An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
Published: 7th, July 2025 GMT
Shugaban kasa Bola Tinubu ya ce gwamnatin tarayya za ta gudanar da aikin samar da wutar lantarki ga jami’ar tarayya ta Kashere da ke jihar Gombe domin tabbatar da samar da isasshen wutar lantarki domin inganta harkokin ilimi.
Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen taron hadaka karo na uku na jami’ar tarayya ta Kashere da ke karamar hukumar Akko a jihar Gombe.
Shugaba Bola Tinubu ya kuma bayyana cewa ma’aikatar albarkatun ruwa ta tarayya za ta fara aikin gina madatsar ruwa a kogin Kashere domin tallafa wa shirin koyar da aikin gona na jami’ar da inganta samar da ruwa ga al’ummomin da ke kewaye.
Ya jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta samar da ingantaccen ilimi ta hanyar shiga tsakani na asusun bayar da lamuni na ilimi na kasa (NELFUND).
Ya kuma bukaci jami’o’in Najeriya da su binciko tsarin samar da kudade mai ɗorewa yana mai cewa dole ne zamanin dogaro da kai ga ayyukan gwamnati ya ba da dama ga sabbin hanyoyin samar da kudaden shiga, da haɗin gwiwar dabarun bunƙasa dukiyoyi da kuma asusun bayar da tallafi na gari.
A jawabinsa na maraba, Shugaban jami’ar tarayya ta Kashere, farfesa Umar Pate, ya bayyana cewa martabar jami’ar tana karuwa ne saboda shekaru masu yawa na tsare-tsare da hangen nesa na Hukumar gudanarwar jami’ar.
Ya ce cibiyar ta ba da fifikon dacewa da ilimi ta hanyar ingantaccen ayyukan bincike da haɗin gwiwa tare da sahihan cibiyoyi na ƙasa da ƙasa.
HUDU Shehu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
Wasu lauyoyi biyu a Najeriya sun gargaɗi Gwamnatin Tarayya da ta yi taka-tsantsan wajen yin hulɗa da ƙasar Amurka, inda suka ce maganganun Amurka a kan Najeriya abun ruɗarwa ne
Babban lauyan nan, Cuf Okoi Obono-Obla, wanda tsohon mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara ne, ya zargi Amurka da son raba kan ’yan Najeriya da sunan kare Kiristoci.
Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a NijeriyaYa ce iƙirarin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya ƙarya ne face nufin tayar da hankali da kawo rikici.
“Najeriya ba ta taɓa zama barazana ga zaman lafiyar duniya ba,” in ji Obono-Obla.
“Idan Amurka, inda ake yawan harbe mutane a coci-coci, ba ta gayyaci sojojin ƙetare su shigo musu ba, to kamata ya yi ta bar Najeriya ta magance nata matsalolin.”
Ya yi gargaɗin cewa duk wani yunƙurin Amurka na yin katsa-landan cikin harkokin Najeriya zai zama take doka da tauye ikon ƙasa.
Shi ma Barista Leonard Anyogo, kuma shugaban ƙungiyar ‘Good Governance Advocacy International’, ya shawarci Najeriya da ta bi hanyoyin diflomasiyya wajen mayar wa Amurka martani ba da faɗa ba.
“Ya kamata mu tattauna, ba mu yi fada ba,” in ji Anyogo.
“Najeriya ta nemi haɗin kai da Amurka a fannin tsaro da diflomasiyya domin kare muradunta.”