Aminiya:
2025-07-07@15:57:07 GMT

’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, sun Jikkata 4 a Borno

Published: 7th, July 2025 GMT

An kashe mutane tara tare da jikkata wasu huɗu a wani da mayakan Boko Haram suka kai yankin a Malam Fatori da ke Jihar Borno.

Gwamna Babagana Zulum, wanda baya kasar a halin yanzu, ya tura tawaga ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Ƙananan Hukumomi, Sugun Mai Mele, domin jajanta wa waɗanda abin ya shafa da kuma tantance halin da ake ciki.

Mai Mele ya jaddada aniyar Gwamna Zulum na jajircewa wajen tabbatar da tsaron Malam Fatori saboda muhimmancinsa.

Ya sanar da shirin tura manyan injina domin tona ramuka a kusa da hedikwatar ƙaramar hukumar don hana hare-hare nan gaba daga Boko Haram da ISWAP.

Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato Sarkin Ibadan ya rasu yayin da ake shirin bikin cikarsa shekara guda a mulki

Haka nan kuma ya gargaɗi mazauna yankin kan haɗin gwiwa da ’yan tawaye, inda ya yi barazanar “sakamakon Ubangiji” ga duk masu haɗin gwiwa.

An bayar da tallafin kuɗi, inda aka bai wa duk gidan da suka asa yan uwa ₦500,000, yayin da waɗanda suka jikkata huɗu kowannensu ya samu ₦250,000.

A halin yanzu, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Tsaro na Cikin Gida, Usman Tar, ya sanar da shirin sake tsugunar da ƙarin iyalai 3,000 da suka rasa matsugunansu a Malam Fatori, wanda hakan zai kai ga jimlar gidaje 5,000 da aka sake tsugunar da su.

Tar ya tabbatar wa mazauna yankin ci gaba da ƙoƙarin gwamnati na samar da matakan tsaro da kayan aiki don dawwamammen dawowar su, yana mai kira gare su da su ci gaba da kasancewa a faɗake tare da kai rahoton duk wani abu da ba a aminta da shi ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI

Rahotanni daga kudanci Lebanon sun ce, sau uku jiragen yakin HKI su ka kai hare-hare a kan gidajen mutane da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya da kuma jikkatar wasu da dama.

A garin Shaqra’dake yankin Bint-jubail, jiragen sama marasa matuki sun kai hare-hare da ya yi sanadiyyar jikkatar mutane biyu da raunuka, kamar yadda ma’aikatar kiwon lafiya ta Lebanon ta sanar.

Har ila yau wani jirgin maras matuki na abokan gaba ya kai wani harin akan wata mota a yankin “Safful-Hawa” da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya.

A garin Shab’a kuwa ‘yan sahayoniyar sun kai hari akan wani gida, wanda ya yi sanadiyyar jikkatar mutanen dake cikinsa.

Majiyar asibiti a garin Marja’iyyun ta ce an kai mata wani mutum wanda ya sami raunuka masu hatsari.

HKI dai tana ci gaba da kai hare-hare akan kasar Lebanon bayan tsagaita wutar yaki a shekarar da ta gabata.   

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Rasha Tana Ci Gaba Da Karya Kadarin Kasashen Turai A Yakin Da Suke Yi A Ukraine  
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a Borno
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
  • Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
  • Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC
  • Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka
  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno