Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
Published: 7th, July 2025 GMT
Mummunan lamari ya faru ne a lokacin da wata mota kirar bas ta kasuwanci da wata babbar mota ta yi taho-mu-gama da tare da daukar rayukan mutane 21 a hanyar Zariya zuwa Kano.
Hadarin ya afku ne a Kasuwar Dogo, Dakatsale, wanda ya hada da wata motar kasuwanci kirar Toyota Hiace da wata tirela ta DAF.
Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ta bayyana cewa, binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa direban motar bas din ya saba ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa, lamarin da ya kai ga yin karo da babbar motar da ke zuwa.
Hatsarin ya yi sanadiyar mutuwar fasinjoji 21 nan take, wadanda suka hada da manya maza 19 da manya mata 2, yayin da wasu uku suka samu raunuka, kuma an kai musu daukin gaggawa.
Jami’an FRSC tare da sauran kungiyoyin bayar da agajin gaggawa sun isa wurin domin gudanar da aikin ceto tare da kwashe tarkacen motocin, wanda hakan ya baiwa ababen hawa damar ci gaba da amfani da hanyar.
Da yake tofa albarkacin bakinsa, Shugaban Rundunar FRSC, Marshal Shehu Mohammed, ya bayyana matukar alhininsa game da asarar rayuka da aka yi, ya kuma jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa.
Ya kuma tabbatar da cewa, ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike domin gano cikakken al’amuran da suka faru a hatsarin.
“Wannan mummunan bala’i kuma wani abin tunawa ne mai raɗaɗi na mummunan sakamakon rashin biyayya ga dokokin hanya,” in ji shi.
“Tuƙi gangaci da wuce gona da iri sune manyan abubuwan da ke ba da gudummawa ga irin waɗannan bala’o’in da za a iya gujewa a kan hanyoyinmu.”
Rundunar ta Corps Marshal ta bukaci dukkan direbobi musamman masu sana’ar tuki da su bi ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa.
Ya kuma jaddada cewa za a kara kaimi wajen tabbatar da tsaro da wayar da kan jama’a domin hana ci gaba da asarar rayuka.
Hukumar ta FRSC ta yi kira ga masu amfani da hanyar da su kai rahoton hatsarita hanyar kiran lambar kyauta 122, ko kuma a tuntubi duk wata tawagar sintiri ta FRSC.
An ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a asibitin Nasarawa dake Kano, inda ake jiran tantancewa da kuma mikawa iyalansu.
Rel/Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hatsari
এছাড়াও পড়ুন:
Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
Adadin mutanen da suka yi shahada sakamakon kisan kiyashin da ‘yan sahayoniyya suke yi a Gaza ya doshi 65,000
Adadin mutanen da suka yi shahada sakamakon yakin da yahudawan sahayoniyya suka kakaba wa Falasdinawa a yankin Zirin Gaza ya karu zuwa shahidai 64,871 da kuma jikkatan wasu 164,610 tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekarar 2023.
Bisa kididdigar baya-bayan nan da ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta fitar a zirin Gaza a ranar Lahadin da ta gabata, mutane 12,321 ne suka yi shahada yayin da wasu 52,569 suka samu raunuka tun bayan da gwamnatin mamayar Isra’ila ta sake komawa yaki kan Falasdinawa a ranar 18 ga watan Maris.
A cikin sa’o’i 24 da suka gabata, Falasdinawa 68 ne suka yi shahada tare da jikkatan wasu 68 da aka isa da su zuwa asibitocin Gaza.
Haka nan wasu Falasdinawa 10 sun yi shahada wasu 18 kuma suka jikkata da aka kai su asibitoci, lamarin da ya kawo adadin wadanda hare-haren ta’addancin ya rutsa da su a cikin bala’in neman tallafin abinci suka haura zuwa shahidai 2,494 da kuma wasu fiye da 18,135 da suka samu raunuka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Larabawa Da Na Musulmi Sun Fara Taro A Qatar. September 14, 2025 Gwamnatin Najeriya Ta Sanar Da Sabon Sharadi Na Bude Asusun Banki September 14, 2025 An Zabi Issa Tchiroma A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A Kamaru September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci