’Yan Banga Sun Ceto Mutum 3 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Taraba
Published: 19th, March 2025 GMT
“Sun zo da tsakar dare ɗauke da bindigogi, suka tafi da mu, suka ɗaure mu, tare da barazana cewa idan ba mu bi umarninsu ba za su kashe mu,” in ji shi.
Adamu, wanda yake fama da ciwo saboda dukan da aka yi masa, ya roƙi gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙoƙari wajen daƙile ayyukan ’yan bindiga.
Samamen da aka kai ya biyo bayan wani hari da aka kai garin Yelwa a ranar 15 ga watan Maris, inda aka kashe mutane biyu, aka kuma sace wasu uku.
Shugaban ayyuka na ‘yan bangar, Muniru Bello Abubakar, ya tabbatar da cewa ’yan bindiga na amfani da bayanan sirri daga mutanen cikin gari don samun bayani kan waɗanda za su sace da kuma hanyoyin kauce wa jami’an tsaro.
Ya gargaɗi masu taimaka wa ’yan bindiga da cewa za a ɗauke su a matsayin ’yan ta’adda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Banga Garkuwa Taraba Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe
Gwamnatin Yobe ta bayyana cewa aƙalla mutane 9,854 ne ke ɗauke da cutar AIDS a jihar, kuma dukkaninsu na karɓar maganin ceton rai.
Hukumar ta tabbatar da cewa waɗannan marasa lafiya suna rayuwa cikin ƙoshin lafiya, tare da rage yiwuwar yaɗa cutar ga wasu.
Babban Daraktan Hukumar Kula da Cutar AIDS ta Jihar Yobe (YOSACA), Dakta Jibril Adamu Damazai, ne ya bayyana cewa Yobe na da mafi ƙarancin adadin masu ɗauke da cutar a ƙasar nan da kashi 0.4%, inda ya danganta hakan da dabarun yaƙi da cutar da ake aiwatarwa a jihar.
“Ba mu tsaya a kan wannan nasara ba, muna ƙara ƙoƙari don rage yawan kamuwa da cutar,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta kashe sama da Naira miliyan 120 wajen sayen kayan gwaji, abin da ya bai wa ƙungiyoyi damar gano mutanen da ba a san suna ɗauke da cutar ba a cikin al’umma, domin a ba su magani.
A cewarsa, Yobe na kan gaba wajen daidaita dabarun yaƙi da cutar AIDS, musamman ganin yadda ake samun sauye-sauye a kuɗaɗen da ake kashewa a duniya.
Dakta Damazai ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta fara shirye-shiryen samar da magungunan ƙwayar cutar HIV a cikin gida.
Ya yaba da jajircewar gwamna Mai Mala Buni, wanda ya ƙara kuɗaɗen da ake bai wa hukumar kula da cutar AIDS da kashi 400%, tare da samar da katafaren ofis na dindindin ga hukumar.