Kasar Rasha Tana Ci Gaba Da Karya Kadarin Kasashen Turai A Yakin Da Suke Yi A Ukraine
Published: 7th, July 2025 GMT
Shugaban kasar Rasha ya aike da sako mai zafi wa kasashen Yammacin Turai da suke tallafawa Ukraine
A daidai lokacin da yakin Rasha da Ukraine yake ci gaba da ruruwa, kuma har yanzu an gagara cimma tsagaita wuta. Sabbin abubuwan da suka faru a fagen sojan Rasha sun hada da ma’aikatar tsaron kasar da ta sanar da cewa sojojin kasar sun ‘yantar da garuruwan Poddubnoye na Donetsk People’s Republic da Sobolevka a yankin Kharkiv.
Sanarwar da ma’aikatar tsaron kasar ta fitar ta bayyana cewa: Sojojin kasar Rasha sun ci gaba da zurfafa kai hare-hare kan makiya, inda suka yi ta janyo hasarar bil’adama da na dukiya kan sojojin kasar Ukraine a yankuna da dama na jamhuriyar Donetsk People’s Republic da yankin Dnipropetrovsk. Sojojin Ukraine sun yi hasarar ma’aikata fiye da 390, da motocin yaki masu sulke, da kuma wasu manyan bindigogin fage.
A cikin iska … Jiragen saman Rasha na aiki da dabara sun lalata ababen more rayuwa na filayen jiragen sama na soji, da masana’antar kere-kere, ma’ajiyar ajiyar jirage marasa matuka ciki, da tashar mai da rusa sansanonin sojoji, sannan suka kakkabo bama-bamai na iska guda shida da jiragen sama 298.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
Hukumar IAEA mai kula da ayyukan makamashin nukliya a kasar Iran ta bada sanarwan cewa ma’aikatan hukumar sun fice daga kasar a jiya Jumma’a bayan da gwamnatin kasar ta jingine aiki da ita, bayan hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa cibiyoyin nuklliya na kasar da ke Fordo, Natanz da kuma Esfahan a yakin kwanaki 12 da suka dorawa kasar.
Hukumar ta bada sanarwan cewa ma’aikatan hukumar a Iran suna cikin kasar a lokacin yakin kwanaki 12 kan Iran, kuma a jiya sun bar Tehran zuwa Vienna bayan da gwamnatin kasar ta jingine aiki da ita, kuma tuni sun isa birnin Vienna inda cibiyar hukumar take.
A ranar Alhamis da ta gabata ne ministan harkokin wajen kasar Iran abbas Aragch ya bayyana cewa daga yanzun kuma hukumar zata yi mu’a mala da majalisar tsaron kasa, kan duk wani abu da ya shafi shirin makamashin nukliya na kasar.
Banda haka yace kasar Iran har yanzun bata fice daga yarjeniyar NPT ta hana yaduawar makamashin nukliya ba. Amma hukumar ta bayyana cewa Tehran bata shaida mata a hukumance kan cewa ta jingine aiki da ita ba.
Bayan yakin kwanaki 12, wato a ranar 25 ga watan yunin da ya gabata ne majalisar dokokin kasar Iran ta amince da jingine aiki da hukumar ta IAEA tare da zargin shugabanta Rafael Grossi da zama wanda ya ingiza yakin kwanaki 12 a kan kasar. Sannan yana mika bayanan da ya tattara a iran dangane da shirinta na makamashin nukliya ta zaman lafiya ga HKI.