Wata Kungiyar Agaji Mai Zaman Kanta, Ike Odoeme Foundation, ta taimaka wa yankuna biyu a karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa, ta hanyar haka rijiyoyin burtsatse guda bibbiyu a kowane yanki.

A yayin kaddamar da ayyukan a kauyukan Facawa da Riniyal da ke  Ringim, jami’ar shirye-shirye ta gidauniyar, Miss Suzie Agas, ta bayyana jin dadinsu na yin tasiri a rayuwar al’ummar yankin.

 

A cewarta, wannan aikin yana tabbatar da kudirin gidauniyar na tabbatar da cewa kowace al’umma tana da damar samun tsaftataccen ruwa, ba tare da la’akari da matsayinta ko inda take ba.

Suzie Agas ta jaddada cewa ruwa yana da matukar muhimmanci ga kiwon lafiya da ci gaban tattalin arziki, amma abin takaici, al’ummomi da dama na fuskantar kalubale wajen samun tsaftataccen ruwa.

Ta kara da cewa rashin ruwa mai tsafta yana haddasa cututtukan da ake dauka ta ruwa, yana hana mutane yin ayyuka da kyau, kuma yana rage damarmakin yaran makaranta don mayar da hankali kan karatunsu.

Suzie ta gode wa hukumomin karamar hukumar Ringim bisa goyon baya da hadin kai da suka bayar wajen tabbatar da tsaro da aminci a lokacin aikin.

Ta kuma roki al’ummomin Facawa da Riniyal da su kula da rijiyoyin, don gujewa samun matsala.

A nasa jawabin yayin kaddamar da rijiyoyin, hakimin Sankara, Alhaji Yusi Ahmed, ya tabbatar da cewa wadannan al’ummomi sun shafe shekaru da dama suna fama da karancin ruwa.

Ya ce ko da yake an taba samar da rijiyoyi a wadannan yankuna, rashin kulawa da su ya sa suka lalace.

Ya bukaci mazauna yankin da su dauki nauyin kula da rijiyoyin domin su dade suna amfani da su fiye da wadanda aka samar a baya.

Shi ma da yake nasa jawabi, Shugaban Karamar Hukumar Ringim, Alhaji Badamasi Dabi, ya jinjinawa gidauniyar bisa jajircewarta wajen tabbatar da kammala aikin.

Ya bayyana cewa karamar hukumar Ringim tana da cikakken shirin yin hadin gwiwa da kungiyoyin agaji domin ci gaban al’umma.

Bayan haka, gidauniyar ta rabawa al’ummar buhunan shinkafa.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun bayyana godiyarsu bisa wannan aikin, inda suka ce hakan ya rage wahalar da ‘ya’yansu ke fuskanta wajen yin doguwar tafiya domin samo ruwa.

 

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025

Hukumar Jin Daɗin Alhazai a Jihar Kebbi ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana a Ƙasa Mai Tsarki.

Amirul Hajji na jihar na shekarar 2025 kuma Sarkin Argungu, Alhaji Samaila Muhammad Mera, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a lokacin taron farko da aka gudanar a hedkwatar hukumar da ke Birnin Kebbi.

Ya kuma yi alkawarin tabbatar da jin daɗin mahajjatan jihar yayin da suke a ƙasa mai tsarki.

Amirul Hajjin ya bayyana cewa jimillar mahajjata 3,800 daga jihar ne suka biya kuɗin kujerunsu gaba ɗaya domin aikin hajjin bana, kuma jigilar mahajjatan za ta fara ne ranar 9 ga watan Mayu, inda ya ce da yardar Allah za a ci gaba da jigilar ba tare wani tsaiko ba har sai an kammala.

Ya kuma bayyana cewa, a wannan shekarar, za a yi wa mahajjata canjin kuɗin guzirinsu na BTA zuwa kudin Saudiyya wato riyal  kai tsaye, da nufin dakile ayyukan damfara da kuma kare mahajjata daga asarar kuɗi yayin musayar kuɗaɗe a nan gida da kuma Saudiyya.

Alhaji Muhammadu Mera ya shawarci mambobin tawagar gwamnati da jami’an hukumar jin daɗin mahajjata da su gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah, tare da kare haƙƙoƙin mahajjata, daidai da manufar Gwamna Nasir Idris na gudanar da sahihin aikin Hajji mafi kyau.

Shugaban Hukumar, Alhaji Faruk Musa Yaro, ya yi alkawarin bayar da cikakken haɗin kakaga tawagar gwamnati domin tabbatar da nasarar aikin Hajji da ba a taɓa irin sa ba a tarihin jihar.

Ya ce an riga an samu masauki da sauran abubuwan buƙata ciki har da sufuri da abinci a ƙasa mai tsarki, sannan kuma kamfanin jirgin samsada ya yi jigilar Alhazan jihar a shekarar da ta gabata,  wato Flynas, a bana ma shi ne zau yi jigilar mahajjatan zuwa kasa mai tsarki.

Haka kuma, an an fara yi wa Amirul Hajj da sauran mambobin tawagar gwamnati allurar rigakafi  yayin kaddamar da shirin rigakafin mahajjatan.

 

Daga Abdullahi Tukur

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA