Aminiya:
2025-11-15@13:15:44 GMT

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira

Published: 19th, March 2025 GMT

Matatar Dangote ta sanar da dakatar da sayar da Man Fetur da Naira na wucin gadi.

Kamfanin ya bayyana wannan mataki ne a cikin wata sanarwa da ya aike wa dillalan man fetur a ranar Laraba da rana.

Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas  Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas

A cewar sanarwar, matatar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin guje wa matsalar biyan kuɗin ɗanyen mai da ta ke saya da dalar Amurka.

“Ya zuwa yanzu, mun sayar da sama da adadin man fetur da muka samu a Naira.

“Domin daidaita cinikayyarmu da sayen ɗanyen mai, dole ne mu ɗauki wannan mataki na wucin gadi,” in ji sanarwar.

Kamfanin Dangote ya kuma ƙaryata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa ya dakatar da sayar.

Kamfanin ya ce wannan labari ba gaskiya ba ne, inda ya jaddada cewa tsarinsa yana da inganci kuma ba a samu wata matsala ba.

Matatar ta Dangote ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da sayar da mai a Naira da zarar ta samu ɗanyen mai da aka sayar mata a Naira daga kamfanin NNPC.

“Muna nan daram wajen yi wa kasuwar Najeriya hidima, kuma za mu dawo da sayar da mai a Naira da zarar mun samu kaya,” in ji sanarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dalar Amurka da sayar da

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta bukaci duniya ta gaggauta daukar mataki a Sudan

Iran ta bukaci kasashen duniya dasu gaggauta daukar mataki kan halin da ake ciki a Sudan musamman a yankin El Fasher don magance matsalar dake ta’azzara a arewacin Darfour.

Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya, Ali Bahraini, ne ya bayyanan hakan a jawabinsa yayin zaman musamman na 38 kan yanayin kare hakkin dan adam a yankin El Fasher da kewaye a yayin rikicin da ke ci gaba da faruwa a Sudan.

Mista Bahraini ya yi gargadi game da yunwa, yawan ‘yan gudun hijira da kuma tasirin tsoma bakin kasashen waje kan rikicin.

Wadanan matsalolin sun haifar da daya daga cikin rikicin jin kai mafi muni a duniya, wanda ke bukatar kulawa nan take daga kasashen duniya,” in ji jakadan.

Jami’in na Iran ya soki kasashen duniya kan “yin shiru” yayin da rikicin ke kara ta’azzara kuma ya nuna damuwa game da shigar kasashen waje cikin lamarin.

Shishigin kasashen waje, gami da samar da makamai da daukar sojojin haya, suna kara rura wutar ci gaba da rikice-rikicen da kuma karuwar ta’azarar rikicin jin kai,” in ji shi.

Bahrain ya yi kira ga dukkan kasashe da su dauki “matakai masu tsauri,” su kare fararen hula da kuma tallafawa kokarin da ake yi na samar da zaman lafiya da haɗin kai mai ɗorewa a Sudan.

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce yakin ya yi sanadin mutuwar akalla mutane 40,000, kuma MDD ta ce wasu miliyan 12 sun rasa matsugunansu.

A zamansu na ranar Juma’a, manyan kungiyoyin kare hakkin bil’adama na MDD sun amince da wani kuduri da ya umarci tawagar bincike mai zaman kanta ta MDD kan Sudan da ta gaggauta binciki lamarin domin hukunci wadanda ke da laifi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka EU ta bukaci Isra’ila ta dauki mataki don kawo karshen tashin hankali a Yammacin Kogin Jordan November 15, 2025  Amurka Ta Sanar Da Fara Kai Farmakin Soja Mai Sunan ” Mashin Kudu” Akan Yankin Latin November 14, 2025 Ana Samun Kwararar ‘Yan Hijira Daga Mali Zuwa Kasar Cote De Voire November 14, 2025  Unrwa: Fiye Da Gidaje 282,000 “Isra’ila” Ta Rusa A Gaza November 14, 2025 Limamin Juma’a Ya Bukaci Ganin An Kai Karar Donald Trump A Kotunan Duniya November 14, 2025 Iran ce ta farko wajen fitar da dabino a duniya November 14, 2025 Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza November 14, 2025 Kwamitin Tsaro ya tsawaita wa’adin aikin tawagar MDD a Afrika ta Tsakiya November 14, 2025 Tehran da Ankara sun jaddada muhimmancin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin November 14, 2025 Iran ta yi tir da G7 kan goyon bayan takunkuman Amurka November 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahara sun kashe matan aure sun ƙona gidansu a Kano
  • Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
  • Iran ta bukaci duniya ta gaggauta daukar mataki a Sudan
  • Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
  • Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
  • Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe
  • An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe
  • Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harajin kashi 15 na shigo da fetur da dizal
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki