A wani yunkuri na bunkasa samar da wutar lantarki da kuma bunkasar tattalin arziki, gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da rabon kashi na farko na taransfoma 500 ga al’ummomin karkara a fadin kananan hukumomin jihar 44.

 

Gwamna Abba Yusuf ne ya kaddamar da shi a hukumance a Kano a wani shirin da nufin magance kalubalen rashin samar da wutar lantarki.

 

Gwamna Yusuf ya ce samar da taransfoma wani shiri ne na bunkasa masana’antu da zaburar da harkokin kasuwanci musamman a yankunan karkara.

 

“Wannan rabon shi ne kashi na farko na aikin samar da wutar lantarki a yankunan karkara, ba wai kawai wani aikin samar da wutar lantarki ba ne, wani muhimmin mataki ne na inganta samar da wutar lantarki ga jama’armu. Samar da wutar lantarki mai inganci na da matukar muhimmanci ga ci gaban masana’antu da bunkasar tattalin arziki.”

 

Gwamnan ya bukaci masu ruwa da tsakin al’umma da su mallaki na’urar taransifoma gaba daya, sannan ya umurci shugabannin kananan hukumomin da su kafa kwamitoci don kula da ayyukan da kuma tabbatar da tsaro.

 

Kwamishinan Ma’aikatar Raya Karkara da Cigaban Al’umma Abdulkadir Abdulsalam ya yabawa kokarin Gwamnan na inganta rayuwar al’umma da bunkasa tattalin arzikin karkara.

 

“Wannan rabon na nuna alamar ci gaba da yunƙurin da Gwamna ya yi na tunkarar ƙalubalen da al’ummomin karkara ke fuskanta. Na’urar taransifoma za ta inganta rayuwar jama’a sosai, da inganta tattalin arziƙi, da kuma jawo hankalin masu zuba jari.”

 

Bikin ya samu halartar mataimakin gwamnan jihar Kano, kakakin majalisar dokokin jihar Kano, mai martaba Sarkin Karaye, da manyan jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kaddamarwa samar da wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya

Shugaban Hukumar Kula da Asibitoci ta Jihar Kano (HMB), Dakta Mansur Mudi Nagoda, ya kai ziyarar ba-zata ta duba aiki a Asibitin karbar Haihuwa na Imamu Wali, na Marmara, da kuma Asibitin Sabon Bakin Zuwo.

Ya kai ziyarar ce domin tabbar bin umarnin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, na wucin gadi wajen sauya wuraren gudanar da ayyukan karbar haihuwa da na yara zuwa wasu cibiyoyi daban.

A karkashin wannan umarni, an mayar da sashen haihuwa na Asibitin Koyarwa na Muhammad Abdullahi Wase zuwa Asibitin Haihuwa na Imamu Wali, yayin da aka mayar da ayyukan yara kyauta da ake yi a Asibitin Yara na Hasiya Bayero zuwa Asibitin Haihuwa na Marmara.

Wadannan canje-canjen sun biyo bayan ci gaba da gyare-gyare da sabunta wadannan asibitoci, wani muhimmin bangare na hangen nesa na Gwamna Yusuf wajen inganta cibiyoyin lafiya a Kano zuwa matakin kasashen duniya da suka ci gaba.

Domin tabbatar da ci gaba da bayar da ayyuka ba tare da tangarda ba, ma’aikatan sassan da abin ya shafa suma an tura su zuwa sabbin wuraren da aka kebe musu.

Yayin ziyarar, Dakta Nagoda tare da daraktoci da ma’aikatan hukumar, ya jaddada muhimmancin bin umarnin gwamnati yadda ya kamata, tare da yabawa shugabanci da ma’aikatan asibitocin da aka ziyarta saboda hadin kai da jajircewarsu.

Ya kara tabbatar da kudirin hukumar wajen tabbatar da cewa bayar da ayyukan lafiya a Jihar Kano zai ci gaba da kasancewa cikin sauki, da inganci, tare da mayar da hankali kan marasa lafiya, duk da gyare-gyaren da ake yi.

 

Daga Khadijah Aliyu

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Dakta Umar Kabir Yusuf-Bakatsinen da ya kirkiro manhajar Masjid Suite da ke sada zumuncin hada masallaci da masallata
  • Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP
  • Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.