Ba tarbiyya nake koyarwa ba — Sadiq Sani Sadiq
Published: 19th, March 2025 GMT
Fitaccen jarumi a Masana’antar Kannywood Sadik Sani Sadik ya ce shi ba fadakarwa yake yi a fim ba, inda ya ce neman kuɗi kawai yake yi.
Jarumin ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da Gidan Rediyon Freedom, inda a ciki yake cewa ba tarbiyya yake koyarwa ba, ballantana a ce yana bata tarbiyyar.
Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a RibasA cewarsa, “Ni ban ce ina fadakarwa ba.
“Tarbiyya ana ba yaro daga gida ne, fadawarka kuma malamai ne ke yi. Ni ba mai fadakarwa ba ne. Ni mai neman kudi ne.
“Shi fim ba ya da yare, ba ya da addini, saboda haka ya danganta da yanayin da za ka gudanar da fim dinka.
“Idan danka ya kalli fim dina, tarbiyyarsa ta tabu, ba daga ni ba ne, daga kai ne. Idan ma danka bai kalli fim din Hausa ba, zai kalli na Indiya da wakokin Turawa da ake rungume-rungume.
“Ni kuma a fim din Hausa idan na taba hannun mace ya zama abin magana, ban isa ba wallahi.”
Game da mata sun fi maza samun kudi, sai ya ce, “Wasu matan sun fi wasu mazan kudi.
“Kudi ai sirri ne ba wai ka ga mutum ya hau motoci ko ya sanya gwala-gwalai ba ne.
“Ya danganta ne, wani idan yana da dubu daya sai ka gane, wani kuma yana da miliyan daya, amma ba za ka gane ba.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
Shugaba Bola Tinubu ya naɗa tsohon babban hafsan tsaron, Janar Christopher Gwabin Musa a matsayin sabon Ministan Tsaron Nijeriya
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar ranar Talata.
An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a YobeSanarwar ta bayyana cewa Shugaba Tinubu ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio wasiƙar sanar da shi sabon naɗin da ya yi.
Naɗin Janar Musa na zuwa ne kwana guda bayan murabus ɗin Mohammed Badaru Abubakar, wanda ya sauka daga muƙaminsa ranar Litinin saboda dalilai na rashin lafiya.
Aminiya ta ruwaito cewa a jiya Litinin ce Janar Musa ya yi wata ganawar sirri da Shugaba Tinubu, sa’o’i kaɗan gabanin sanar da murabus ɗin Mohammed Badaru.
Musa wanda zai cika shekara 58 a ranar 25 ga Disamba, ya yi aiki a matsayin Babban Hafsan Tsaro daga 2023 har zuwa Oktoban 2025 lokacin da Shugaban Kasa ya sauke shi daga muƙamin a watan Oktoba, bayan wani yunkurin juyin mulki da aka yi.