’Yan Banga Sun Ceto Mutum 3 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Taraba
Published: 19th, March 2025 GMT
“Sun zo da tsakar dare ɗauke da bindigogi, suka tafi da mu, suka ɗaure mu, tare da barazana cewa idan ba mu bi umarninsu ba za su kashe mu,” in ji shi.
Adamu, wanda yake fama da ciwo saboda dukan da aka yi masa, ya roƙi gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙoƙari wajen daƙile ayyukan ’yan bindiga.
Samamen da aka kai ya biyo bayan wani hari da aka kai garin Yelwa a ranar 15 ga watan Maris, inda aka kashe mutane biyu, aka kuma sace wasu uku.
Shugaban ayyuka na ‘yan bangar, Muniru Bello Abubakar, ya tabbatar da cewa ’yan bindiga na amfani da bayanan sirri daga mutanen cikin gari don samun bayani kan waɗanda za su sace da kuma hanyoyin kauce wa jami’an tsaro.
Ya gargaɗi masu taimaka wa ’yan bindiga da cewa za a ɗauke su a matsayin ’yan ta’adda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan Banga Garkuwa Taraba Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
Daga Ali Muhammad Rabi’u
’Yan bindiga kimanin guda huɗu dauke da makamai sun kai hari a garin Eruku da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara, inda suka sace wani manomi mai suna Mista Aasaru.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa wannan hari shi ne na biyu da aka kai wa garin Eruku cikin wata guda, kuma ya faru ne kwanaki kaɗan bayan gwamnatin tarayya ta samu ’yantar da mambobin Cocin Christ Apostolic Church (CAC) 38 da aka yi garkuwa da su a yankin.
Majiyar da ta yi magana da Rediyon Najeriya ta ce ’yan bindigar sun farmaki Aasaru ne a wani daji da ke kan hanyar Koro.
Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sandan jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin.
A cewarta, jami’an ’yan sanda daga sashin Eruku sun karɓi korafi a ranar Lahadi cewa wasu mutane huɗu dauke da makamai sun kutsa wata gona a kan hanyar Koro, Eruku, inda suka sace wani Mista Aasanru mai shekaru 40.
Ejire-Adeyemi ta ce ana cigaba da ƙokari wajen ganin an kubutar da manomin da aka sace.