Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce an samar da isassun matakan tsaro domin kawar da wasu gungun miyagu da ke aikata munanan laifuka a jihar.

 

AbdulRazaq ya bayyana hakan ne yayin da ya bayyana wa masu ruwa da tsaki daga yankin Lafiagi na jihar Kwara ta Arewa kan dimbin kokarin gwamnatin jihar a wani taro da aka gudanar a Ilorin.

 

Gwamnan ya amince da damuwar al’ummar tare da tabbatar musu da matakin da gwamnati ke jagoranta kan lamarin.

 

Ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kai hare-hare a dazuzzukan da aka gano a matsayin sansanin ‘yan ta’adda a Kwara ta Arewa da Kudu.

 

Gwamna AbdulRazaq ya ce ayyukan za su hada da sabbin jami’an tsaron dazuzzukan da aka horas da su a wuraren da aka kebe.

 

Ya kara da cewa, ayyukan za su fatattaki ‘yan ta’addan daga maboyarsu tare da dawo da kwanciyar hankali a yankunan da abin ya shafa, ya kuma kara da cewa za a yi taka-tsan-tsan don hana ’yan ta’adda yin katsalandan a wasu wurare.

 

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin jihar na hada hannu da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro domin kawar da barazanar da ake fuskanta a sassan jihar, musamman ma kauyukan da aka gano a kananan hukumomin Ifelodun, Edu da Patigi.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA October 13, 2025 Labarai Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano October 13, 2025 Manyan Labarai Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Ministan Yada Labarai Ya Bayyana Jihar Borno A Matsayin Mafi Juriya A Najeriya
  • Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno