Aminiya:
2025-11-05@12:52:47 GMT

Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba

Published: 19th, March 2025 GMT

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya umarci ɗaukacin Masarautun Kano guda huɗu da su fara shirye-shiryen Hawan Sallah da bisa al’ada aka saba domin ganin jama’a da maziyarta sun nishaɗantu a yayin bukukuwan Sallah na bana.

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne a yayin wani taron buɗa-baki da sarakunan gargajiya da aka yi a ɗakin taro na Ante Chamber da ke gidan gwamnatin Kano a ranar Talata.

Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano

Abba ya jaddada cewa al’ummar jihar sun ƙagara don ganin wannan al’ada ta sanya sabbin tufafi a lokacin bukukuwan Sallah, tare da tsayawa a kan tituna domin kallon sarakunansu a kan doki suna musayar gaisuwa.

“Al’ummar Kano babu abin da suke a duniya, illa bayan azumin watan Ramadan, su caɓa ado, su fito su yi dandazo a bakin titi, sarkinsu ya fito, hakimai su fito a kan dawakai, su yi jinjina su yi godiya, sannan sarki ya yi musu addu’a.”

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba, kuma ba za ta bari wasu maƙiya su tauye wa al’ummar wannan haƙƙin da suke matuƙar mutuntawa ba.

Kazalika, ya tabbatar da cewa dukkanin hukumomin tsaro a jihar za su ba da himma wajen bai wa jama’a kariya a yayin bukukuwan.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa za a ƙaddamar da Majalisar Masarautar Jihar Kano a watan Afrilun bana domin samun damar gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

Ya bayyana cewa za a sanar da ka’idoji, tsare-tsare da sauran muhimman abubuwan da suka danganci majalisar a ranar ƙaddamarwa.

Ya yaba wa sarakunan bisa kyakkyawar alaƙar da suka nuna tun bayan naɗa su, inda ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihin jihar da ake samun mutuntawa a tsakanin sarakunan musamman ta fuskar matsayi.

A nasa jawabin, Shugaban Majalisar Masarautar Kano kuma Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi II, ya tabbatar da cewa alaƙar da ke tsakaninsa da sarakunan ta musamman ce.

Ya yi kira ga Gwamnan da ya yi amfani da masarautun gargajiya wajen yaɗa manufofi da tsare-tsare ga al’umma, tare da tabbatar da aiwatar da ayyuka cikin inganci.

A nasu ɓangaren, Sarkin Karaye, Muhammad Muhammad Maharaz; Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru; da mai martaba Sarkin Gaya Dokta Aliyu Ibrahim Abdulkadir duk a madadin jama’arsu, sun yaba wa Gwamnan kan samar da takin zamani da sauran ababen more rayuwa a fannonin ilimi, lafiya da tituna a yankunansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Sallah Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gina Gadar Sama Da Ta Kasa A Mararraba

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta ce ta samu amincewar gwamnatin tarayya domin gina sabbin gada biyu na sama da kuma ta karkashin kasa (under-pass) a yankin Mararaba da ke Karamar Hukumar Karu.

Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna Abdullahi Sule kan Harkokin Jama’a, Mr. Peter Ahemba, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

A cewar Ahemba, gwamnati za ta fara aikin kafin gwamnatin yanzu ta kai ga karewar wa’adinta a shekara ta 2027. Ya ce tun da dadewa Gwamna Abdullahi Sule ya ware kudaden aikin, kafin ma a kammala tsarinsa.

Ya bayyana cewa, tun daga shekarar 2019, gwamnatin jihar ta kan ** tabbatar da ajiyar kuɗi kafin fara kowanne babban aiki**, saboda dorewa da tabbatar da kammalawa akan lokaci.

Ahemba ya ce gina wadannan flyovers da under-pass ya zama dole sakamakon cunkoson ababen hawa da ke addabar yankin Karu–Mararaba, musamman ga mazauna da direbobi da matafiya.

“Wannan aiki zai magance matsalar cunkoso, ya inganta tafiyar ababen hawa, tare da ƙara ingancin hanyoyi,” in ji shi.

Ya kara da cewa gwamna ya bai wa Hukumar Nasarawa State Urban Development Agency (NUDA) umarnin gudanar da bincike da tantance wuraren da suka fi dacewa domin gina wadannan ayyukan.

Mr. Ahemba ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta kuduri aniyar fara aikin, ta kuma kammala shi kafin karewar wa’adinta a 2027.

Aliyu Muraki, Lafia.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Gudanar Da Taron Masana Harkokin Yada Labarai Karo Na 2 A Kano
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gina Gadar Sama Da Ta Kasa A Mararraba
  • Gwamnan Kano Ya Yaba Da Matakin Da Sojoji Suka Dauka kan Matsalar Tsaron Tsanyawa
  • Kwamishinan Kano Na Ziyarar Tabbatar Da Zaman Lafiya A Wannan Kaka
  • 2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC
  • Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya
  • An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa
  • Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
  • Abba ya umarci a riƙa gudanar da taron tsaro a ƙananan hukumomin Kano
  • Gidan rediyo ya ɗauki nauyin sanya yara 40 a makaranta a Kano