Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a yau Litinin cewa, atisayen da sojojin kasar Sin suka yi a mashigin tekun Taiwan wani muhimmin martani ne ga goyon bayan da kasashen waje ke nunawa kan yunkurin neman “’yancin kan Taiwan,” kuma babban gargadi ne ga ‘yan awaren Taiwan.

Kakakin ta ce, matakin soja da kasar Sin ta dauka ya wajaba, kuma yana bisa doka, ya kuma dace don kare ikon mallakar kasa, da tsaro da kuma cikakkun yankunanta.

Mao ta bayyana hakan ne a lokacin da take ba da amsa ga tambayoyi a taron manema labarai na yau, inda ta ce, rahotanni sun nuna cewa, sojojin kasar Sin sun gudanar da atisayen soji a mashigin tekun Taiwan a yau Litinin. Kuma an yi imanin cewa, atisayen na da nasaba da sauye-sauyen da aka yi a shafin yanar gizon ma’aikatar harkokin wajen Amurka a baya-bayan nan dangane da manufar Taiwan, da kuma ayyukan ‘yan aware masu neman ‘yancin kan Taiwan. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru

Tsohon Ministan Tsaro, Abubakar Badaru, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya san dalilin da ya sa ya yi murabus.

Badaru, ya ajiye aiki ne a ranar Litinin, inda ya ce matsar rashin lafiya ce ta sa ya yi murabus.

Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta

Shugaban ƙasa ya amince da murabus ɗinsa kuma ya naɗa Janar Chris Musa a matsayin sabon Ministan Tsaro.

Badaru, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa ya yi murabus ne saboda barazanar da Amurka ta yi na ɗaukar matakin soji kan Najeriya game da zargin kisan Kiristoci.

“Ina so na bayyana a fili cewa wannan labari ƙarya ne, an ƙirƙire shi don ɓata min suna, kuma ba shi da alaƙa da ni ko wani da ke magana a madadina,” in ji shi.

Ya ce an ƙirƙiro wannan ƙarya ne don a ɓata masa suna da kuma haddasa rikici tsakaninsa da shugaban ƙasa.

“Gaskiyar dalilin murabus ɗina na bayyana ta shugaban ƙasa. Duk wani ƙarin bayani na daban ƙarya ne da aka ƙirƙira,” in ji Badaru.

Ya tabbatar wa Tinubu da ’yan Najeriya cewa har yanzu yana biyayya, tare da jajircewa wajen ganin an samu zaman lafiya, tsaro da nasarar jam’iyyar APC kafin zaɓen 2027.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta ce Tsaron Yankin Tekun Fasha Jan Layi Ne Da Za’a Fuskanci Mayar Da Martani Adan Aka Taba Shi
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru
  • Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • Shugaban Kungiyar ECOWAS  Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • Tawagar ECOWAS za ta je Guinea-Bissau, bayan juyin mulkin soji