwa gareshi na sulhu, sai dukaninsi ko mafi yawansu sun daga murya suna cewa (muna sun rayuka muna son rayuwa). Wannan ya nuna yadda suke kin mutuwa, suke kuma tsoron jihadi. Basa son duk wani abu wanda zai kai ga yaki da Mu’awiya dan Abusufyan.

Sannan sojojin Imam Al-Hassan (a) sun rasa wadanda suka fahinci addinin musulunci kekyawar fahinta, wadanda suka san matsayin iyalan gidan manzon Allah (s) a cikin musulmi. Mafi yawansu daga baya ne suka musulunt suka shiga addinin musulunci.

Malaman tarihi sun bayyana cewa sahabban manzon Allah (S) wadanda suka musulunta tun farkon bayyanar addinin musulunci kuma suka halarci yakin badar basu fi 63 ne a cikin rundunar Imam Hassan Almujaba (a) ba.

Amma a lokacin yakin Jamal da siffin Imam Ali (a) yana tare ragowarsu daga cikin  da manya manyan sahabban manzon Allah (s) wadanda suka san matsayinsa suka san matsayin iyalan gidan manzon Allah (s) basa saba masa kan duk abinda ya umurcesu. Sahabbai kamar, Ammar dan Yasir, Hashimul Murkal,thabit dan qais, da zuzshahadataini, da makamantarsu, duk sun yi shahada a yake-yaken Jamal  da siffin kuma sune suke jagorantar rundunar Imam Ali (a), har zu lokacin shahadarsu.

Da a ce wadan nan sahbban da masu kama da su, suna cikin rundunar Imam Al-Haasan (a) da baya bukatar dogaro da wadanda basu san matsayinsa basu san matsayin iyalan gidan manzon Allah(s) a cikinsu ba.

Abu na gaba wanda ya jawo Rauni ciki  rundunar Imam Al-Hassan sun hada da kiraye-kirayen Mu\awiya dan Abu Sufyan da Sulhu da kuma zaman lafiya. Wannan bayan da kwamandoji da shuwagabanni kabilu da dama daga rundunar Imam Hassan (a) suka koma bangaren Mu’awiya saboda rashawa da ya basu ko kuma alkawulan da yayi masu.

Wadan nan kiraye-kiraye basu da bambanci da daga Mushafi da sojojin mu’awiya suka yi a siffin. Inda Imam Ali (a) ya bayyana masu cewa makirce kada su kula da su, amma suka saba masa suka ki biyayya a gareshi banda haka suka yi masa barazanan zasu kasheshi kamar yadda suka kashe Uthman.

Haka al-amarin yake a rundunar Imam Al-Hassan, sun amince da kiraye-kirayen da Mu’awiya yake yin a sulhuntawa, basu  fahinci sharrin da ke ciki ba, amma kamar yadda zamu gani, daga karshe da aka yi sulhun suka kuma dandani masifa daga sarakunan banu Umayya sai da suka gommace Khalifa Uthman a kansa. Saboda musibar da Mu’awiya dan abu sufyan ya shuka a cikin daular Musulunci, da kuma azbatar da su da yayi, da shi da danginsa na tsawon kimani shekaru 80, musibar ta kai ga ba wanda zai iya sauke su daga kan wuyoyin musulmi sai da musulmi ajamawa daga yankin Khurasan na kasar Iran karkashin jagorancin Abu Muslimul Khurasani ne ya sami nasarar kifar da daularsu a kan musulmi.

Don haka sojojin Imam Hassan (a) sun rasa mutanen kirki wadanda suka san matsayinsa, suka fahinci addinin kamar wadanda suka sansu cikin sahabban manzon Allah (s). Don haka jahilcinsu ne yasa suke maraba da neman sulhun Mu’awiya.

Don haka daga karshe rundunar Imam Al-Hassan (a) ta zami sulhu da Mu’awiya kuma Imam Al-Hassan (a) ba zai iya tursasu yaki da shi ba. Don haka bai da zabi in banda sulhu da Mu,awiya, da kuma kare wadanda suka rage daga cikin iyalan gidan manzon Allah da kuma mabiyansu da gaske da suka rage.

Kha’incin Ubaidullahi dan Abbas, yana daga cikin manya-manyan al-amura da suka jawo kashe guiwar sojojin Imam Al-Hassan (a), da raunanat, saboda ganin yadda ya kasance babban kwamandan sojojin gaba daya, ko kuma runduna mafi girma daga cikin rundunonin Imam Al-Hassan (a) banda haka yana daga cikin Imam Alhassan  wato Banu Hashim. Kowa na ganin idan da kowa zai bar Imam Al-Hassan (a) irinsa bai kamata su kha’inci Imam Al-Hassan ba saboda shi dan amminsa ne. Kuma a wayewarsa da saninsa matsayin iyalan gidan manzon Allah (s), ha rya taba zama gwamnan kasar Yemen a lokacin khalifancin Amirul muminina (a) . To bai kamata a ce ya guda zuwa wajen Banu Umayya makiya Banu Hashin a tarihi, kafin da kuma bayan bayyanar addinin musulunci. Wannan abinda ya aikata ya zama abin kunya kuma babban tabo ne ga yan gidan Abbas ammin manzon Allah (s).

Kamar yadda wani mawaki yake cewa.

Idan na kusa wanda kai dan kungiyarsa ne ya kubuce maka* To kada kayi mamaki idan wadanda suke nesa da kai su mika ga Makiya.

Abinda Ubaidullahi dan Abbas ya yi ya cusa bakin ciki a cikin zuciyar Imam Al-Hassan, bakin ciki mai yawa. Don bai mutunta duk abubuwan mutuntawa tsakaninsa da Imam Hassan, a ko wani bangare. Bai mutunta dankon addinin wanda ya fito daga gidansu Banu Hashim ba, bai mutunta dankon zumncin da ke tsakaninsa da Imam Al-Hassan na cewa shi dan ammin manzon Allah (s). banda haka shi ne babban kwamandan sojojin Imam Alhassan (a), kuma a matsayin wanda y afara kiran a yi masa bai’a sannan wanda ya fara yi masa bai’a ba. Kuma bai ji tsoron yanda wannan abinda yayi zai zama tabo ga zuriyyarsa har duniya ta nade ba.

Idan zaku tuna Kais dan Sa’adu dan Ubada, bayan da Ubaidullahi ya koma bangaren Mu’awiya shi ya bada sallar Asubaha, sannan yayi khuduba, yana cewa: Wannan da dan’uwansa da babansa basu taba aikin alkhairi ba. Yace Abbas ammin manzon Allah (s) ya yake shi a Abadar sai da aka kamashi a matsayin fursinan yaki. Ya kuma karbi kudi a wajensa don ya fanshi kansa.

Sannan Imam Ali ya nada dan’uwansa a matsayin wali a Basra, ya sace kudade ya sayi bayi, yana ganin sun halatta a gareshi. Sannan shi Ubaidullahi, a matsayinsa na gwamnan Imam Ali (a) a Yemen, a lokacinda Busru ya kai hare-hare kan kasar Yemen ya gudu ha ya bar yayansa a hannun makiya suka kashesu, maimakon ya nuna turjiya ko da kuwa zai mutune. Sannan gashi ya kara da abinda yayi na Kha’inci ga Imam Al-Hassan (a).

Abinda Ubaidullahi yayi ya shafi danginsa da suka yi Mulki bayan banu Umayya, har sai da ya kai suna boye abubuwan kunyan da ya faru a cikin danginsu a farko farkon Musulunci.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya December 1, 2025 Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3  A Kasar Lebanon December 1, 2025 Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru December 1, 2025 Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi December 1, 2025 Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100% December 1, 2025 Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta December 1, 2025 Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta December 1, 2025 Nijar : zamu sayar da uranium dinmu ga wanda muka ga dama_ Janar Tiani December 1, 2025 Tawagar ECOWAS za ta je Guinea-Bissau, bayan juyin mulkin soji December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32