Aminiya:
2025-11-08@16:11:53 GMT

Gobara ta kashe yara 3, ta jikkata 13 a Yobe

Published: 19th, March 2025 GMT

Rahotanni sun nuna cewa gobara ta kashe yara uku tare da jikkata wasu 13 a ƙauyuka tara na Jihar Yobe, tsakanin watan Janairu zuwa Maris ɗin 2025.

Gobarar ta kuma lalata gidaje 86, inda ta bar mutane da dama ba tare da matsuguni ba.

Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas Ba tarbiyya nake koyarwa ba — Sadiq Sani Sadiq

Babban sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Yobe (YOSEMA), Dokta Mohammed Goje, ya bayyana cewa rashin kula da wutar lantarki, amfani da gas, ƙonewar daji, da kuma zubar da shara ba bisa ƙa’ida ba, ke haddasa yawan gobara a jihar.

Ya ce lamarin ya fi shafar yankunan Damaturu, Gulani, da Yusufari, inda mazauna ke kokawa kan asarar da suka yi.

Domin magance matsalar, hukumar YOSEMA ta fara wayar da kan jama’a kan hanyoyin kauce wa gobara.

Haka kuma, sun kafa kwamitoci da za su taimaka wajen kare lafiyar al’umma, musamman a lokacin rani da hunturu.

Dokta Goje ya ce hukumar, tare da haɗin gwiwar Hukumar Kashe Gobara ta jihar, za su ɗauki matakan hana ƙone daji da kuma bin ƙa’idojin zubar da shara domin rage haɗuran gobara.

A gefe guda, Gwamna Mai Mala Buni ya umarci hukumar YOSEMA da ta tantance ɓarnar da gobarar ta yi, domin sanin irin taimakon da waɗanda lamarin ya shafa suke buƙata.

Gwamnan ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa za a tallafa musu.

A halin yanzu, hukumomi na ci gaba da faɗakar da jama’a kan muhimmancin kiyaye dokokin kare gobara domin gujewa aukuwar irin wannan iftila’i a gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara gwamnati rasuwa shara yara

এছাড়াও পড়ুন:

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

Dangane da fargaba game da karancin abinci na amfanin gona da aka canza jinsinsu (GMOs), farfesan ya ce domin tabbatar da lafiyar abinci da kare lafiyar jama’a, dole ne kowace iri da za ta shigo kasar ta bi matakan doka da ka’idoji da ke tabbatar da cewa tana da aminci. Ya ce, dokokin da ake amfani da su wajen kula da GMOs ma sun fi tsauri fiye da na amfanin gona na gargajiya saboda an kara musu sinadaran halittu (genetic materials).

“Kafin a saki kowane irin amfanin gona domin a fara amfani da shi a kasuwanci, dole ne ta bi diddigin binciken halittu da sinadaran gina jiki sosai. Bayanai da ake da su a halin yanzu sun nuna cewa amfanin gona na GMO suna da lafiya, bisa sama da bincike 200 da aka gudanar a Turai, Amurka, Latin Amurka da wasu kasashen Afirka.

Shi ya sa aka amince a ci su, domin sun cika sharudan tsaro. Babu wani rahoto daga Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ko kuma Hukumar Abinci da Aikin Gona ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO) da ya nuna cewa amfanin gona ko abincin da aka sarrafa ta hanyar ilmin kwayoyin halitta (GMO) na da illa ga mutane ko dabbobi.

A halin yanzu akwai amfanin gona irin su masara, tumatir, shinkafa, waken suya da gwanda da aka sarrafa ta hanyar GMO a kasuwa. Babu wani tabbacin matsalar tsaro game da hakan.”

Adamu ya ce Nijeriya ba ta samar da isasshen abinci na gargajiya (organic) ba, sai dai amfanin gona na yau da kullum kamar sauran kasashe masu tasowa, inda manoma ke amfani da takin zamani, magungunan kashe kwari da sauran sinadarai.

Ya bayyana cewa amfanin gona na kwayoyin halitta (GM crops), an noman wasu daga cikinsu ne domin su iya jure matsalolin da manoma ke fuskanta a lokacin noman su, kamar kwari masu lalata shuka, irin su stem borer da kuma kwaron fall armyworm.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026 November 7, 2025 Tattalin Arziki Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho November 7, 2025 Tattalin Arziki Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria October 25, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan
  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Cin zarafin Wakilin NTA ya tada ƙura a Yobe
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku a Kudancin Lebanon  
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano