An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
Published: 7th, July 2025 GMT
Shugaban kasa Bola Tinubu ya ce gwamnatin tarayya za ta gudanar da aikin samar da wutar lantarki ga jami’ar tarayya ta Kashere da ke jihar Gombe domin tabbatar da samar da isasshen wutar lantarki domin inganta harkokin ilimi.
Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen taron hadaka karo na uku na jami’ar tarayya ta Kashere da ke karamar hukumar Akko a jihar Gombe.
Shugaba Bola Tinubu ya kuma bayyana cewa ma’aikatar albarkatun ruwa ta tarayya za ta fara aikin gina madatsar ruwa a kogin Kashere domin tallafa wa shirin koyar da aikin gona na jami’ar da inganta samar da ruwa ga al’ummomin da ke kewaye.
Ya jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta samar da ingantaccen ilimi ta hanyar shiga tsakani na asusun bayar da lamuni na ilimi na kasa (NELFUND).
Ya kuma bukaci jami’o’in Najeriya da su binciko tsarin samar da kudade mai ɗorewa yana mai cewa dole ne zamanin dogaro da kai ga ayyukan gwamnati ya ba da dama ga sabbin hanyoyin samar da kudaden shiga, da haɗin gwiwar dabarun bunƙasa dukiyoyi da kuma asusun bayar da tallafi na gari.
A jawabinsa na maraba, Shugaban jami’ar tarayya ta Kashere, farfesa Umar Pate, ya bayyana cewa martabar jami’ar tana karuwa ne saboda shekaru masu yawa na tsare-tsare da hangen nesa na Hukumar gudanarwar jami’ar.
Ya ce cibiyar ta ba da fifikon dacewa da ilimi ta hanyar ingantaccen ayyukan bincike da haɗin gwiwa tare da sahihan cibiyoyi na ƙasa da ƙasa.
HUDU Shehu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
Wacce irin gudunmwa kafofin samun ilimi suke badawa ta yadda za a samu hanyar kara ilimi
A kokarin da ake yi na yadda za a samar da dama wadda kowa zai iya samun ilimi mai kuma inganci,ta kuma kafofin sadarwa na zamani. Hanyoyin koyo da kafofin sadarwa na zamani,kamar digirin da ake yi saboda yin karatun digiri ta kafar sadarwa ta zamani,da kuma a kasnce kamar ana cikin aji ne,saboda a ba dalibai wata dama wadanda kuma suka kasance daga wuraren da suka bambanta, manufa anan itace yadda suka zo daga wurare daban daban.Rin wannan ci gaban wanda ya kan kasance ga mutane ko al’umma daban daban,wadanda zasu iya fuskantar bambanci saboda daga wurin da suka fito, lamarin kudi,ko kuma sauran wasu dalilai na dabaru ko salon ilimi.
Alal misali,yadda aka samu tafarkin tsarin ilimi ta kafar sadarwa ta zamani,musamman ma digiri,wanda hakan ya ba dalibai dama su kammala iliminsu ba tare da bata lokaci ba,ba tare da rasa ingancin abin ba.Su wadannan tsare tsaren karatun suna taimakawa manya wadanda suke yin aiki,Iyaye,da kuma sauran al’umma wadanda suke da zummar ganin sun samu shiga tafarkin samun aikiand.Ta bada dama ga wadanda suke son samun damar yin karatu,ta hakan ne za su iya samun damar mallakar takardun sheda na digiri,a cin lokaci ba mai tsawo ba,wato kamar shi irin zabin yaba da dama abin bay a tsaya kan lamarin kashe kudade masu yawa ba, ya samu damar inganta ko samun ilimi mai zurfi wanda hakan wani mataki ne na samun daidaituwar bambancin da ake da shi yadda ake samun bambance- bambance na ilimi a a kasashen duniya.
Bugu da kari ire-iren su nayoyin kara karatu na kafafen sadarwa na zamani,suna taimakawa masu koyo su samu taimakon kasashen waje ko samun damar yadda za su gana da tsararrakinsu a duniya,kai harma su samu damar wani lokaci da zasu damar tattaunawa wadda zata taimaka masu.Irin ita damar idan aka same ta,tana tabbatar da kamar yadda shi ilimi wanda bai da wata iya da za ace kar ya wuce ta,bunkasa ilimi wata dama ce wadda kowa yake son cimmawa. Idan har aka samu damar yin amfani da fasaha, hakan yana bada muhimmaiyar dama ta samun samar da daidaituwar ilimin da ake da shi tsakanin wannan kasa da waccan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp