Kakakin hukumar raya hadin gwiwar neman ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin (CIDCA), Li Ming, ya bayyana a gun taron manema labaru na yau Litinin cewa, rage yawan tallafin kasashen waje da Amurka ta yi, da rage fiye da kashi 90 cikin 100 na ayyukan da take yi, sun sabawa alkawuran da ta dauka, da kuma nauyin da ke bisa wuyanta a karkashin tsarin MDD, kuma hakan wani yunkuri ne na ja da baya, wanda kasashen duniya ba sa goyon baya.

Li Ming ya jaddada cewa, alkawarin da kasar Sin ta yi na kara yawan albarkatu ga hadin gwiwar ci gaban duniya, ba zai canza ba. Ya kara da cewa, ka’idojin kasar Sin na kin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu, da kin sanya sharadi na siyasa, da kin yin alkawuran banza suna nan daram. Ban da wannan kuma, yadda kasar Sin ke bin tsarin ba da tallafi na ketare bisa gaskiya da rikon amana, da kudurinta na yin shawarwari bisa daidaito da hadin gwiwar samun nasara tare da kasashe masu ci gaba da masu tasowa ba za su canza ba.

Li Ming ya ci gaba da cewa, dole ne kasashen da suka ci gaba su tabbatar da bin ra’ayin bangarori daban daban bisa gaskiya, da mutunta alkawuransu na tabbatar da ci gaba, da nuna sanin ya kamata, da yin watsi da dabarun tashin wani faduwar wani, da hada kai da kasashe masu tasowa, don ci gaba da aiwatar da ajandar ci gaba mai dorewa ta MDD ta shekarar 2030, da gina al’umma mai makomar bai daya ga bil Adama. (Mohammed Yahaya)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci

Wata sabuwar badakala ta sake bata sunan kungiyar Tarayyar Turai, inda ‘yan sanda suka farmawa gidan toshuwar shugaban kula da manufofin harkokin wajen na kungiyar Federica Mogherini, tare da tsare ta a ranar Talata, a Belgium.

Mogherini wacce ta yi aiki a mukamin tun daga 2014 zuwa 2019, Ita da wasu abokan aikinta biyu ana binciken su kan yadda aka yi amfani da kudaden Tarayyar Turai ba bisa ka’ida ba, cin hanci da rashawa.

Federica Mogherini, jami’ar diflomasiyya ‘yar Italiya mai shekaru 52, ana tsare da ita tare da Stefano Sannino, babban jami’i a Hukumar da kuma mataimakin darakta na Kwalejin Turai.

An kama su, su ukun a wani bangare na binciken da Ofishin Mai Gabatar da Kara na Tarayyar Turai ya jagoranta.

Binciken ya shafi zargin nuna fifiko wajen bayar da shirin horo ga jami’an diflomasiyya.

Ofishin Mai Gabatar da Kara na Tarayyar Turai ya zarge su da “zamba wajen bayar da kwangilolin gwamnati, cin hanci da rashawa, inda ‘Yan sandan Belgium suka gudanar da jerin bincike a ranar Talata a hedikwatar Hukumar Kula da Harkokin Waje ta Tarayyar Turai, a gine-gine da dama na Kwalejin Turai da ke Bruges, da kuma gidajen wadanda ake zargin su uku uku.

Dama dai a cfen baya an gano tarin takardun kudi na Yuro a gidajen ‘yan majalisar dokoki na turai, tare da kyaututtuka daga Qatar, Mauritania, da Morocco. Lamarin da ya girgiza Majalisar Dokokin Turai matuka a watan Disamba na 2022. Ana zargin ‘yan majalisar wakilai da mataimakan majalisar dokoki da dama da karbar cin hanci da rashawa a madadin tasirinsu kan wasu shawarwari na majalisar.

Akwai wasu badakaloli da dama da ake yawan samu a cikin kasashen Turai, musamman game da karkatar da kudaden EU.

A cewar sabon rahoto daga Ofishin Mai Gabatar da Kara na Tarayyar Turai, amfani da kudaden EU ba bisa ka’ida ba ya zama ruwan dare a kasashe 27 na Tarayyar.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu December 3, 2025 Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta December 3, 2025 Kasar Qatar Ta Gargadi Isra’ila Game Da ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza December 3, 2025 Sharhi: HKI tana fama da karancin sojoji a dukkan rassan sojojin kasar December 2, 2025 Shugaba Pizishkiyan:  Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufa December 2, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Janar Chiristopher Musa ( Ritaya) A Matsayin Ministan Tsaro December 2, 2025 Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa December 2, 2025  Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar  Taka Su Da Mota December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale
  • An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela
  • Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran
  • An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci
  • Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare
  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  • Shugaba Pizishkiyan:  Goyon Bayan Al’ummar Iran Ga Tsarin Musulunci Ne Ya Hana Abokan Gaba Cimma Manufar
  • Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa
  • Shugaban Kungiyar ECOWAS  Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi