Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana a yau Litinin cewa, atisayen da sojojin kasar Sin suka yi a mashigin tekun Taiwan wani muhimmin martani ne ga goyon bayan da kasashen waje ke nunawa kan yunkurin neman “’yancin kan Taiwan,” kuma babban gargadi ne ga ‘yan awaren Taiwan.

Kakakin ta ce, matakin soja da kasar Sin ta dauka ya wajaba, kuma yana bisa doka, ya kuma dace don kare ikon mallakar kasa, da tsaro da kuma cikakkun yankunanta.

Mao ta bayyana hakan ne a lokacin da take ba da amsa ga tambayoyi a taron manema labarai na yau, inda ta ce, rahotanni sun nuna cewa, sojojin kasar Sin sun gudanar da atisayen soji a mashigin tekun Taiwan a yau Litinin. Kuma an yi imanin cewa, atisayen na da nasaba da sauye-sauyen da aka yi a shafin yanar gizon ma’aikatar harkokin wajen Amurka a baya-bayan nan dangane da manufar Taiwan, da kuma ayyukan ‘yan aware masu neman ‘yancin kan Taiwan. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An ɗaura auren Sanata Kawu Sumaila da wata jami’ar soji a Kano

An ɗaura auren Sanatan Kano ta Kudu, Abdulrahman Kawu Sumaila, da Aisha Isah, wata jami’ar soji a Rundunar Sojin Sama ta Najeriya, a wani ɗan ƙwarya-ƙwaryan biki da aka gudanar sali-alin a Rano.

Ɗaurin auren wanda jama’a kaɗan ne suka halarta ya gudana ne da safiyar Litinin ɗin nan a fadar Sarkin Rano da ke Jihar Kano, lamarin da ya nuna cewa ba a yi wata sanarwa ta musamman ba kafin bikin.

Masu ibadar Umarah 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka ’Yan Majalisar Dokokin Taraba 16 sun sauya sheka daga PDP zuwa APC

Mai taimaka wa sanatan kan harkokin yaɗa labarai, Muttaqa Babire, ya tabbatar da auren a shafinsa na Facebook, inda ya wallafa hoton sanatan tare da amaryar cikin kayanta na jami’an soji.

Shi ma wani na hadiminsa, Ahmad Tijjani Kiru, ya wallafa a shafin Facebook cewa: “Alhamdulillah, yau 17-11-2025, an ɗaura auren Sanata S.A. Kawu Sumaila OFR, PhD a Rano. Allah Ya albarkaci rayuwar auren Ya kawo zuri’a ɗayyiba.”

Kawu Sumaila, wanda shi ne shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Albarkatun Mai, a bayan nan ne ya sauya sheƙa daga jam’iyyar NNPP zuwa APC.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3
  • Kasar Maziko Tayi Watsi Da Shirin Trump Na Kai Harin Soji Kan Iyakar Kasar.
  • Iran Ta yi Gargadi Kan Kada Kudurin Amurka Da MDD Ta Amince Da Shi Ya Tauye Hakkin Falasdinawa  
  • Mai taɓin hankali ya kashe soja a Legas
  • Sojojin Najeriya Sun Karyata Cewa “ISWAP” Ta Kashe Wani Babban Jami’i Mai Mukamin  Birgediya
  • Afrika ta Kudu Ta yi Gargadi Game Da Duk Wani Yunkuri Na Fitar Da Falasdinawa Daga Yankin Gaza
  • Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno
  • Na’im Dassim: Gwamnatin Lebanon Zata Yi Babban Kuskure Matukar Tabi Hanyar Sassauci
  • An ɗaura auren Sanata Kawu Sumaila da wata jami’ar soji a Kano
  • Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan