HausaTv:
2025-07-07@23:26:02 GMT

Kenya: Zanga-zanga Ta Tsayar Da Kai Komo A Birnin Nairobi

Published: 7th, July 2025 GMT

Rahotanni da suke fitowa daga kasar ta Kenya sun ce tun safiyar yau Litinin ne ‘yan sanda su ka rufe muhimman hanyoyin da su ka nufi tsakiyar babban birnin kasar Nairobi da kuma muhimman cibiyoyin kasuwanci.

Kafafen watsa labarun kasar ta Kenya sun ce da akwai jami’an ‘yansanda masu yawa da aka girke su a cikin muhimman wurare da shatale-tale a cikin birnin da kuma hanyoyin da suka nufi fadar gwamnati.

 Dubban mutane ne su ka fito titunan birnin Nairobi domin nuna kin amincewarsu da salon Mulki William Ruto wanda suke zargi da cin hanci da rashawa da kuma kama karya.

Zanga-zangar ta yau dai ana ba ta sunan; 7/7, wacce ta samo asali a 1990 da al’ummar kasar su ka yi Zanga-zangar gamagari ta yin kira da a gudanar da zabe  cikin ‘yanci, da a karshe gwamnati ta amince da bukatar hakan.

A watan da ya shude na Yuni masu Zanga-zanga sun kutsa cikin ginin majalisar dokokin kasar da hakan ya tilastawa gwamanti ta janye dokar da ta yi akan harkokin kudade da haraji.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza

Kungiyar Falasdinawa ta Jihadul Islami a Gaza, ta bada sanarwan halaka ko jikatar sojojin yahudawan Sahyoniyya 40 a gaza a wani tarko mai sarkakiyan da suka dana masu.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Saraya Qudus” reshen soje na kungiyar Jihadul Islamim yana fadar haka a jiya Jumma’a.

Daya daga cikin kwamnadojin dakarun ya bayyana cewa da farko halakar yahudawan ta faru ne a garin Gaza a kuma unguwar shuja’iyya. Inda da farko suka halaka sojojin yahudawa kimani 10 a cikin wani ginin da suka shiga cikinsa tare da amfani da makamai mai linzami, sannan a wani gidan

Sannan waso sojojin kimani 20 sun halaka ko sun ji rauni a lokacin dakarun suka yi am,fani da makamin TBG wanda yake watsa isakar gas da ruwa da kuma gari a inda ya fashe don kona jikin wadanda ya fashe a cikinsu.

Na uku kuma sun tana nakiyoyi masu karfi kan tankar yaki dauke da akalla sojojin yahudawa 6 suka kone .

Labarin ya kara da cewa sojojin makiya a irin wannan halin sun kasa daukar wani mataki in banda gudu daga wurin. Daga karshe ba abinda zaka gani sai gawakin sojoji a waste a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miliyoyin Yan Najeriya Ne Suka Gudanar da Tattakin Ashoora Wasu Kuma A Makarantunsu…
  •  Togo: An Yi Kiran Sake Yin Wata Sabuwar Zanga-zanagr Kin Jinin Gwamnati
  • An Yi Gagarumin Taron Ashura A Birnin Beirut Na Kasar Lebanon
  • Miliyoyin Mutane Sun Yi Juyayin Imam Husain ( a.s) A Karbala
  • Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17
  • Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba
  • Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza