Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a Zariya
Published: 7th, July 2025 GMT
Kananan yara uku sun rasu yayin da wasu da shidan ke kwance a asibiti sakamakon sake bullar cutar nan ta mashako a garin Zariya da ke Jihar Kaduna.
Wani mazaunin unguwar Kwarbai a yankin na Zariya, Mallam Bashir Magaji wanda ya rasa ’yarsa sakamakon barkewar cutar wadda a turance ake kira Diphtheria, ya bayyana yadda take bazuwa cikin sauri a kwanakin nan.
A cewarsa, ’yarsa da ta nuna alamun kamuwa da cutar na kumburin wuya da sarkewar numfashi, an gaggauta mika ta Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika, amma daga bisani ta ce ga garinku nan.
Mallam Bashir ya bayyana cewa, tun bayar rasuwar ’yarsa, a yanzu haka an samu wasu karin yaran uku da suka soma nuna alamun kamuwa da cutar kamar dai yadda ta kasance ga ’yarsa.
Sai dai ya ce ya gaggauta kai rahoton lamarin ga wasu muhukuntan lafiya mafi kusa wadanda suka turo tawagar jamiai da ta soma bayar da allurar riga kafi a yankin.
“Na samu labarin cewa alamun cutar sun bayyana a jikin wasu yaran makwabcina biyu da wata mata a layin da nake zama.”
Ya kara da cewa an kwantar da wasu yaran hudu da su ma suka nuna alamun cutar a wata cibiyar lafiya ta Kakaki da ke kusa da Kwarbai, kuma tuni har an sallami yaro daya.
Ya kuma bayyana damuwa kan zargin cewa babu allurar rigakafin cutar a duk fadin Jihar Kaduna, “wadda na samu labarin cewa sai daga Jihar Neja aka kawo mana ita.”
Aminiya ta yi kokarin jin ta bakin sakatariyar lafiya ta Karamar Hukumar Zariya, amma ba ta amsa kiran da wakilinmu ya yi mata ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zariya
এছাড়াও পড়ুন:
Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
Hukumar ƙididdigar a Najeriya NBS ta bayyana cewa an samu raguwar hauhawar farashin kaya a watan Agusta idan aka kwatanta da watan Yulin da ya gabace shi.
Cikin sabbin alƙaluman da NBS ta fitar a ranar Litinin sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.76 a watan Agustan saɓanin watan Yulin, wanda ya nuna karo na hudu ke nan a jere hauhawar farashin yana sauka.
NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murnaRahoton na hukumar NBS na zuwa ne kwanaki bayan da Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin karya farashin kayan abinci ƙasar.
A watanin baya-bayan an riƙa samun raguwar hauhawar farashin kayyaki a ƙasar.
Ko alƙaluman da NBS ta fitar a watan Yuni, ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka zuwa kashi 22.22 daga 22.97 da aka samu a watan Mayu.
A baya dai dai an yi ta kiraye-kirayen gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakan rage hauhawarar farashi domin magance tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar.