’Yan Banga Sun Ceto Mutum 3 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Taraba
Published: 19th, March 2025 GMT
“Sun zo da tsakar dare ɗauke da bindigogi, suka tafi da mu, suka ɗaure mu, tare da barazana cewa idan ba mu bi umarninsu ba za su kashe mu,” in ji shi.
Adamu, wanda yake fama da ciwo saboda dukan da aka yi masa, ya roƙi gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙoƙari wajen daƙile ayyukan ’yan bindiga.
Samamen da aka kai ya biyo bayan wani hari da aka kai garin Yelwa a ranar 15 ga watan Maris, inda aka kashe mutane biyu, aka kuma sace wasu uku.
Shugaban ayyuka na ‘yan bangar, Muniru Bello Abubakar, ya tabbatar da cewa ’yan bindiga na amfani da bayanan sirri daga mutanen cikin gari don samun bayani kan waɗanda za su sace da kuma hanyoyin kauce wa jami’an tsaro.
Ya gargaɗi masu taimaka wa ’yan bindiga da cewa za a ɗauke su a matsayin ’yan ta’adda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Banga Garkuwa Taraba Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF
Asusun kula da yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya bayyana cewa fiye da yara miliyan 400 a faɗin duniya na rayuwa cikin yanayin talauci mai tsanani.
A cikin sabon rahoton da ya fitar, UNICEF ya ce ƙarin ɗaruruwan miliyoyin yara na fuskantar hatsarin faɗawa talauci sakamakon katse tallafi, rikice-rikice, da kuma sauyin yanayi da ke gurgunta samun lafiya da walwala.
An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a JigawaRahoton ya nuna cewa yara miliyan 118 ba sa samun uku daga cikin muhimman buƙatun rayuwa guda biyar da suka haɗa da ilimi, lafiya, abinci mai gina jiki, ruwa da tsafta, da kuma muhallin da ya dace.
Haka kuma, yara miliyan 17 na rasa fiye da huɗu daga cikin waɗannan muhimman buƙatu na yau da kullum da suka zama wajibi a ce suna samu a rayuwarsu.
UNICEF ta bayyana cewa mafi yawan yaran da ke cikin mawuyacin hali na zaune ne a ƙasashen Kudu da Saharar Afrika da kuma Kudancin Asiya.
A ƙasar Chadi kadai, rahoton ya ce kashi 64% na yara ba sa samun aƙalla biyu daga cikin ababen da suka zama dole a rayuwar yaro.
Rahoton ya kuma nuna cewa matsalolin tsafta na ci gaba da addabar yara a duniya, inda kashi 65% na yaran ƙasashe masu ƙaramin ƙarfi ba su da damar yin amfani da makewayi mai inganci, sai kuma wasu kashi 26 a ƙasashe masu matsakaicin tattalin arziƙi, da kuma kashi 11 a manyan ƙasashe, lamarin dake barazana ga lafiyarsu.
UNICEF ta danganta wannan yanayi da yawan rikice-rikice, tasirin sauyin yanayi, basuka da su ka yi wa ƙasashe katutu, da kuma yawaitar jama’a, lamarin da gaba ɗaya ke ƙara dagula rayuwar yara a faɗin duniya.