Aminiya:
2025-10-15@12:20:51 GMT

Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce

Published: 7th, July 2025 GMT

A ƙarshen makon da ya gabata ne fitacciyar ’yar TikTok wacce aka fi sani da Babiana ta fitar da wani sabon bidiyo tana rusa ihu tana kira ga Shugaba Bola Tinubu da wasu mawaƙan kudancin Najeriya da su shiga tsakaninta da ’yan Arewa a kan abin da tace suna yi mata na cin zarafi tun bayan bayyanar bidiyo tsiraicinta a shekarar 2024.

Babiana ta yi bidiyon ne cikin harshen Ingilishi inda ta ce ba a yi mata adalci a Arewa kuma ana barazana da rayuwarta.

Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a Jos

Ta bayyana cewa tsawon shekara ɗaya ta yi tana raɓe-raɓe saboda ba ta son maganganun da mutane ke mata tun bayan bayyanar bidiyon tsiraicin nata a soshiyal midiya.

“Ina cikin halin ƙunci da damuwa, ’yan Kudu ku taimaka min Musulman Arewa na son ganin bayana” a cewar Babiana cikin harshen Ingilishi.

Yar TikTok ɗin ta ƙara bayyana cewa tun bayan ɓullar bidiyon tsiraicin nata ta shiga cikin damuwa inda kusan kullum cikin kuka take kwana, kuma har yanzu ’yan Arewa suna mata barazana da bidiyon.

Sabon bidiyo nata ya tayar ƙura, inda wasu ke ganin kalaman nata ba su kamata ba, kuma babu adalci a ciki, kuma ba ta ɗauko hanyar shawo kan matsalar ba.

Nasiru Salisu Zango, sharhi ya yi akan lamarin inda ya ce “ko da yake a cikin bidiyon Babiana ta yi maganganu na ɗora alhaki kan al’ummar Arewa Musulmai wanda hakan rashin adalci ne, amma fa duk da haka akwai buƙatar jan hankalin masu yaɗa bidiyon kan suji tsoron Allah.”

Ya ƙara da cewa “ya kamata a tausaya mata tun kafin ta faɗa wani yanayin na daban, mun sani tana da ’ya’ya da ’yan uwa da wannan yaɗa bidiyon zai iya rikita wa rayuwa.”

Shi kuwa Bilyaminu Ayuba, cewa ya yi ai dama alhaki kuikuyo ne kuma Babiana ba ta ɗauko hanyar da ya kamata ba wajen gyaran wannan matsalar duk da ya bayyana cewa abin da ake matan bai dace ba.

“ A ganina Babiana ba ta ɗauko hanyar gyara matsalar ba saboda shi mutumci madara ne, idan ya zube shi ke nan kuma har yanzu tana son shisshigi da aibanta mutane shi ya sa kullum za a dinga sukar ta da wannan bidiyon nata na marke.

“Idan har tana son zaman lafiya a rayuwarta, to dole ta daina jifa da shisshigi wa mutane, wannan shi ne. Allah Ya sa mu dace.”

Jamilu Sani a nasa ɓangaren cewa ya yi “a cikin lamarinki akwai wa’azi. A baya kece mai yaɗa bidiyon waɗansu idan sun yi irin wannan abin da kika kira kuskure, yau sai Allah Ya kama ki domin ki ji yadda kika jiyar da ’yan uwanki mata marasa tarbiyya da tunanin gobe.”

Ya ƙara da yin kira ga sauran mutane cewa Babiana da ire-irensu marasa “hangen nesa, sun yi aiki marar kyau a ɓoye. Sun yi wa kansu bidiyo, idan suka tuba , tuba na gaske, sai Allah Ya yafe musu.”

Hafsat Muhammed cewa ta yi, “Ita har ta manta duk abubuwan da ta yi wa mutane, kuma har yau ba ta nemi yafiyarsu ba har tana ma kanta kirari da ‘Queen of Update.’”

Abdulwahab Sa’id Ahmad a shafinsa na Facebook wallafawa ya yi cewa: “Wanda yake da cutar Depression ba shi yake ganewa ba sai dai a gane masa.

“Mahaukaci bai san yana hauka ba sai dai a ba shi labari bayan ya warke

“Ki bar nunawa cewa Musulmi sun yi watsi da ke da ’yan Arewa, ke ce ki ka zaɓi ki zauna a yadda ki ke.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Ta Ce HKI Tana Jinkirta Neman Gawakin Yahudawa A Gaza

Wani babban jami’in kungiyar Hamas a gaza ya bayyana cewa HKI tana dakile kokarinda kungiyar take na nemo da kuma mayar da gawakin yahudawan Sahyoniya da suka halaka saboda barin wutan da sojojin ta suka  yi kan gaza, wanda ya kai ga mutuwar jami’ansu da suka bawa aikin kula da yahudawan.

Don haka wannan ya sa suka rasa samun wadan nan jami’insu saboda sun mutu, sun kuma mutu tare da yahudawan da suke hannunsu. Kungiyar Hamas bata san a dai dai inda suke ba a lokacinda aka kashe su, don haka akwai bukatar lokaci kafin su gano wadannan mutane.

Wasunsu sun karkashin burmudhin gine-gine a gaza wanda yake bukatar kwacesu kafin a kai ga gawakinsu. Don haka lai gwamnatin yahudawanne da sojojinsu. Ya ce, kafin haka mun yi kashedi ga HKI kan cewa hare-harensu yana barazana ga ruyuwar wadan nan yahudawa.

Ya ce a halin yanzu sun mika yahudawa 20 da ransu da kuma gawaki 4. Amma a halin yanzu yahudawan suna barazanar zasu rufe kofar Rafah su kuma rage yawan agajin da ke shigowa Gaza. Daga karshe yace, duk tare da matsaloli Hamas tana kokarin ciki al-kawalin da suka dauka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yansandan Italiya Sun Kara Da Masu Goyon Bayan Falasdinawa A Garin Udine October 15, 2025 Iran Ta Yi Allah Wadai Da Kalaman Kin Jinin Iran Da Trump Ya Yi A Majalisar Dokokin Isra’ila                            October 15, 2025 A Lokacin Yaki, Iran Ta Tarwatsa Wata Cibiyar Leken Asirin Yahudawan Sahayoniyya Da Ke Yankin Farar Hula October 15, 2025 Shugaban Kasar Columbia Ya Yi Dirar Mikiya Kan Donald Trump Kan Bai Wa Isra’ila Makamai October 15, 2025 Kungiyar Jihadul-Islami Ta Falasdinu Ta Ce; ‘Yantar Da Fursunonin Falasdinawa Abu Ne Mai Muhaimmanci October 15, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Ta Bayyana Cewa: Sake Gina Gaza Zai Ci Dala Biliyan 70 October 15, 2025 Araghchi : Trump bai cancanci mai samar da zaman lafiya ba October 14, 2025 UNDP : An ruguza fiye da kashi 80 cikin 100 na gine-ginen Gaza October 14, 2025 Sojojin Madagaska sun karbe mulkin kasar October 14, 2025 Trump ya ce zai yi shawara game da batun kafa kasar Falasdinu October 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce HKI Tana Jinkirta Neman Gawakin Yahudawa A Gaza
  • ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Bayyana Cewa: Sake Gina Gaza Zai Ci Dala Biliyan 70
  • Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
  • Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata
  • Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata
  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • An Kara Zaburar Da ‘Yan Arewa Game Da Muhimmancin Mallakar Katin Zabe
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi