Madatsar Ruwan Lagdo na yi wa jihohi 3 na Nijeriya barazanar ambaliya
Published: 7th, July 2025 GMT
Rahotanni sun bayyana cewa mazauna wasu jihohin Nijeriya uku na cikin shirin ko-ta-kwana, sakamakon ƙaruwar fargabar samun ambaliya saboda yiyuwar sakin ruwan Madatsar Lagdo ta Kamaru.
A cewar wani rahoto da jaridar Punch ta wallafa, jihohin da mazauna ke cikin zaman ɗar-ɗar sun haɗar da Benuwe da Edo da kuma Bayelsa, waɗanda tuni suka fara shiri don kauce wa barazanar ambaliyar.
Sai dai Ma’aikatar Albarkatun Ruwa ta Nijeriya ta yi watsi da rahotonnin da ke cewa an buɗe madatsar ruwan, a yayin da tuni jihohin suka fara shirya wa barazanar.
Gwamnatin Benuwe ta ce ta fara aikin wayar da kan jama’a sakamakon ƙaruwar saukar ruwan sama da ake samu a ’yan kwanakin nan.
Jami’ar yaɗa labarai na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa na Jihar Benuwe, Tema Ager ta ce a yanzu haka suna jiran umarni daga ma’aikatar albarkatun ruwa ta ƙasar.
Sai dai ta ce Ministan Albarkatun Ruwan, Farfesa Joseph Utsev, ya yi watsi da rahotanni da ke cewa Gwamnatin Kamaru fara sako ruwa daga Madatsar Ruwan na Lagdo.
Aminiya ta ruwaito cewa, kusan duk shekara dai Gwamnatin Tarayya takan shawarci al’ummomi da ke yankuna a sahun gaba-gaba da su dauki matakan da suka dace domin dakile illar da ka iya haifar da ambaliyar ruwa saboda bude Madatsar Ruwa ta Lagdo.
Da ma duk shekara sai hukumomin Jamhuriyar Kamaru sun saki ruwan Madatsar Lagdo saboda tumbatsar da take yi, abin da kan janyo mummunar ambaliyar ruwa da ke shafar wasu jihohin Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Kamaru Madatsar Ruwa ta Lagdo
এছাড়াও পড়ুন:
Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
Gwamnatin kasar Spaine ta soke kontaragin sayan makama daga HKI wadanda yawansu ya kai Euro Miliyon 700, saboda kissan kiyashin da ke faruwa a gaza.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a jiya Litinin ne gwamnatin firay minister Pedro Sanchez ta bada wannan sanarwan ta kuma kara da cewa makaman su ne makamai masucilla rokoki samfurin Elbit kirar HKI.
Labarin ya kara da cewa Madrid ta soke wani kontaragi wanda ya kai Eur miliyon 287 da HKI. Na sayan garkuwan tankunan yaki wadanda za’a kerasu a kasar karkashin lacicin HKI a kasar Espania.
Banda haka firay minister Pedro Sanchez ya bukaci a haramta HKI daga dukkanin wasannin nakasa da kasa saboda kissan kiyashin da take aikata a gaza a ranar Lahadin da ta gabata.
Gwamnatin kasar ta Espania tabayyana cewa tanada shirin daukar wasu karin matakan kan HKI saboda kissan kiyashin datake aikatawa Gaza.
Daga cikinsu har da haramtawa dukkan yahudawan da suke da hannu cikin kissan kiyashin shiga kasar Espania .
Sannan akwai takunkuman tattalin arzikin na hana sayan dukkan kayakin da ake kerawa a kasar Falasdinu da aka mamaye.
Daga karshen gwamnatin kasar Espania ta zargi kasashen turai kan nuna fuska biyu a kissan kiyashin Gaza, idan an kwatanta da na Ukraine.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci