’Yan Banga Sun Ceto Mutum 3 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Taraba
Published: 19th, March 2025 GMT
“Sun zo da tsakar dare ɗauke da bindigogi, suka tafi da mu, suka ɗaure mu, tare da barazana cewa idan ba mu bi umarninsu ba za su kashe mu,” in ji shi.
Adamu, wanda yake fama da ciwo saboda dukan da aka yi masa, ya roƙi gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙoƙari wajen daƙile ayyukan ’yan bindiga.
Samamen da aka kai ya biyo bayan wani hari da aka kai garin Yelwa a ranar 15 ga watan Maris, inda aka kashe mutane biyu, aka kuma sace wasu uku.
Shugaban ayyuka na ‘yan bangar, Muniru Bello Abubakar, ya tabbatar da cewa ’yan bindiga na amfani da bayanan sirri daga mutanen cikin gari don samun bayani kan waɗanda za su sace da kuma hanyoyin kauce wa jami’an tsaro.
Ya gargaɗi masu taimaka wa ’yan bindiga da cewa za a ɗauke su a matsayin ’yan ta’adda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Banga Garkuwa Taraba Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa, sun sace matarsa a Bauchi
Ana zargin wasu ’yan bindiga da kashe wani fitaccen ɗan kasuwa, Alhaji Muhammad Bakoshi, lokacin da suka kai hari garin Zalau da ke Ƙaramar Hukumar Toro a Jihar Bauchi.
Bayan kai hari, sun sace ɗaya daga cikin matansa, Hannatu Muhammad.
Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — TinubuWani mazaunin yankin, Shamsuddeen Hashimu Zalawa, ya shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar sun je gidan mutumin da tsakar dare.
Ya ce sun dinga harbe-harbe ba ƙaƙƙautawa, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin firgici.
Ya ƙara da cewa sun nufi gidan Bakoshi kai-tsaye, wanda hakan ya sa wasu ke zargin ko turo su aka yi.
Ɗan kasuwar mutum ne da ke taimakon jama’a musamman a sha’anin tsaro da kuma sabgogin maharba.
Haka kuma, ya kasance jami’in ladabtarwa a ƙungiyar First Aid ta JIBWIS a Zalau.
Zalawa, ya ce Bakoshi yana da mata biyu.
’Yan bindigar sun tafi da babbar matarsa, yayin da suka bar ƙaramar matarsa wacce ba ta jima da haihuwa ba.
Ƙoƙarin jin karin bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi, bai yi nasara ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.