Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaba Tinubu
Published: 17th, March 2025 GMT
Seyi Tinubu, ɗan shugaban kasa Bola Tinubu, ya bayyana cewa mahaifinsa shi ne shugaban Nijeriya mafi girma a tarihi, yana yaba wa shugabancinsa da himmarsa wajen bunkasa rayuwar matasa. A cikin wani faifan bidiyo da ya bayyana ranar Litinin, Seyi ya furta wannan magana yayin da yake jawabi ga taron matasa a jihar Adamawa.
Ya ce, “Shi ne shugaban Nijeriya mafi girma a tarihi,” yana mai cewa mahaifinsa ya ba da fifiko ga ci gaban tattalin arziki da samar da dama ga matasa.
Ya kara da cewa, “Shi ne kawai shugaban da ya kiyaye mutanenku a gida, tun lokacin da ya kasance gwamna har ya zama shugaban kasa. Shugaban da ya dauki matasa da muhimmanci, ya samar da dandali don matasa su zama wasu.” Seyi ya kuma bayyana cewa gwamnatin mahaifinsa tana kan kirkiro tattalin arzikin da zai amfanar da kowa, yana mai cewa, “Shi ne kawai shugaban da ba shi da nufin wadatar da kansa.”
Dalilin Da Ya Sa Tinubu Ya Nada Jega A Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Samar Da Sauyin Noma Da Kiwo Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Karramawar Da Sojoji Suka Yi Wa Seyi TinubuKwanan nan, Seyi Tinubu ya shiga cikin ayyukan al’umma, musamman a jihohin arewacin Najeriya, inda aka gan shi yana rarraba kayayyakin abinci. A watan Maris, ya halarci wurare a jihar Kano, inda ya gana da mutane da dama ciki har da shugaban jam’iyyar NNPP na jihar, Hashimu Dugurawa, wajen buda bakin azumin Ramadan.
Haka kuma, Seyi ya ziyarci jihar Yobe a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarinsa na shiga cikin al’umma da matasan Nijeriya. Ayyukansa na ziyartar jihohi da bayar da tallafi ga al’umma sun nuna kokarin da yake yi na kara kusantar jama’a da kuma tallafawa manufofin mahaifinsa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya
Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), ta bayyana cikakken goyon bayanta ga gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da Mataimakinsa, Kashim Shettima.
Shugabannin ƙungiyar sun kai wa Mataimakin Shugaban Ƙasa, ziyara a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, inda suka gayyace shi zuwa bikin cika shekaru 25 da kafa ACF.
An sanya dokar hana fita bayan ɓarkewar zanga-zanga kan zaɓen Tanzania Gwamnati ta bai wa ASUU N2.3bn domin biyan bashin albashin malamaiShugaban kwamitin amintattu na ACF, Alhaji Bashir Dalhatu, ya yaba da kyakkyawar alaƙar aiki tsakanin Shugaba Tinubu da Shettima, ya bayyana cewa hakan alama ce ta haɗin kai da shugabanci na gari.
“A wajenmu ’yan Arewa, Mataimakin Shugaban Ƙasa shi ne jakadanmu na farko. Yana yin biyayya ga Shugaban Ƙasa kuma yana aiki tuƙuru ba don Arewa kaɗai ba, har ma da Najeriya gaba ɗaya,” in ji Dalhatu.
Dalhatu, ya ƙara da cewa ACF za ta ci gaba da mara wa gwamnati baya tare da ba ta shawarwari masu amfani a duk lokacin da ya dace.
“Muna alfahari da Mataimakin Shugaban Ƙasa da sauran ’ya’yanmu na Arewa da ke cikin gwamnati.
“Za mu ci gaba da goyon bayansu, amma kuma za mu nuna musu wuraren da ake buƙatar gyara domin amfanin dukkanin ’yan Najeriya,” in ji shi.
Ya bayyana cewa ACF, wadda aka kafa a shekara ta 2000, an samar da ita ne domin haɗa kan al’ummar Arewa da kuma ƙarfafa zaman lafiya da ci gaban ƙasa baki ɗaya.
A cewarsa, ƙungiyar ta taka muhimmiyar rawa wajen magance rikice-rikice, tallafa wa ci gaban tattalin arziƙi, da kuma ƙarfafa wa matasa da al’umma gwiwa su dogara da kansu ta hanyar ilimi da sana’o’i.
Dalhatu, ya ce bikin cikar ƙungiyar shekaru 25 da kafuwa, zai zama dama ta haɗa kan ƙasa, inda za su gayyaci manyan ƙungiyoyin yankuna kamar Afenifere, Ohanaeze Ndigbo da PANDEF domin ƙarfafa zumunci da fahimtar juna.
Hakazalika, ya yi fatan bikin zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya a tsakanin ƙabilu Najeriya domin samun ci gaban ƙasa.