Aminiya:
2025-12-07@16:13:30 GMT

Ba tarbiyya nake koyarwa ba — Sadiq Sani Sadiq

Published: 19th, March 2025 GMT

Fitaccen jarumi a Masana’antar Kannywood Sadik Sani Sadik ya ce shi ba fadakarwa yake yi a fim ba, inda ya ce neman kuɗi kawai yake yi.

Jarumin ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da Gidan Rediyon Freedom, inda a ciki yake cewa ba tarbiyya yake koyarwa ba, ballantana a ce yana bata tarbiyyar.

Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas

A cewarsa, “Ni ban ce ina fadakarwa ba.

Ni Sadik Sani Sadik ban ce ina fadakarwa ba. Ban ce ina tarbiyyantarwa ba.

“Tarbiyya ana ba yaro daga gida ne, fadawarka kuma malamai ne ke yi. Ni ba mai fadakarwa ba ne. Ni mai neman kudi ne.

“Shi fim ba ya da yare, ba ya da addini, saboda haka ya danganta da yanayin da za ka gudanar da fim dinka.

“Idan danka ya kalli fim dina, tarbiyyarsa ta tabu, ba daga ni ba ne, daga kai ne. Idan ma danka bai kalli fim din Hausa ba, zai kalli na Indiya da wakokin Turawa da ake rungume-rungume.

“Ni kuma a fim din Hausa idan na taba hannun mace ya zama abin magana, ban isa ba wallahi.”

Game da mata sun fi maza samun kudi, sai ya ce, “Wasu matan sun fi wasu mazan kudi.

“Kudi ai sirri ne ba wai ka ga mutum ya hau motoci ko ya sanya gwala-gwalai ba ne.

“Ya danganta ne, wani idan yana da dubu daya sai ka gane, wani kuma yana da miliyan daya, amma ba za ka gane ba.”

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC

Kakakin Majalisar Dokokin jihar Ribas, Martin Amaewhule tare da mambobin majalisar su 15 sun sanar da sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Amaewhule ya bayyana shawarar ’yan majalisar ne a zaman majalisa na ranar Juma’a, inda ya ce akwai abin da ya kira “rarrabuwar kai a fili” a cikin PDP wanda ya sa suka yanke wannan shawara.

Muna tafe da karin bayanai…

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166
  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Amurka ta Faɗaɗa Jerin ƙasashen Afrika Da ta Sanya wa Takunkumin Visa
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC