Aminiya:
2025-07-07@23:18:56 GMT

Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a Zariya

Published: 7th, July 2025 GMT

Kananan yara uku sun rasu yayin da wasu da shidan ke kwance a asibiti sakamakon sake bullar cutar nan ta mashako a garin Zariya da ke Jihar Kaduna.

Wani mazaunin unguwar Kwarbai a yankin na Zariya, Mallam Bashir Magaji wanda ya rasa ’yarsa sakamakon barkewar cutar wadda a turance ake kira Diphtheria, ya bayyana yadda take bazuwa cikin sauri a kwanakin nan.

Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi Amurka za ta ɗauki nauyin ’yan tawaye domin yaƙi da ta’addanci

A cewarsa, ’yarsa da ta nuna alamun kamuwa da cutar na kumburin wuya da sarkewar numfashi, an gaggauta mika ta Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika, amma daga bisani ta ce ga garinku nan.

Mallam Bashir ya bayyana cewa, tun bayar rasuwar ’yarsa, a yanzu haka an samu wasu karin yaran uku da suka soma nuna alamun kamuwa da cutar kamar dai yadda ta kasance ga ’yarsa.

Sai dai ya ce ya gaggauta kai rahoton lamarin ga wasu muhukuntan lafiya mafi kusa wadanda suka turo tawagar jamiai da ta soma bayar da allurar riga kafi a yankin.

“Na samu labarin cewa alamun cutar sun bayyana a jikin wasu yaran makwabcina biyu da wata mata a layin da nake zama.”

Ya kara da cewa an kwantar da wasu yaran hudu da su ma suka nuna alamun cutar a wata cibiyar lafiya ta Kakaki da ke kusa da Kwarbai, kuma tuni har an sallami yaro daya.

Ya kuma bayyana damuwa kan zargin cewa babu allurar rigakafin cutar a duk fadin Jihar Kaduna, “wadda na samu labarin cewa sai daga Jihar Neja aka kawo mana ita.”

Aminiya ta yi kokarin jin ta bakin sakatariyar lafiya ta Karamar Hukumar Zariya, amma ba ta amsa kiran da wakilinmu ya yi mata ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka

Majiyar kafafen yada labarai na Amurka sun bayyana cewa akalla mutane 52 suka rasa rayukansu sanadiyyar ambaliyar ruwan sama a jihar Texas.

Jaridar US Today ta bayyana cewa an kubutar da daruruwan mutane daga halaka, amma kuma har yanzun ba san makamon daruruwan mutane ba. Sannan kungiyoyin bada agaji suna ci gaba da neman masu sauran shanruwa.

Ruwan sama kamar da bakin kwarya ne ya sauka a jiya Asabar ya kuma ciika kogin Guadalupe wanda yayi ambaliya ya kuma rufe garuruwa da dama da suke bakin kogin.

Gwamnatin Jihar Tezas Dan Patrick ya bayyana cewa an kubutar da mutane kimani 850 amma yawan matattu kuma yana karuwa a lokacinda jami’an agaji suke ci gaba da neman gawaki da kuma masu sauran numfashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Yobe
  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Gombe
  • Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida
  • Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC
  • Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutum 50 a Amurka
  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka
  • Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu