Wata Kungiya Mai Zaman Kanta Ta Samar Da Rijiyoyin Burtsatse A Karamar Hukumar Ringim
Published: 19th, March 2025 GMT
Wata Kungiyar Agaji Mai Zaman Kanta, Ike Odoeme Foundation, ta taimaka wa yankuna biyu a karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa, ta hanyar haka rijiyoyin burtsatse guda bibbiyu a kowane yanki.
A yayin kaddamar da ayyukan a kauyukan Facawa da Riniyal da ke Ringim, jami’ar shirye-shirye ta gidauniyar, Miss Suzie Agas, ta bayyana jin dadinsu na yin tasiri a rayuwar al’ummar yankin.
A cewarta, wannan aikin yana tabbatar da kudirin gidauniyar na tabbatar da cewa kowace al’umma tana da damar samun tsaftataccen ruwa, ba tare da la’akari da matsayinta ko inda take ba.
Suzie Agas ta jaddada cewa ruwa yana da matukar muhimmanci ga kiwon lafiya da ci gaban tattalin arziki, amma abin takaici, al’ummomi da dama na fuskantar kalubale wajen samun tsaftataccen ruwa.
Ta kara da cewa rashin ruwa mai tsafta yana haddasa cututtukan da ake dauka ta ruwa, yana hana mutane yin ayyuka da kyau, kuma yana rage damarmakin yaran makaranta don mayar da hankali kan karatunsu.
Suzie ta gode wa hukumomin karamar hukumar Ringim bisa goyon baya da hadin kai da suka bayar wajen tabbatar da tsaro da aminci a lokacin aikin.
Ta kuma roki al’ummomin Facawa da Riniyal da su kula da rijiyoyin, don gujewa samun matsala.
A nasa jawabin yayin kaddamar da rijiyoyin, hakimin Sankara, Alhaji Yusi Ahmed, ya tabbatar da cewa wadannan al’ummomi sun shafe shekaru da dama suna fama da karancin ruwa.
Ya ce ko da yake an taba samar da rijiyoyi a wadannan yankuna, rashin kulawa da su ya sa suka lalace.
Ya bukaci mazauna yankin da su dauki nauyin kula da rijiyoyin domin su dade suna amfani da su fiye da wadanda aka samar a baya.
Shi ma da yake nasa jawabi, Shugaban Karamar Hukumar Ringim, Alhaji Badamasi Dabi, ya jinjinawa gidauniyar bisa jajircewarta wajen tabbatar da kammala aikin.
Ya bayyana cewa karamar hukumar Ringim tana da cikakken shirin yin hadin gwiwa da kungiyoyin agaji domin ci gaban al’umma.
Bayan haka, gidauniyar ta rabawa al’ummar buhunan shinkafa.
Wasu daga cikin mazauna yankin sun bayyana godiyarsu bisa wannan aikin, inda suka ce hakan ya rage wahalar da ‘ya’yansu ke fuskanta wajen yin doguwar tafiya domin samo ruwa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
A ƙoƙarinta na ƙara wayar da kan jama’a game da harkokin lafiya a birane da karkara na Malam Madori, majalisar ƙaramar hukumar ta horar da mata da ‘yan mata 50 kan tsafta a lokutan al’ada domin kare kansu daga cututtukan mahaifa.
Jami’in shirin, Malam Ali Haruna, ya ce an zaɓi mahalarta horon ne daga kowace gunduma ta yankin
A cewarsa, manufar horon ita ce koyar da mahalarta yadda za su samar da kariya yayin al’ada da kansu domin rage kashe kuɗi da kuma kare kansu daga kamuwa da cututtukan mahaifa.
Shi ma shugaban sashen ruwa da tsafta, Malam Shehu Sani Gwadayi, ya bayyana cewa tsafta na da matuƙar muhimmanci ga rayuwar ɗan adam domin inganta rayuwa da ƙarfafa garkuwar jiki.
A nasa jawabin, mataimakin shugaban sashen ruwa da tsafta, Malam Muhammad Abdullahi, ya yi wa mahalarta horon bayani kan muhimmancin tsafta yayin al’ada domin gujewa kamuwa da cututtuka.
Shugaban ƙaramar hukumar Malam Madori, Alhaji Salisu Sani Garun Gabas, ya shawarci mahalarta da su mai da hankali ga sashen aikace-aikace na yadda ake sarrafa audugar mata a gida yayin horon.
Usman Muhammad Zaria