Sheikh Ibrahim Zakzaky Ya Taya JMI Murnar Nasara A Kan Mikiyanta
Published: 7th, July 2025 GMT
Shugaban Kungiyar Harka Islamia a tarayyar Najeriya Sheikh Irahim Zakzaky ya taya mutanen kasar murna saboda nasarar da suka samu kan HKI da kuma Amurka a yakin kwanaki 12 a cikin watan da ya gabata.
Ya ce wannan nasarar bata takaita da mutanen kasar Iran kadai ba , hada har da al-ummar Musulmi da kuma da kuma masu sun yenci a ko ina suke.
Ya kuma yaba da yadda gikuwan nmalamai na kasar Iran suka sami nasarar kare kasar daga mafi yawan hare-haren HKI a kan kasar.
Ya bayyana cewa Iran ta sami nasara a kan kasashen yamma da makamai wadanda suka fi nasu karfi da inganci, har’ila yau sun sami nasara a kan ma;aikatan yahudawan da suke taimaka masu a cikin kasar. Daga karshe yace kasashen yamma sun yo kokarin boye wannan shan kayen da suka yi a hannun Iraniyawa tare da taimakon All.. ya kuma ji dadi yadda wannan yakin ya kara hada kan mutanen kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
A yau Asabar ne ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwaran aikinsa na kasar Ghana Samuel Okudzeto Ablakwa, suka aikewa juna sakon murnar cika shekaru 65, da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.
A cikin sakonsa Wang Yi ya bayyana cewa, cikin shekaru 65, an raya dangantaka tsakanin Sin da Ghana yadda ya kamata, kana an karfafa imani da juna kan harkokin siyasa, tare da samun manyan nasarori a hadin gwiwarsu ta fannoni daban daban. Kazalika, sassan biyu sun goyi bayan juna a fannin kulawa da harkokin kasa da kasa.
Wang Yi ya ce, ana fatan yin kokari tare da minista Ablakwa, wajen kara fadada mu’ammala a tsakanin ma’aikatun harkokin wajen kasashen biyu, da goyon bayan juna, da aiwatar da manufofi da aka amince da su, a gun taron koli na Beijing, na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, don sa kaimi ga daga dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakanin Sin da Ghana zuwa sabon matsayi.
A nasa bangare, minista Ablakwa ya bayyana cewa, kasar Ghana na godewa Sin, bisa samar mata da gudummawa, da goyon baya a fannonin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma. Ya ce an samu manyan nasarori a fannin hadin gwiwar sassan biyu karkashin tsarin dandalin FOCAC, wanda hakan ya samar da babbar gudummawa ga kasashen Afirka ciki har da Ghana, wajen inganta karfinsu na samun ci gaba, kuma hakan zai amfani jama’ar kasashen Afirka baki daya. Bugu da kari, kasar Ghana tana fatan kokartawa tare da kasar Sin, wajen sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare yadda ya kamata. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp