(ENT) Aikin Hanci , Makogaro da Kunne

(Dental) Hakori

(Fibroid) Qarin mahaifa,

(Urology) Aikin Mafitsara

Asibitin ya zakulo zakakuran likitoci domin gudanar da wannan ayyukan daga yau Litinin 8, ga watan Yuli 2025, ga duk masu bukatar wannan ayyukan, akan farashin kaso 50% cikin 100 shima za a biya.

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu  Asibitin Aminu Kano Ya Musanta Cire Mahaifar Mara Lafiya Ba Tare Da Izini Ba

Hakan na kunshe ne cikin wata sanar da shugaban asibitin Alh Auwal Muhd Lawal ya bayyanawa jaridar Alfijir Labarai a safiyar Litinin.

Lawal yace sun yanke wannan hukuncin ne sakamakon buƙatar da al’umma suke da ita a wannan bangarorin ga kuma yawan da mutane suka yiwa gwamnati shi yasa hukumar gudanarwar Asibitin Kwararru na Best Choice itama taga da cewar bada tata gudummawar domin kara karfafar gwamnati a wannan fannin.

Auwal ya kuma bayyana jin dadinsa ganin yadda al’umma suke ta cin gajiyar bude fiyil kyauta da rage kaso 50% ganin likita tare da manya da kananan ayyukan asibitin da yayi a satin da ya gabata.

Dukkannin waɗannan ayyuka za a fara gudanar da sune a yau Litinin, don haka ga masu irin wadannan matsaloli za su iya zuwa domin a tantancesu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Tiyata

এছাড়াও পড়ুন:

Malamin Addinin Musulunci Yayi Kira Da Ayi Gaggawa Gyaran Hanyar Zamfara

Wani malamin addinin musulunci a jihar Zamfara, Sheikh Mohammed Tukur Sani Jangebe, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar Zamfara da su gaggauta gudanar da kananan gyare-gyare daga mahadar Maru –Mayanchi – Maradun, da ke kan hanyar zuwa wani yanki na karamar hukumar Talata Mafara.

 

Ya ce mummunan yanayin hanyar yana ci gaba da haifar da babban kalubale ga matafiya tare da fallasa su ga hare-haren ‘yan bindiga a kan hanyar.

 

Sheikh Jangebe ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake zantawa da wakilin gidan rediyon Najeriya a Gusau babban birnin jihar Zamfara.

 

Ya bayyana cewa babbar hanyar Maru zuwa Talata Mafara ta samar da ramuka sama da dari, wadanda ke hana zirga-zirgar ababen hawa.

 

A cewarsa, hanyar ta zama hanya mai hatsarin gaske saboda yawaitar ‘yan fashi da garkuwa da mutane.

 

Malamin ya bayyana cewa, duk da cewa gwamnatin tarayya ta bayar da kwangilar tagwayen hanya na titin Zaria zuwa Funtua zuwa Gusau zuwaTalata Mafara zuwa Sokoto amma har yanzu aikin bai kai ga tsallaka babbar hanyar Maru zuwa Talata Mafara ba.

 

Sheikh Tukur Jangebe ya bayyana cewa, dubban matafiya sun dogara ne da hanyoyin sufuri, kasuwanci, kiwon lafiya, noma, ko sauran muhimman ayyuka yayin da hanyar ita ce babbar hanyar da ta tashi daga Zamfara zuwa Sokoto har zuwa jihar Kebbi.

 

“Abin takaici, hanyar da ta tashi daga Bungudu ta bi ta Maru, Mayanchi, mahadar Maradun, har zuwa wani yanki na Talata Mafara, gaba daya ta lalace.

 

Sheikh Jangebe ya jadadda cewa, rashin kyawun hanyar yana haifar da fasa-kwaurin manyan motoci a lokuta da dama da kuma kara yawan yin garkuwa da mutane, domin masu aikata laifuka suna amfani da jinkirin da aka samu wajen yi wa matafiya kwanton bauna.

 

A cewarsa, direbobin ‘yan kasuwa da sauran masu ababen hawa na iya shaida rashin kyawun hanyar.

 

“Ina so in yi amfani da wannan damar in yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta hannun Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya da ta gaggauta gudanar da kananan gyare-gyaren gaggawa a kan hanyar domin saukaka radadin mutanen da ke tafiya a cikinta a kullum.”

 

Sheik Tukur Sani Jangebe ya kuma ce shigowar damina ta bana ya kara ta’azzara yanayin hanyar, tare da samar da karin ramuka da kuma sanya tafiye-tafiyen da ke da hadari.

 

Malamin ya kuma yi kira ga Gwamnonin jihohin Kaduna, Zamfara, Katsina, da Sokoto da su hada kai tare da gyara duk wani bangare na babbar hanyar da ke bukatar kulawa cikin gaggawa, har sai an kai ga aikin da ake yi a bangaren domin sake gina shi na karshe.

 

Ya bukaci ma’aikatar ayyuka ta tarayya da ’yan kwangilar da ke tafiyar da aikin hanyar da su hanzarta gudanar da aikin domin ganin an kammala shi a kan lokaci.

 

AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
  • Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano
  • Malamin Addinin Musulunci Yayi Kira Da Ayi Gaggawa Gyaran Hanyar Zamfara
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba
  • An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci