Aminiya:
2025-07-07@21:10:37 GMT

Madatsar Ruwan Lagdo na yi wa jihohi 3 na Nijeriya barazanar ambaliya

Published: 7th, July 2025 GMT

Rahotanni sun bayyana cewa mazauna wasu jihohin Nijeriya uku na cikin shirin ko-ta-kwana, sakamakon ƙaruwar fargabar samun ambaliya saboda yiyuwar sakin ruwan Madatsar Lagdo ta Kamaru.

A cewar wani rahoto da jaridar Punch ta wallafa, jihohin da mazauna ke cikin zaman ɗar-ɗar sun haɗar da Benuwe da Edo da kuma Bayelsa, waɗanda tuni suka fara shiri don kauce wa barazanar ambaliyar.

Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a Jos

Sai dai Ma’aikatar Albarkatun Ruwa ta Nijeriya ta yi watsi da rahotonnin da ke cewa an buɗe madatsar ruwan, a yayin da tuni jihohin suka fara shirya wa barazanar.

Gwamnatin Benuwe ta ce ta fara aikin wayar da kan jama’a sakamakon ƙaruwar saukar ruwan sama da ake samu a ’yan kwanakin nan.

Jami’ar yaɗa labarai na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa na Jihar Benuwe, Tema Ager ta ce a yanzu haka suna jiran umarni daga ma’aikatar albarkatun ruwa ta ƙasar.

Sai dai ta ce Ministan Albarkatun Ruwan, Farfesa Joseph Utsev, ya yi watsi da rahotanni da ke cewa Gwamnatin Kamaru fara sako ruwa daga Madatsar Ruwan na Lagdo.

Aminiya ta ruwaito cewa, kusan duk shekara dai Gwamnatin Tarayya takan shawarci al’ummomi da ke yankuna a sahun gaba-gaba da su dauki matakan da suka dace domin dakile illar da ka iya haifar da ambaliyar ruwa saboda bude Madatsar Ruwa ta Lagdo.

Da ma duk shekara sai hukumomin Jamhuriyar Kamaru sun saki ruwan Madatsar Lagdo saboda tumbatsar da take yi, abin da kan janyo mummunar ambaliyar ruwa da ke shafar wasu jihohin Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Kamaru Madatsar Ruwa ta Lagdo

এছাড়াও পড়ুন:

Lauyoyin Majalisar Dattawan Nijeriya Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

A ƙarshe, lauyoyin Majalisar sun ja hankalin lauyoyin Sanata Akpoti-Uduaghan da su yi taka-tsantsan don kauce wa yi wa kundin tsarin mulki kutse ko sanya rikici a majalisa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
  • Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
  • Lauyoyin Majalisar Dattawan Nijeriya Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki
  • Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza
  • Trump Ya Yi Barazanar Ƙarin Haraji Ga Ƙasashen Da Suka Rungumi BRICS
  • An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
  • Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka
  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka
  • Tsadar rayuwa ta sa ’yan Nijeriya na siyan abincin da ya lalace