MAfi yawancin mambobin kwamitin tsaron sun yi tir da harin da sojojin HKI su ka kai wa mutanen Gaza a cikin daren shekaran jiya wanda ya yi sanadiyyar shahadar fiye da Falasdinawa 400.

 Wakilin kasar Rasha a MDD  ya bayyana cewa; Sake bude yaki a Gaza, yana nufin korar Falasdinawa daga kasarsu” ya kuma jaddada cewa; “  Wajibi ne ga kwamitin tsaro ya yi duk abinda zai iya yi, domin sake tsayar da wutar yaki, bai kuma kamata a ce an sake maimaita kurakuren baya ba.

Shi kuwa wakilin kasar Aljeriya a MDD, ya bayyana ya zargi HKI da amfani da yunwa a matsayin makamin yaki, yana mai jaddada cewa; Wannan lokaci ne da hukunta masu laifi, domin babu wanda ya fi karfin doka.” Haka nan kuma ya ce;  Yanzu duniya  ta daina kawar da kanta daga laifukan da ‘yan mamaya suke yi.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

ISWAP: Mun kawar da duk wata barazana — Gwamnatin Ondo

Gwamnatin Jihar Ondo ta roƙi jama’a da su kwantar da hankalinsu bayan gargaɗin da Hukumar Tsaro ta DSS, ta yi na cewar wasu mayaƙan ISWAP na shirin kai hari wasu sassan jihar.

A cikin wata sanarwa, Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Mista Idowu Ajanaku, ya bayyana cewa irin waɗannan rahotanni abu ne na yau da kullum a harkokin tsaro.

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Haraji Da Zai Fara Aiki A 2026 Idan Tinubu ya gaza zai yi wuya a samu shugaban da zai yi nasara — Shehu Sani

Ya ce hukumomin tsaro suna yawan musayar bayanai irin waɗannan domin daƙile duk wata barazana.

Ajanaku, ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnati tare da hukumomin tsaro sun ɗauki matakai don kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.

“Gwamnati da hukumomin tsaro suna kan lamarin kuma suna ɗaukar duk matakan da suka dace don tabbatar da cewa Jihar Ondo ta kasance cikin aminci,” in ji sanarwar.

Ya kuma roƙi mazauna jihar da su kwantar da hankalinsu, su ci gaba da ayyukansu na yau da kullum, sannan su riƙa sanar da hukumomin tsaro idan suka ga wani abun zargi.

Kwamishinan ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta mayar da hankali sosai kan yankunan da ke iyakar wasu jihohi don kawar da kowace irin barazana.

“Don Allah kada ku firgita, kada kuma ku ɗauki doka a hannunku. Ku haɗa kai da gwamnati da hukumomin tsaro domin mu ci gaba da tabbatar da tsaron jiharmu,” in ji Ajanaku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sauke Hafsoshin Tsaro: Za a yi wa Janar-Janar 60 ritaya daga aiki
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Kiran Da A Nisanci Siyasantar Da Kwamitin Tsaron Majalisar
  • Shugaban Kasar Venezuela Ya Ce; Amurka Tana Son Kaddamar Da Yaki Kan Kasarsa
  • Bangarorin Falasdinawa Sun Amince Da Shirin Gudanar Da Zirin Gaza Nan Gaba
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
  • Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 
  • Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta
  • Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka
  • An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15
  • ISWAP: Mun kawar da duk wata barazana — Gwamnatin Ondo