Leadership News Hausa:
2025-11-25@00:40:48 GMT

’Yan Banga Sun Ceto Mutum 3 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Taraba

Published: 19th, March 2025 GMT

’Yan Banga Sun Ceto Mutum 3 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Taraba

“Sun zo da tsakar dare ɗauke da bindigogi, suka tafi da mu, suka ɗaure mu, tare da barazana cewa idan ba mu bi umarninsu ba za su kashe mu,” in ji shi.

Adamu, wanda yake fama da ciwo saboda dukan da aka yi masa, ya roƙi gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙoƙari wajen daƙile ayyukan ’yan bindiga.

Samamen da aka kai ya biyo bayan wani hari da aka kai garin Yelwa a ranar 15 ga watan Maris, inda aka kashe mutane biyu, aka kuma sace wasu uku.

Shugaban ayyuka na ‘yan bangar, Muniru Bello Abubakar, ya tabbatar da cewa ’yan bindiga na amfani da bayanan sirri daga mutanen cikin gari don samun bayani kan waɗanda za su sace da kuma hanyoyin kauce wa jami’an tsaro.

Ya gargaɗi masu taimaka wa ’yan bindiga da cewa za a ɗauke su a matsayin ’yan ta’adda.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Banga Garkuwa Taraba Yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa, sun sace matarsa a Bauchi

Ana zargin wasu ’yan bindiga da kashe wani fitaccen ɗan kasuwa, Alhaji Muhammad Bakoshi, lokacin da suka kai hari garin Zalau da ke Ƙaramar Hukumar Toro a Jihar Bauchi.

Bayan kai hari, sun sace ɗaya daga cikin matansa, Hannatu Muhammad.

Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu

Wani mazaunin yankin, Shamsuddeen Hashimu Zalawa, ya shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar sun je gidan mutumin da tsakar dare.

Ya ce sun dinga harbe-harbe ba ƙaƙƙautawa, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin firgici.

Ya ƙara da cewa sun nufi gidan Bakoshi kai-tsaye, wanda hakan ya sa wasu ke zargin ko turo su aka yi.

Ɗan kasuwar mutum ne da ke taimakon jama’a musamman a sha’anin tsaro da kuma sabgogin maharba.

Haka kuma, ya kasance jami’in ladabtarwa a ƙungiyar First Aid ta JIBWIS a Zalau.

Zalawa, ya ce Bakoshi yana da mata biyu.

’Yan bindigar sun tafi da babbar matarsa, yayin da suka bar ƙaramar matarsa wacce ba ta jima da haihuwa ba.

Ƙoƙarin jin karin bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi, bai yi nasara ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Yara 50 Da Aka Sace A Najeriya Sun Tsere Daga Hannun Barayin Daji
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan kasuwa, sun sace matarsa a Bauchi
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • Najeriya : An sako mutum 38 da ‘yan bindiga suka sace a jihar Kwara_Tinubu
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 
  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba
  • ’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara