Aminiya:
2025-11-03@07:44:07 GMT

Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba

Published: 19th, March 2025 GMT

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya umarci ɗaukacin Masarautun Kano guda huɗu da su fara shirye-shiryen Hawan Sallah da bisa al’ada aka saba domin ganin jama’a da maziyarta sun nishaɗantu a yayin bukukuwan Sallah na bana.

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne a yayin wani taron buɗa-baki da sarakunan gargajiya da aka yi a ɗakin taro na Ante Chamber da ke gidan gwamnatin Kano a ranar Talata.

Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas HOTUNA: An yi gobara a kasuwar ’yan gwan-gwan da ke Kano

Abba ya jaddada cewa al’ummar jihar sun ƙagara don ganin wannan al’ada ta sanya sabbin tufafi a lokacin bukukuwan Sallah, tare da tsayawa a kan tituna domin kallon sarakunansu a kan doki suna musayar gaisuwa.

“Al’ummar Kano babu abin da suke a duniya, illa bayan azumin watan Ramadan, su caɓa ado, su fito su yi dandazo a bakin titi, sarkinsu ya fito, hakimai su fito a kan dawakai, su yi jinjina su yi godiya, sannan sarki ya yi musu addu’a.”

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba, kuma ba za ta bari wasu maƙiya su tauye wa al’ummar wannan haƙƙin da suke matuƙar mutuntawa ba.

Kazalika, ya tabbatar da cewa dukkanin hukumomin tsaro a jihar za su ba da himma wajen bai wa jama’a kariya a yayin bukukuwan.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa za a ƙaddamar da Majalisar Masarautar Jihar Kano a watan Afrilun bana domin samun damar gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

Ya bayyana cewa za a sanar da ka’idoji, tsare-tsare da sauran muhimman abubuwan da suka danganci majalisar a ranar ƙaddamarwa.

Ya yaba wa sarakunan bisa kyakkyawar alaƙar da suka nuna tun bayan naɗa su, inda ya ce wannan shi ne karo na farko a tarihin jihar da ake samun mutuntawa a tsakanin sarakunan musamman ta fuskar matsayi.

A nasa jawabin, Shugaban Majalisar Masarautar Kano kuma Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi II, ya tabbatar da cewa alaƙar da ke tsakaninsa da sarakunan ta musamman ce.

Ya yi kira ga Gwamnan da ya yi amfani da masarautun gargajiya wajen yaɗa manufofi da tsare-tsare ga al’umma, tare da tabbatar da aiwatar da ayyuka cikin inganci.

A nasu ɓangaren, Sarkin Karaye, Muhammad Muhammad Maharaz; Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru; da mai martaba Sarkin Gaya Dokta Aliyu Ibrahim Abdulkadir duk a madadin jama’arsu, sun yaba wa Gwamnan kan samar da takin zamani da sauran ababen more rayuwa a fannonin ilimi, lafiya da tituna a yankunansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Sallah Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka

A yayin da ake ci gaba da cece-kuce kan kalaman Shugaban Amurka Donald Trump da ke zargin gwamnatin Nijeriya da watsi da batun kisan Kiristoci a ƙasar, Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta bayyana cewa ta fara shirin kai farmaki a Nijeriya.

Sakataren Ma’aikatar, Pete Hegseth, ne ya tabbatar da hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, yana mai cewa ma’aikatarsa “na shirye-shiryen ɗaukar mataki” bayan umarnin da Trump ya bayar.

Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 

“Muna shirye-shirye don ɗaukar mataki a Nijeriya. Idan gwamnatin Nijeriya ba ta kare Kiristoci ba, za mu kai hari, mu kawar da ‘yan ta’addan Musulmai da ke aikata wannan ta’asar,” in ji Hegseth.

Trump dai ya yi wannan barazanar ne a cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, inda ya ce Amurka za ta dakatar da duk tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma tana iya “shiga ƙasar da ƙarfin soji domin share ‘yan ta’addan da ke kashe Kiristoci.”

“Idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da duk wata tallafi, kuma mai yiwuwa ta shiga wannan ƙasar, ta cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’addan Musulmai masu zafin kishin addini,” in ji Trump.

Ya kuma gargaɗi gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta ɗaukar mataki, yana cewa idan Amurka ta kai farmaki “za ta yi shi cikin sauri, da tsananin ƙarfi, da gamsuwa.”

Lamarin na zuwa ne kwana guda bayan Trump ya mayar da Nijeriya cikin jerin ƙasashen da za a sanyawa ido, yana zargin cewa “ana yi wa Kiristoci kisan gilla” a hannun ƙungiyoyin Musulmi masu tsattsauran ra’ayi.

Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai dimokuraɗiyya wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar ‘yan ƙasa daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.

A cewar mai ba wa Tinubun shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, za a yi ganawa tsakanin Shugaba Tinubu da Shugaba Trump “a cikin kwanaki kaɗan masu zuwa” domin tattaunawa da warware wannan saɓanin fahimta.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar