Aminiya:
2025-07-02@00:47:01 GMT

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira

Published: 19th, March 2025 GMT

Matatar Dangote ta sanar da dakatar da sayar da Man Fetur da Naira na wucin gadi.

Kamfanin ya bayyana wannan mataki ne a cikin wata sanarwa da ya aike wa dillalan man fetur a ranar Laraba da rana.

Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas  Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas

A cewar sanarwar, matatar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin guje wa matsalar biyan kuɗin ɗanyen mai da ta ke saya da dalar Amurka.

“Ya zuwa yanzu, mun sayar da sama da adadin man fetur da muka samu a Naira.

“Domin daidaita cinikayyarmu da sayen ɗanyen mai, dole ne mu ɗauki wannan mataki na wucin gadi,” in ji sanarwar.

Kamfanin Dangote ya kuma ƙaryata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa ya dakatar da sayar.

Kamfanin ya ce wannan labari ba gaskiya ba ne, inda ya jaddada cewa tsarinsa yana da inganci kuma ba a samu wata matsala ba.

Matatar ta Dangote ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da sayar da mai a Naira da zarar ta samu ɗanyen mai da aka sayar mata a Naira daga kamfanin NNPC.

“Muna nan daram wajen yi wa kasuwar Najeriya hidima, kuma za mu dawo da sayar da mai a Naira da zarar mun samu kaya,” in ji sanarwar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dalar Amurka da sayar da

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Tashin farashin man fetur a kasuwannin duniya ci-gaban mai hakar rijiya ne ga Nijeriya wadda ke kan gaba wajen fitar da mai ta yadda za ta samu makuddan kudin shiga sai dai gagarumar matsala ce ga ‘yan kasa wadanda za su fuskanci karin mai a cikin gida wanda zai zama silar karin kunci a dalilin farashin abubuwa da dama da zai hau sama. 

A cewar masana, Gabas ta Tsakiya da ke samar da akalla kashi 34 na mai a duniya da kashi 18 na gas, gumurzun kasashen biyu ya haddasa farashin danyen mai tashi da kashi 10, yayin da gas ya kara da kashi 7. Haka ma akwai fargabar Isra’ila na iya illata harkokin mai da jigilarsa a mashigar Hormuz da ke karkashin ikon Iran.

Baya ga wannan farashin rarraba kaya da fitar da kaya ta jiragen ruwa ya karu a bisa ga tashin kudin inshoran jiragen ruwa a Gabas ta Tsakiya wanda ya kawo tsaikon kasuwanci a duniya. 

A yanzu haka dai a wannan makon kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL) ya fitar da sanarwar karin kudin mai a gidajen man sa a fadin kasar bakidaya. 

Tun a kwanan baya masana suka bayyana cewar farashin man fetur zai tashi a kasuwannin duniya a dalilin fafatawar yakin Iran da Isra’ila. 

Kamfanin ya bayyana karin kudin mai zuwa naira 945 wanda karin ya biyo bayan karin kudin mai da matatar mai ta Dangote mai zaman kan ta ta yi zuwa naira 880. 

A bayyana yake cewar Iran babbar kasa ce daga cikin manyan kasashen duniya masu karfin arzikin man fetur da ke fitar da shi a kasashen duniya don haka wajibi ne yaki da kasar ya shafi tattalin arzikin kasashe da dama. 

Duk da matatar mai ta Dangote ta na aiki amma har zuwa yanzu shigo da man fetur ake yi a Nijeriya don haka tashin farashin a kasuwannin duniya na nufin tashin farashinsa a Nijeriya kamar yadda masana suka bayyana. 

Da yake bayani kan illar yakin ga Nijeriya, masani kan tattalin arziki da huldar diflomasiyya kuma Shehin Malami a jami’ar Ibadan, Farfesa Tayo Bello ya yi gargadin yakin zai shafi Nijeriya da babban kalubale sosai. 

Ya ce Nijeriya wadda ita ce babbar kasar Afurka mafi albarkatun mai za ta ci-gaba da amfana da karin kudin mai a gajeren lokaci, amma hakan zai haifar da gagarumar illa ga ‘yan Nijeriya a gida.

“Yakin tamkar takobi biyu ne mai kaifi ga Nijeriya, a daya hannu a na tsammanin farashin mai a kasuwar duniya zai tashi sosai. Hakan na nufin Nijeriya za ta ci-gaba da samun karin haraji sosai musamman idan farashin ya tashi daga dala 75 a ganga daya zuwa dala 90 ko sama da haka.”

“Karin kudin mai a duniya na nufin karin kudin mai a Nijeriya. Man dizel, fetur da sauran abubuwa za su yi tsada sosai wanda hakan na nufin hauhawar farashi sosai.”

Injiniya Yabagi Sani fitaccen mai sharhi kan al’ummarran man fetur a Nijeriya ya bayyanawa BBC Hausa cewar illar da yakin ya yi wa sauran kasashen duniya shine ya shafi Nijeriya. 

Ya ce a bayyane yake kusan kashi 20 zuwa 30 na mai da ake hada- hadarsa a kasuwannin duniya a na yin sa ne ta mashigar Hormuz da ke karkashin kasar Iran don haka su ke da ikon shiga da ficen mai. 

Masanin ya bayyana cewar a sakamakon wannan yakin Iran ta yi barazanar rufe mashigar wanda sakamakon fargabar matsalar da za ta iya biyowa baya, jiragen dakon man fetur suka fara kauracewa mashigar wanda a cewarsa wannan ne ya haifar da karancin mai a kasuwandnin duniya bakidaya.”  

Shi kuwa tsohon jakadan Nijeriya a kasar Ethiopia, Bulus Lolo na ganin ko kadan ba alheri ba ne ga kowa ciki har da Nijeriya kan ci-gaba da nunawa juna yatsa da kasashen biyu ke yi. 

Ya ce a wasu lokutan fada irin wannan yana da amfani, a wasu lokutan kuma ba ya da amfani. Nijeriya ba ta fuskantar farmaki kai tsaye, amma ta na amayar da muryar ta kan kasashen biyu da su tsagaita wuta su daina kaiwa juna hari, a zauna a teburin sulhu.*

Ya ce kasuwar mai a duniya za ta shaidi artabun da ke faruwa a ma’ajiyar man Iran, amma ba su fatar kazantar lamariin a  kasuwar duniya, a cewarsa suna fatar abubuwa za su daidaita domin hasashen su ya tafi daidai. 

“Akwai yiyuwar karin kudi ta yadda farashi zai hau sama sosai amma har zuwa yaushe? Sabani ne wanda ba mu san yadda karshensa zai kasance ba.” In ji Lolo. 

Masana da jama’a na ganin mafitar kawar da radadin farashin mai a Nijeriya shine gwamnafi ta inganta matatun mai, ta yadda za su rika aiki yadda ya kamata domin samar da wadataccen mai ga ‘yan kasa.

Haka ma gwamnati za ta iya saukakawa jama’a ta hanyar rage farashin mai wanda hakan zai magance hauhawar farashin kaya da al’umma ke fargaba a halin yanzu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
  • Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
  • Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki
  •  HKI:Har Yanzu Matatar Man Fetur Ta Haifa Ba Ta Koma Aiki Ba
  • Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
  • Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara
  • Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
  • An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina
  •   Ka’a’ni: Nasarar Da Mu Ka Samu Za Ta Ci Gaba Da Dorewa