Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-15@12:21:26 GMT

Olubadan Na Ibadan Ya Rasu Yana Da Shekara 90

Published: 7th, July 2025 GMT

Olubadan Na Ibadan Ya Rasu Yana Da Shekara 90

Olubadan na Ibadan, Oba Owolabi Olakulehin ya rasu, yana da shekara 90 a duniya.

Kakakin iyalan basaraken ne ya tabbatar da mutuwarsa da safiyar yau Litinin cikin wani saƙo da ya aike wa manema labarai.

Kwanaki biyu da suka gabata ne basaraken ya gudanar da bikin cikarsa shekara 90 a duniya a wani ƙasaitaccen biki da aka gudanar a fadarsa.

A shekarar da ta gabata ne aka naɗa Sarki Olakulehin a matsayin Olubadan na Ibadan bayan rasuwar wanda ya gabace shi Sarki Alli Okunmade II.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Rasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali

Babbar Kotun Jihar Kano a ranar Talata ta bayar da umarnin aikewa da Ogugua Christopher zuwa gidan gayarn hali bisa zarginsa da hannu a sata da kuma safarar yara daga jihar Kano zuwa kudancin Najeriya.

Ana dai zargin mutumin ne da mallakar wani gidan marayu a jihar Delta ba bisa ka’ida ba, sannan yana amfani da shi wajen ajiye yaran da ake zargin na sata ne a ciki.

Majalisa ta gayyaci CBN da bankunan kasuwanci kan yawan cire wa kwastomomi kuɗaɗe DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?

Hukumar Hana Fatucin Mutane ta Kasa (NAPTIP) ce dai da gurfanar da Christopher tare da wasu abokar harkallarsa su biyu, Hauwa Abubakar da Nkechi Odlyne, wadanda su ba su je kotun ba a ranar.

Alkalin kotun, Mai Shari’a Amina Adamu ce ta bayar da umarnin kullewar yayin fara sauraron shari’ar, bayan sauraron bukatar lauyan masu kara, Salisu Muhammad Tahir da na wanda ake karar, Gideon Uzo.

Daga nan ne kuma kotun ta dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 27 ga watan Oktoba inda ake sa ran za a gurfanar da Christpher tare da sauran wadanda ake zargin.

An dai kama Chrispoher ne bayan wani samame da jami’an hukumar ta NAPTIP suka kai gidan nasa da ke jihar Delta sannan suka ceto yara takwas da ake zargin ya sace su daga Kano sannan ya kai su gidan marayun nasa da ke Asaba, babban birnin jihar ta Delta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta aike da mutumin da ake zargi da satar yaran Kano yana kaiwa Delta zuwa gidan gyaran hali
  • Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • Aragchi Yana Uganda Don Halattan Taron Ministocin Kungiyar NAN
  • Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu
  • Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa