Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba
Published: 19th, March 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya umarci ɗaukacin Masarautun Kano guda huɗu da su fara shirye-shiryen Hawan Sallah da bisa al’ada aka saba domin ganin jama’a da maziyarta sun nishaɗantu a yayin bukukuwan Sallah na bana.
Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne a yayin wani taron buɗa-baki da sarakunan gargajiya da aka yi a ɗakin taro na Ante Chamber da ke gidan gwamnatin Kano a ranar Talata.
Abba ya jaddada cewa al’ummar jihar sun ƙagara don ganin wannan al’ada ta sanya sabbin tufafi a lokacin bukukuwan Sallah, tare da tsayawa a kan tituna domin kallon sarakunansu a kan doki suna musayar gaisuwa.
“Al’ummar Kano babu abin da suke a duniya, illa bayan azumin watan Ramadan, su caɓa ado, su fito su yi dandazo a bakin titi, sarkinsu ya fito, hakimai su fito a kan dawakai, su yi jinjina su yi godiya, sannan sarki ya yi musu addu’a.”
Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba, kuma ba za ta bari wasu maƙiya su tauye wa al’ummar wannan haƙƙin da suke matuƙar mutuntawa ba.
Kazalika, ya tabbatar da cewa dukkanin hukumomin tsaro a jihar za su ba da himma wajen bai wa jama’a kariya a yayin bukukuwan.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa za a ƙaddamar da Majalisar Masarautar Jihar Kano a watan Afrilun bana domin samun damar gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.
Ya bayyana cewa za a sanar da ka’idoji, tsare-tsare da sauran muhimman abubuwan da suka danganci majalisar a ranar ƙaddamarwa.
Ya yaba wa sarakunan bisa kyakkyawar alaƙar da suka nuna tun bayan naɗa su, inda ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihin jihar da ake samun mutuntawa a tsakanin sarakunan musamman ta fuskar matsayi.
A nasa jawabin, Shugaban Majalisar Masarautar Kano kuma Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi II, ya tabbatar da cewa alaƙar da ke tsakaninsa da sarakunan ta musamman ce.
Ya yi kira ga Gwamnan da ya yi amfani da masarautun gargajiya wajen yaɗa manufofi da tsare-tsare ga al’umma, tare da tabbatar da aiwatar da ayyuka cikin inganci.
A nasu ɓangaren, Sarkin Karaye, Muhammad Muhammad Maharaz; Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru; da mai martaba Sarkin Gaya Dokta Aliyu Ibrahim Abdulkadir duk a madadin jama’arsu, sun yaba wa Gwamnan kan samar da takin zamani da sauran ababen more rayuwa a fannonin ilimi, lafiya da tituna a yankunansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hawan Sallah Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Limamin Tehran: Duniya Ce Ta Yi Yaki Da Iran
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a Tehran ya bayyana cewa; A cikin kwanaki 12 da su ka gabata duniya ce ta yi yaki da Iran.
Hujjatul Islam Wal Muslimin Abu Turabi Fard, ya fara hudubarsa da mika sakon ta’aziyyar shigowar ranakun Ashura, haka nan kuma jinjina ga shahidan jamhuriyar musulunci masu daraja da HKI ta yi wa kisan ta’addanci a tsawon kwanaki12 na yaki.
Limamin na Tehran ya kuma ce; Abubuwan da su ka faru a cikin kwanaki 12 na yaki sun bude wani sabon shafi na siyasa a cikin wannan yankin da kuma a fagen siyasar kasa da kasa.
Hari la yau limamin na Tehran ya jinjinawa jagoran juyin musulunci na Iran saboda yadda Iran a karkashin jagorancinsa ta zama cibiyar gwgawarmayar musulunci a cikin wannan yankin.
Limamin juma’ar na Tehran ya kuma kara da cewa; HKI ta kawo wa Iran hari ne a jajiberin ranar Idan Gadir bisa cikakken taimakon bayanai na asiri daga Amurka.”
Limamin ya kuma kara da cewa; Masu bin diddigin abubuwan da suke faruwa suna bayyana cewa; Makiya, sun dauki shekaru kusan 20 suna shirya wannan yakin. Shi kanshi fira ministan HKI ya yi furuci da hakan.
Hujjatul Islami Wal Muslimin Abu Turabi Fard ya kuma ce; HKI ta kawo wannan harin ne adaidai lokacin da ake tattaunawa.