Aminiya:
2025-11-22@19:41:44 GMT

Gobara ta kashe yara 3, ta jikkata 13 a Yobe

Published: 19th, March 2025 GMT

Rahotanni sun nuna cewa gobara ta kashe yara uku tare da jikkata wasu 13 a ƙauyuka tara na Jihar Yobe, tsakanin watan Janairu zuwa Maris ɗin 2025.

Gobarar ta kuma lalata gidaje 86, inda ta bar mutane da dama ba tare da matsuguni ba.

Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas Ba tarbiyya nake koyarwa ba — Sadiq Sani Sadiq

Babban sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Yobe (YOSEMA), Dokta Mohammed Goje, ya bayyana cewa rashin kula da wutar lantarki, amfani da gas, ƙonewar daji, da kuma zubar da shara ba bisa ƙa’ida ba, ke haddasa yawan gobara a jihar.

Ya ce lamarin ya fi shafar yankunan Damaturu, Gulani, da Yusufari, inda mazauna ke kokawa kan asarar da suka yi.

Domin magance matsalar, hukumar YOSEMA ta fara wayar da kan jama’a kan hanyoyin kauce wa gobara.

Haka kuma, sun kafa kwamitoci da za su taimaka wajen kare lafiyar al’umma, musamman a lokacin rani da hunturu.

Dokta Goje ya ce hukumar, tare da haɗin gwiwar Hukumar Kashe Gobara ta jihar, za su ɗauki matakan hana ƙone daji da kuma bin ƙa’idojin zubar da shara domin rage haɗuran gobara.

A gefe guda, Gwamna Mai Mala Buni ya umarci hukumar YOSEMA da ta tantance ɓarnar da gobarar ta yi, domin sanin irin taimakon da waɗanda lamarin ya shafa suke buƙata.

Gwamnan ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa za a tallafa musu.

A halin yanzu, hukumomi na ci gaba da faɗakar da jama’a kan muhimmancin kiyaye dokokin kare gobara domin gujewa aukuwar irin wannan iftila’i a gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara gwamnati rasuwa shara yara

এছাড়াও পড়ুন:

Tuƙin ganganci: KASTELEA  Ƙaddamar Da gangamin wayar da kai a Zariya

Hukumar Kula da Tsaftace Muhalli da Ababen Hawa ta Jihar Kaduna (KASTELEA) ta ƙaddamar da yaƙin wayar da kan jama’a na watannin ƙarshen shekara na shekarar 2025 a Tashar Motoci ta Malam Nasiru El-Rufa’i da ke ’Yan Ƙarfe, Sabon Gari, Zariya.

Taron yaƙin wayar da kan jama’a na  ‘Watannin Ember’ na shekarar 2025 mai taken: “Tafiyar aminci ana cimma ta ta hanyar tuƙi cikin tsaro,” ya samu halartar hukumomin tsaro daban-daban da ke da ƙudirin rage haɗurra a kan manyan hanyoyin jihar

A wajen taron, Sarkin Zazzau, Malam Ahmad Nuhu Bamalli, ya jaddada muhimmancin rawar da kowa a cikin al’umma zai taka wajen tabbatar da tsaron hanya da kuma tuƙi cikin natsuwa.

Wakilin Sarkin a taron, Injiniya Ibrahim Balarabe Musa, ya bayyana cewa harkar kula da zirga-zirgar ababen hawa aiki ne da ya haɗa hukumomi da dama.

Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba

“Batun zirga-zirga ba na hukuma ɗaya ba ne. Rundunar ’yan sanda, ma’aikatan kashe gobara, Sibil Difens Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) duk suna da rawar da za su taka wajen cimma manufa ɗaya — tsaro,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa wayar da kan jama’a kan tsaro a hanya aiki ne na kullum, tare da yaba wa jajircewar ma’aikatan tsaro.

‘Watannin Ember’ da cunkoson hanya

A nata jawabin, Shugabar KASTELEA, Karla AbdulMalik, ta bayyana cewa Watannin Ember — daga Satumba zuwa Disamba — sukan fi fuskantar cunkoso sakamakon tafiye-tafiyen al’umma domin bukukuwan ƙarshen shekara.

Ta ce yawan zirga-zirgar ababen hawa a wannan lokaci kan haifar da cunkoso, tuƙin ganganci fa kuma karuwar hadurra, lamarin da ke janyo asarar rayuka da dukiya.

“Mun zo ne domin wayar da kan jama’a su bi ƙa’idojin hanya, tare da ƙarfafa wa fasinjoji gwiwa su tsawatar idan suka ga direba na tuƙi cikin hatsari. Kauce wa haɗurra nauyi ne da ya rataya a kan kowa,” in ji ta.

Ta buƙaci direbobi da ke cikin jihar ko masu wucewa su kiyaye dokokin hanya, su kuma rinƙa tuƙi cikin natsuwa don tsira da rayuwar al’umma.

Kiran FRSC da ƙungiyoyin sufuri

A nasa ɓangaren, Kwamandan Shiyyar Zariya na Hukumar FRSC, Nasiru Abdullahi Falgore, wanda SRC Kabiru Kabiru Mado ya wakilta, ya bayyana wannan lokaci a matsayin na tsananin taka-tsantsan.

Ya nuna damuwa kan yawaitar mutuwar mutane da asarar dukiya, tare da kira ga direbobi su bi doka su kuma ɗauki matakan rage haɗurra.

Daga ɓangaren kungiyoyin sufuri, Mataimakin Shugaban NARTO na Jihar Kaduna, Sa’idu Mustapha Basawa, ya bayyana kyakkyawar hulɗar da ke tsakaninsu da hukumomin tsaro.

Ya kuma buƙaci gwamnati ta ƙara sanya alamun hanya a wurare masu muhimmanci, tare da jaddada buƙatar direbobi su riƙa bin ƙa’idojin hanya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Ta Kashe Yara Falasdinawa Guda 22 A Yankin Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Tuƙin ganganci: KASTELEA  Ƙaddamar Da gangamin wayar da kai a Zariya
  • Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • UNICEF Ta Jinjinawa Jihohin Kano, Katsina da Jigawa Bisa Inganta Rayuwar Kananan Yara
  • Dalibai a Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Koka Game da Ƙalubalen Tsaro a Yankin
  • Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
  • Jihar Jigawa Ta Amince da Naira Biliyan 3.5 a Matsayin Kudaden Tallafin UBEC 2025
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 
  • Za a aurar da marayu 200 a Zamfara