Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara
Published: 7th, July 2025 GMT
Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce an samar da isassun matakan tsaro domin kawar da wasu gungun miyagu da ke aikata munanan laifuka a jihar.
AbdulRazaq ya bayyana hakan ne yayin da ya bayyana wa masu ruwa da tsaki daga yankin Lafiagi na jihar Kwara ta Arewa kan dimbin kokarin gwamnatin jihar a wani taro da aka gudanar a Ilorin.
Gwamnan ya amince da damuwar al’ummar tare da tabbatar musu da matakin da gwamnati ke jagoranta kan lamarin.
Ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kai hare-hare a dazuzzukan da aka gano a matsayin sansanin ‘yan ta’adda a Kwara ta Arewa da Kudu.
Gwamna AbdulRazaq ya ce ayyukan za su hada da sabbin jami’an tsaron dazuzzukan da aka horas da su a wuraren da aka kebe.
Ya kara da cewa, ayyukan za su fatattaki ‘yan ta’addan daga maboyarsu tare da dawo da kwanciyar hankali a yankunan da abin ya shafa, ya kuma kara da cewa za a yi taka-tsan-tsan don hana ’yan ta’adda yin katsalandan a wasu wurare.
Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin jihar na hada hannu da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro domin kawar da barazanar da ake fuskanta a sassan jihar, musamman ma kauyukan da aka gano a kananan hukumomin Ifelodun, Edu da Patigi.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe
Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya gargaɗi sarakunan gargajiya a faɗin ƙananan hukumomi 11 na jihar kan zargin hannu a mamaye hanyoyin kiwo da filayen kiwo, abin da ke haddasa rikici tsakanin makiyaya da manoma.
Gwamnan ya nuna damuwa kan rahotannin da ke cewa wasu sarakuna na karɓar cin hanci suna kuma ba da damar shiga filayen kiwo ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ke ƙara tayar da zaune tsaye a tsakanin al’umma.
Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka“Duk wanda aka kama yana da hannu a wannan aika-aikar, za mu hukunta shi bisa doka,” in ji Gwamna.
Ya kuma roƙi makiyaya da su guji shiga gonaki domin hakan na haifar da rikici maras amfani.
Ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta aiwatar da shawarwarin kwamitin da ke bincike kan lamarin, tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa ta hanyar kare hanyoyin kiwo da tabbatar da adalci wajen amfani da filaye.