Kungiyar Jihadul-Islami Ta Falasdinu Ta Sanar Da Shahadar Abu Hamza Kakakin Dakarunta Na Sarayal-Kudus”
Published: 19th, March 2025 GMT
A jiya Talata ne dai kungiyar ta Jihadul-Islami ta kaddamarwa da al’ummar Musulmi shahadar Naji Abu Saif, wanda ake yi wa lakbi da Abu Hamza, da ya kasance kakakin dakarun “Sarayal-Kudus” bayan da ‘yan sahayoniya su ka yi masa kisan gilla tare da iyalansa da iyalan dan’uwansa.
A bayanin da ta fitar, kungiyar ta Jihadul-Islami ta ce; Duniya ta yi sanayya da sautin shahidin wanda ya kasance sauti ne na gwagwarmaya da ba ya tsoron wani zargi akan tafarkin Allah, wanda kuma Allah ya yi wa baiwar fasahar zance da kuma jarunta da kare hakkokin al’ummarmu ta Falasdinu.
Kungiyar ta kuma ci gaba da cewa,kisan gillar da ‘yan sahayoniyar su ka yi wa Abu Hamza wani sashe ne na jerin kisan kiyashin da suke yi wa al’ummar Falasdinu wanda ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa da dama, kananan yara maza da mata.
Kungiyar ta Jiahdul-Islami ta kuma ce;Amurka ce take karfafawa ‘yan sahayoniya gwiwa da kuma taimaka musu akan laifukan da suke yi, tare da bayyana mamaki akan yadda duniya ta sanya idanu tana kallo.
Sai dai kungiyar ta ce; Abinda yake faruwa babu abinda zai karawa Falasdinawa sai tsayin daka da jajurcewa wajen kare hakkokinsu da dakile manufofin abokan gaba baki daya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.
Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.
Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,