Amurka ce Kadai Ta Ki Yin Allawadai Da Killace Gaza A Tsakanin Mambobin Kwamitin Tsaro na MDD
Published: 19th, March 2025 GMT
MAfi yawancin mambobin kwamitin tsaron sun yi tir da harin da sojojin HKI su ka kai wa mutanen Gaza a cikin daren shekaran jiya wanda ya yi sanadiyyar shahadar fiye da Falasdinawa 400.
Wakilin kasar Rasha a MDD ya bayyana cewa; Sake bude yaki a Gaza, yana nufin korar Falasdinawa daga kasarsu” ya kuma jaddada cewa; “ Wajibi ne ga kwamitin tsaro ya yi duk abinda zai iya yi, domin sake tsayar da wutar yaki, bai kuma kamata a ce an sake maimaita kurakuren baya ba.
Shi kuwa wakilin kasar Aljeriya a MDD, ya bayyana ya zargi HKI da amfani da yunwa a matsayin makamin yaki, yana mai jaddada cewa; Wannan lokaci ne da hukunta masu laifi, domin babu wanda ya fi karfin doka.” Haka nan kuma ya ce; Yanzu duniya ta daina kawar da kanta daga laifukan da ‘yan mamaya suke yi.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza
Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa 24 daga cikin dare zuwa wayewar garin ranar Alhamis a Zirin Gaza.
Majiyoyi a yankin sun shaida wa gidan talabijin na Al-Jazeera cewa akasarin mutum 24 din da aka kashe a zirin na Gaza mata ne da kananan yara.
NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss MustaphaAkasarin mutanen dai an kashe su ne a tsakiya da kudancin zirin na Gaza.
Ma’aikatan lafiya a asibitin Al-Aqsa da ke Gaza sun ce a yankin Deir el-Balah kawai akwai Falasdinawa 13 da aka kashe sannan an jikkata wasu da dama.
Gabanin nan ma, Isra’ila ta kashe mutum hudu a harin da ta kai sansanin ’yan gudun hijira na Bureij, shi ma wanda ke tsakiyar Gaza.
Sama da mutum 700 ne Isra’ila ta kashe Falasdinawa 700 da ke kokarin karbar tallafi a wuraren karbar tallafi na Gidauniyar GHF wanda Amurka da Isra’ilar suke goya wa baya tun lokacin da aka kaddamar da shi a watan Mayu.
Daga cikin mutanen dai akwai yara kanana da dama, ciki har da wani jariri dan kwana 10 da haihuwa.