Seyi Tinubu, ɗan shugaban kasa Bola Tinubu, ya bayyana cewa mahaifinsa shi ne shugaban Nijeriya mafi girma a tarihi, yana yaba wa shugabancinsa da himmarsa wajen bunkasa rayuwar matasa. A cikin wani faifan bidiyo da ya bayyana ranar Litinin, Seyi ya furta wannan magana yayin da yake jawabi ga taron matasa a jihar Adamawa.

Ya ce, “Shi ne shugaban Nijeriya mafi girma a tarihi,” yana mai cewa mahaifinsa ya ba da fifiko ga ci gaban tattalin arziki da samar da dama ga matasa.

Ya kara da cewa, “Shi ne kawai shugaban da ya kiyaye mutanenku a gida, tun lokacin da ya kasance gwamna har ya zama shugaban kasa. Shugaban da ya dauki matasa da muhimmanci, ya samar da dandali don matasa su zama wasu.” Seyi ya kuma bayyana cewa gwamnatin mahaifinsa tana kan kirkiro tattalin arzikin da zai amfanar da kowa, yana mai cewa, “Shi ne kawai shugaban da ba shi da nufin wadatar da kansa.”

Dalilin Da Ya Sa Tinubu Ya Nada Jega A Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Samar Da Sauyin Noma Da Kiwo Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Karramawar Da Sojoji Suka Yi Wa Seyi Tinubu

Kwanan nan, Seyi Tinubu ya shiga cikin ayyukan al’umma, musamman a jihohin arewacin Najeriya, inda aka gan shi yana rarraba kayayyakin abinci. A watan Maris, ya halarci wurare a jihar Kano, inda ya gana da mutane da dama ciki har da shugaban jam’iyyar NNPP na jihar, Hashimu Dugurawa, wajen buda bakin azumin Ramadan.

Haka kuma, Seyi ya ziyarci jihar Yobe a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarinsa na shiga cikin al’umma da matasan Nijeriya. Ayyukansa na ziyartar jihohi da bayar da tallafi ga al’umma sun nuna kokarin da yake yi na kara kusantar jama’a da kuma tallafawa manufofin mahaifinsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya

Rundunar Sojin Saman Najeriya (NAF), ta ce ta taka muhimmiyar rawa wajen daƙile yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin, bayan wasu sojoji sun bayyana hamɓarar da Gwamnatin Shugaba Patrice Talon.

Gungun sojojin, sun bayyana cewa ta rushe gwamnati tare da dakatar da kundin tsarin mulki, da rufe iyakokin ƙasar.

An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano

Sun kuma ayyana Laftanar Kanar Tigri Pascal a matsayin Shugaban gwamnatin soja.

Daga baya gwamnatin Benin ta sanar da cewa sojojin ba su yi nasarar yin juyin mulkin ba.

Rahotanni sun nuna cewa jiragen yaƙin Najeriya sun shiga ƙasar domin kare dimokuraɗiyya, duk da cewa babu cikakkun bayanai ba.

NAF, ta tabbatar da cewa ta yi aiki a Benin bisa yarjejeniyar tsaro ta ECOWAS.

“Sojojin Saman Najeriya sun yi aiki a Jamhuriyar Benin bisa ƙa’idojin ECOWAS da umarnin Rundunar Tsaro ta Yanki,” in ji Air Commodore Ehimen Ejodame.

ECOWAS, ta yi Allah-wadai da yunƙurin juyin mulkin, tare da cewa za ta kare dimokuraɗiyyar ƙasar idan buƙatar hakan ta taso.

“ECOWAS za ta tallafa wa gwamnati da al’ummar Benin, har da tura rundunar tsaro ta yankin, domin kare kundin tsarin mulki da ikon ƙasar,” in ji sanarwar ECOWAS.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
  • Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Isa Abidjan Wajen Rantsar da Shugaba Ouattara
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
  • Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Fadar Shugaban Kasar Benin ta ce Har Yanzu Talon Ne a Kan Mulki
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167