Aminiya:
2025-08-15@11:45:59 GMT

Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba

Published: 19th, March 2025 GMT

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya umarci ɗaukacin Masarautun Kano guda huɗu da su fara shirye-shiryen Hawan Sallah da bisa al’ada aka saba domin ganin jama’a da maziyarta sun nishaɗantu a yayin bukukuwan Sallah na bana.

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne a yayin wani taron buɗa-baki da sarakunan gargajiya da aka yi a ɗakin taro na Ante Chamber da ke gidan gwamnatin Kano a ranar Talata.

Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano

Abba ya jaddada cewa al’ummar jihar sun ƙagara don ganin wannan al’ada ta sanya sabbin tufafi a lokacin bukukuwan Sallah, tare da tsayawa a kan tituna domin kallon sarakunansu a kan doki suna musayar gaisuwa.

“Al’ummar Kano babu abin da suke a duniya, illa bayan azumin watan Ramadan, su caɓa ado, su fito su yi dandazo a bakin titi, sarkinsu ya fito, hakimai su fito a kan dawakai, su yi jinjina su yi godiya, sannan sarki ya yi musu addu’a.”

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba, kuma ba za ta bari wasu maƙiya su tauye wa al’ummar wannan haƙƙin da suke matuƙar mutuntawa ba.

Kazalika, ya tabbatar da cewa dukkanin hukumomin tsaro a jihar za su ba da himma wajen bai wa jama’a kariya a yayin bukukuwan.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa za a ƙaddamar da Majalisar Masarautar Jihar Kano a watan Afrilun bana domin samun damar gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

Ya bayyana cewa za a sanar da ka’idoji, tsare-tsare da sauran muhimman abubuwan da suka danganci majalisar a ranar ƙaddamarwa.

Ya yaba wa sarakunan bisa kyakkyawar alaƙar da suka nuna tun bayan naɗa su, inda ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihin jihar da ake samun mutuntawa a tsakanin sarakunan musamman ta fuskar matsayi.

A nasa jawabin, Shugaban Majalisar Masarautar Kano kuma Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi II, ya tabbatar da cewa alaƙar da ke tsakaninsa da sarakunan ta musamman ce.

Ya yi kira ga Gwamnan da ya yi amfani da masarautun gargajiya wajen yaɗa manufofi da tsare-tsare ga al’umma, tare da tabbatar da aiwatar da ayyuka cikin inganci.

A nasu ɓangaren, Sarkin Karaye, Muhammad Muhammad Maharaz; Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru; da mai martaba Sarkin Gaya Dokta Aliyu Ibrahim Abdulkadir duk a madadin jama’arsu, sun yaba wa Gwamnan kan samar da takin zamani da sauran ababen more rayuwa a fannonin ilimi, lafiya da tituna a yankunansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Sallah Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Liberia Don Inganta Noman Shinkafa

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya karbi bakuncin Mataimakin Ministan Noma na Jamhuriyar Liberia, David Akoi, a wata ziyara ta musamman domin nazarin dabarun noman shinkafa a jihar, wadda ita ce kan gaba a fitar da shinkafa a Najeriya.

A yayin ziyarar ban girma a fadar gwamnati da ke Dutse, Mista Akoi ya ce wannan ziyara za ta ba tawagarsa damar fahimtar dabarun noma da sarrafa shinkafa, samun horo a aikace, tare da koyo game da dukkan sassan harkar noman shinkafa. Ya bayyana cewa, wannan zai taimaka wa Liberia rage dogaro da shinkafar da ake shigowa da ita daga waje.

“A Liberia muna cin shinkafa safe, rana da dare. A shekarar 1979, an yi tarzomar shinkafa da ta kifar da gwamnatin Shugaba William R. Tolbert bayan yunkurin kara farashin shinkafa,” in ji shi. “Yanzu haka muna shigowa da kimanin kashi 70 cikin dari na shinkafar da muke ci.”

Ya ce gwamnatin Liberia ta kuduri aniyar samar da aƙalla kashi 70 cikin dari na bukatar shinkafar cikin gida. Ya bayyana cewa Shugaba Joseph Boakai ya zabi Najeriya, musamman Jihar Jigawa, saboda irin ci gaban da ta samu a harkar noman shinkafa.

“Mun zo ne domin koyo daga Jigawa yadda ta samu wannan nasara, da dabarun da ta yi amfani da su wajen shawo kan matsalolin noma.” In ji shi. “Manufarmu ita ce mu aiwatar da irin wannan nasara a kasarmu.”

Da yake mayar da martani, Gwamna Namadi ya yaba wa Liberia bisa zaben Jigawa, yana mai cewa wannan hadin gwiwa zai bai wa bangarorin biyu damar musayar dabaru da gogewa da za su amfani bangarorin noman su. Ya jaddada cewa noma ita ce ginshikin tattalin arzikin Jigawa.

“A shekarar 2023, Jigawa na noman kadada 60,000 zuwa 70,000 na shinkafa. Amma a 2024, mun kai sama da kadada 200,000, kuma bana muna fatan kaiwa kadada 300,000. Burinmu shi ne mu samar da kashi 50 cikin dari na shinkafar da Najeriya ke bukata nan da 2030,” in ji shi.

Gwamnan ya bayyana cewa jihar na mai da hankali kan noman rani domin rage illar sauyin yanayi. “Muna gyara madatsun ruwa 10 da ke jihar, wanda hakan ke kara fiye da kadada 4,500 ga filayen noma,” In ji shi.

Don kara yawan amfanin gona, gwamnatin jihar ta samar da sababbin taraktoci 300 da  kayayyakin aikin su, injinan girbi 60, injinan shuka 150, da sauran kayan noma na zamani. Kowacce cikin mazabu 30 a jihar tana da akalla taraktoci 10 da ake ba manoma kananan haya a farashi rahusa rahusa.

Gwamna Namadi ya tabbatar da cewa Jigawa za ta ci gaba da zuba jari a harkokin noma na zamani don karfafa sashen shinkafa, tare da bai wa Liberia goyon baya a yunkurinta na cimma wadatar shinkafa a cikin gida.

 

Usman Muhammad Zaria 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • An naɗa sabon Sarkin Alkaleri a Bauchi
  • Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana
  • Jihar Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Liberia Don Inganta Noman Shinkafa
  • Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba
  • Kano Na Karbar Bakuncin Babban Taron Kungiyar NUJ Na Kasa
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello
  • Lafiyar Tinubu kalau – Soludo
  • PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi