Aminiya:
2025-12-15@04:37:09 GMT

Gobara ta kashe yara 3, ta jikkata 13 a Yobe

Published: 19th, March 2025 GMT

Rahotanni sun nuna cewa gobara ta kashe yara uku tare da jikkata wasu 13 a ƙauyuka tara na Jihar Yobe, tsakanin watan Janairu zuwa Maris ɗin 2025.

Gobarar ta kuma lalata gidaje 86, inda ta bar mutane da dama ba tare da matsuguni ba.

Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas Ba tarbiyya nake koyarwa ba — Sadiq Sani Sadiq

Babban sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Yobe (YOSEMA), Dokta Mohammed Goje, ya bayyana cewa rashin kula da wutar lantarki, amfani da gas, ƙonewar daji, da kuma zubar da shara ba bisa ƙa’ida ba, ke haddasa yawan gobara a jihar.

Ya ce lamarin ya fi shafar yankunan Damaturu, Gulani, da Yusufari, inda mazauna ke kokawa kan asarar da suka yi.

Domin magance matsalar, hukumar YOSEMA ta fara wayar da kan jama’a kan hanyoyin kauce wa gobara.

Haka kuma, sun kafa kwamitoci da za su taimaka wajen kare lafiyar al’umma, musamman a lokacin rani da hunturu.

Dokta Goje ya ce hukumar, tare da haɗin gwiwar Hukumar Kashe Gobara ta jihar, za su ɗauki matakan hana ƙone daji da kuma bin ƙa’idojin zubar da shara domin rage haɗuran gobara.

A gefe guda, Gwamna Mai Mala Buni ya umarci hukumar YOSEMA da ta tantance ɓarnar da gobarar ta yi, domin sanin irin taimakon da waɗanda lamarin ya shafa suke buƙata.

Gwamnan ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa za a tallafa musu.

A halin yanzu, hukumomi na ci gaba da faɗakar da jama’a kan muhimmancin kiyaye dokokin kare gobara domin gujewa aukuwar irin wannan iftila’i a gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara gwamnati rasuwa shara yara

এছাড়াও পড়ুন:

Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria

Majalisar Karamar Hukumar Birnin Kudu ta bada tabbacin hada hannu da bankin ajiya na Savings and Loan na Jihar Jigawa domin habaka tattalin arziki.

Shugaban Karamar hukumar, Dr. Builder Muhammad Uba ya bada wannan tabbaci a lokacin da Manajan bankin, Babandi Isah Gumel ya kai masa ziyara.

Builder Muhammad Uba ya ce karamar hukumar za ta ci gaba da mu’amulla da bankin wajen ganin ma’aikatan wucin gadi na bude asusun ajiya a bankin.

Ya kuma bayyana farin cikinsa kan wannan ziyara da kuma karrama shi da aka yi.

A jawabinsa, Manajan bankin Savings and Loan na Jihar Jigawa, Babandi Isa Gumel, ya ce sun karrama shugaban Karamar hukumar ne bisa daukar ma’aikatan wucin gadi a karamar hukumar ta birnin kudu.

Yace Dr Muhammad Uba ya dauki ma’aikatan da dama a fannin kiwon lafiya da ilimi wato B-health da B-teach da kuma amincewa da yin mu’amulla da bankin.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano
  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Iyaye Sun Yi Fitowar Farin Dango Don Yi Wa “Yayansu Allurar Rigakafi a Sule-Tankarkar
  • Ma’aikatar Ilimi ta Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 18 a 2026
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Kiyasta Naira Biliyan 3 Don Ayyukan Hajjin 2026
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su