Aminiya:
2025-11-07@16:57:28 GMT

Goman Ƙarshe: Dama ta ƙarshe ga mai neman rahamar Allah

Published: 19th, March 2025 GMT

Ga shi dai kwanakin Ramadan suna ta gudu, har mun kawo ga goman ƙarshe wanda shi ne dama ta ƙarshe ga wanda ya yi sakaci a farkon watan, ko kuma ya zama cikon alheri ga wanda ya kyautata ya bayar da abin da ake so a baya.

Ya ku masoya! Goman ƙarshe na watan Ramadan kasuwa ce babba da masu tsere suke tserereniya a cikinta.

Abubuwan da ba a sakaci da su a Ramadan —Sheikh Daurawa DAGA LARABA: Abin Da Ake Yi A Goman Tsakiyar Ramadan A Addini Da Al’ada

Lokaci ne da wanda ya yi sakaci yake ƙara ƙwazo a cikinsa, ake jarraba masu himma a cikinsa, ake tantance ma’abota Lahira da ma’abota duniya.

Da yawa masu huɗuba sun yi magana, masu wa’azi sun yi wa’azi, masu nasiha sun yawaita nasiha kan falalolin wadannan kwanaki da darare, zukatan da suka jiku da imani sun amshi wannan kira, wata jama’a ta amshi kiran ta bi hanyar muminai, ta koma cikin masu ruku’u da sujada, hawayensu na kwarara a tsakiyar dare mai duhu, kuma Ubangijinka Yana ji kuma Yana amsa musu, Ubangijinka bai zama Mai zaluntar bayi ba.

Wata jama’ar kuma ta ji kiran amma kamar ba ta damu ba. Suna jin muminai suna salloli da tsayuwar dare don ibada ga Ubangijinsu, amma su kamar ba su da bukata, kai kamar an yi musu lamunin Aljanna, shin masu wannan watsewa ba za su yi tunani ba?

Shin masu wannan sakaci ba za su sake tunani ba?

Ya ku Musulmi! Ranakun watanku suna raguwa, dararensa masu daraja suna karewa, suna masu shaida a kan abin da kuka aikata, suna kiyaye abin da kuka yi, su masu taskace kyawawan ayyukanku, masu tsarewa da adana su har zuwa lokacin da za a kira ku a Ranar Kiyama: “A Ranar da kowane rai ke samun (sakamakon) abin da ya yi.”

Ubangijinku Yana kira: “Ya ku bayiNa! Abin sani ayyukanku ne Nake kidaya muku kuma zan saka muku a kai.

Duk wanda ya samu alheri sai ya gode wa Allah, wanda ya samu wanin wannan kuma, kada ya zargi kowa sai kansa!”

Wannan watanku ne kuma wannan ne dama ta karshe, mutum nawa ne ya fara azumin bai kawo yanzu ba, ko ba zai kammala shi ba?

Kuma mutum nawa ya yi kwadayin dawowarsa a bana amma bai riske shi ba? Shin ba za ku yi nazari a kan ajali da makomarku ba?

Shin ba za ku dubi yaudarar da dogon buri yake yi muku ba?

Ya ku Musulmi! Idan akwai mai gargadi ga rayuka ko mai wa’azi ga zukata, to, bai wuce dan abin da ya saura na kwanakin Ramadan ba.

Saura kwana nawa ne? Muna shirin shiga goma na karshe, kwanakin da Annabinku (S.A.W) yake matukar zage damtse domin bauta wa Allah.

A ashirin na farko yana hada sauran ibadoji da Sallah da barci, amma da goman karshe ya shigo, sai ya tattara shimfidarsa ya daure mazagin wadonsa, ya kaurace wa shimfidar barcinsa, ya tashi iyalansa ya kwankwasa kofar Fatima da Aliyu (Allah Ya yarda da su) yana mai cewa: “Ashe ba za ku tashi ku yi Sallah ba?”

Sannan ya fuskanci dakunan matansa yana umarni tare da bayyana cewa: “Ku farka Ma’abota Babban Gida (Ahlul Bait), da yawa masu sutura a duniya tsirara suke a Lahira.”

Annabi (S.A.W) ya kasance idan goman karshe na Ramadan ya zo, ba ya barin duk wanda zai iya tsayuwar dare daga cikin iyalinsa a kwance face ya tashe shi.

Kuma magabatan kwarai sun fi sauran mutane bibiya da koyi da Annabi (S.A.W).

Ya zo a cikin Muwadda na Imam Malik (Allah Ya yi masa rahama) cewa Umar dan Khaddabi (RA) ya kasance yana Sallah gwargwadon yadda Allah Ya so, har sai dare ya raba, sai ya tashi iyalansa yana ce musu “Sallah! Sallah!”

Sannan sai ya karanto wannan aya: “Ka umarci iyalinka da yin Sallah da hakuri a kanta. Ba Mu tambayarka dukiya, Mu ne masu azurta ka, kuma kyakkyawan karshe na masu taƙawa ne.”

Sufyanu Suri (Rahimahullah) ya ce, “An so idan goma karshe ya shigo (Musulmi) ya yi kokari da daddare ya yi kokari a cikinsa, ya tashi iyalinsa da ’ya’yansa su yi Sallah matukar za su iya hakan.”

Wata mata daga cikin magabatan kwarai ta fada wa mijinta cewa: “Hakika dare ya tafi alhali akwai doguwar tafiya a gabanmu, sannan guzirinmu kadan ne, kuma ayarin salihai ya yi mana nisa, mu ne muka saura a hanya!”

Ya ku Musulmi! Ku san darajar zamaninku, ku girmama mafi falalar lokacinku, ku gabatar da aikin alheri domin kanku.

Kada ku bata lokacinku a cikin abin da ba neman kusanci ba ne ga Allah. Ba da buri ake kyautata zaton alheri ba, ana kyautata zato ne da kyautata aiki.

Sanya ran samun rahama tare da aikata sabo wani nau’i ne na wauta da tabewa. Ba da kuka da share hawaye ake tsoron Allah ba, ana tsoron Allah ne ta barin abin da ake tsoron ukuba a kansa.

Ya ku masoya! Ku gabatar da aikin alheri ga kanku, ku tsayu kuma ku yi kankan da kai.

Uwar Muminai A’isha (Allah Ya yarda da ita) ta ce: “Ya Manzon Allah! Shin idan na riski daren Lailatu Kadari me zan ce a cikinsa?

Sai ya ce: “Ki ce: “Allahumma innaka afuwun tuhibbul afuwa, fa’afu anni.”

Ma’ana “Ya Ubangiji! Kai Mai yawan afuwa ne, Kana son afuwa, Ka yi min afuwa.” Ku yawaita wannan addu’a a cikin goman karshe.

Ubangijinku Ya ce, “Idan bayiNa suka tambaye ka game da Ni, to, lallai ne Ni ina kusa, Ina amsa kiran wanda ya yi kira idan ya kira Ni.

“Don haka su amsa Min, kuma su yi imani da Ni, tsamaninsu suna shiryuwa.”

Ko kun san su wane ne wadannan bayi? Halittu dukkansu bayin Allah ne, sai dai kuma wadannan bayi kebantattu ne.

Su ne bayi daga ma’abuta addu’a, bayin da suke jirar a amsa musu, su ne masu addu’a cikin kankan da kai, masu addu’a tare da babbar fata, masu kankan da kai wajen kwadayin amsawa; “Idan bayiNa suka tambaye ka game da Ni, to, lallai Ni ina kusa…”

Lallai addu’a tana da wani sha’ani mai ban-mamaki da tasiri babba wajen kyawun karshe da gyara hali da dukiya da dacewa a cikin ayyuka da albarka a cikin arziki.

Shin ba ku ganin wanda ya dace da rabo ta wajen addu’a, yana samun rabonsa daga kankan da kai da fakewa ne a wurin Allah a kowane hali ba?

Shi ne yake komawa ga Allah a dukkan bukatunsa ya yi addu’a, a yi masa addu’a, ya rabauta da addu’arsa ta kashin kansa da ta waninsa.

Mahaifansa suna son sa, ’ya’yansa suna yi masa da’a, mutanen da suke kusa da shi dukkansu suna kewaye shi da addu’a.

Mahaliccinsa Yana son sa, don haka Ya fawwala karba masa. Sai halayensa su kyautata, aikinsa ya yi kyau, hannuwa su dagu sama, harsuna su daukaka wajen yi masa addu’a.

Allah Yana lura da shi Ya datar da shi, sha’aninsa yana kyautatuwa tare da dacewa.

Yaya za a kwatanta shi da wanda aka haramta masa haka, wulakatacce wanda bai dandani zakin ganawa da Ubangijinsa a Ramadan ba?

Yaya za a hada shi da wanda ya ji kunyar bauta wa Ubangijinsa, ya yi girman kai daga rokon Ubangijinsa? Abin haramtawa da ya rufe kofar rahama ga kansa, ya lulluba da tufar gafala?

Hudubar Juma’a daga Muhammad bin Mabrouk Lu’awani, Masallacin Khalid bin Walid da ke Saudiyya

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Goman Karshe Rahama Ramadan Wa azi

এছাড়াও পড়ুন:

Mamdani ya zama Musulmi na farko da ya zama magajin garin New York na Amurka

Zohran Mamdani ya lashe zaben Magajin Garin birni mafi girma a Amurka wato New York, kuma zai zama Musulmi na farko a tarihi da ya taɓa shugabantar birnin. Mamdani, mai shekara 34 kuma dan jam’iyyar Democrat mai ra’ayin gurguzu, ya samu nasara bayan ya motsa masu ra’ayin sauyi a cikin birnin da ma fadin ƙasar, duk da suka daga Shugaba Donald Trump da ‘yan Republican, da wasu ‘yan Democrat masu matsakaicin ra’ayi. Tinubu na neman majalisa ta amince masa ya ciyo sabon bashin Tiriliyan 1.150 An yi musayar yawu tsakanin Barau da Akpabio a majalisa kan barazanar Trump A jawabin nasararsa bayan doke tsohon Gwamna Andrew Cuomo, Mamdani ya ce yana da cikakken goyon baya daga jama’a, kuma ya bayyana kansa a matsayin wanda ke gaba da Trump. Ya ce, “A wannan lokaci na duhun siyasa, New York zai zama birni haske.” Ya ƙara da cewa, “Tare za mu kawo sauyi ga wannan zamani. Idan muka rungumi wannan sabuwar hanya ta jarumta maimakon mu gudu daga gare ta, za mu iya fuskantar mulkin masu kuɗi da na danniya da ƙarfin da suke tsoro, ba da sassaucin da suke nema ba.” Mamdani ya ci gaba da kalubalantar Trump kai tsaye: “Wannan ba kawai yadda za mu dakatar da Trump ba ne, har da wanda zai biyo bayansa. Don haka Donald Trump, tun da na san kana kallo, ina da kalmomi guda huɗu gare ka: Kara sauti.” Jawabinsa bai tsaya kan Trump kaɗai ba. Ya fara da ambaton Eugene Debs, wani ɗan gurguzu na ƙarni na 19 da 20, sannan ya yi alkawarin aiwatar da “tsarin da ya fi kowanne girma” don rage tsadar rayuwa a New York tun bayan zamanin Magajin Gari Fiorello LaGuardia kusan shekaru 100 da suka wuce. Mamdani ya doke Cuomo, wanda ya tsaya takara a matsayin ɗan mai zaman kansa bayan faduwa a zaɓen fidda gwani na Democrat a watan Yuni, da kusan maki 9. Dan takarar Republican Curtis Sliwa ya zo nesa da Mamdani. Magajin Gari Eric Adams, wanda ya tsaya takara a matsayin ɗan jam’iyya ta uku bayan nasararsa a 2021 a matsayin Democrat, ya janye a watan Satumba kuma ya goyi bayan Cuomo a watan da ya gabata. Wannan nasara ta Mamdani ta nuna yadda ya yi tasiri cikin siyasar New York cikin shekara guda, daga matsayin ɗan majalisar jiha da ba a san shi ba sosai, zuwa jagoran birni mafi girma a Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon
  • Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu
  • Mamdani ya zama Musulmi na farko da ya zama magajin garin New York na Amurka
  • Tinubu na neman majalisa ta amince masa ya ciyo sabon bashin Tiriliyan 1.150