Gobara ta kashe yara 3, ta jikkata 13 a Yobe
Published: 19th, March 2025 GMT
Rahotanni sun nuna cewa gobara ta kashe yara uku tare da jikkata wasu 13 a ƙauyuka tara na Jihar Yobe, tsakanin watan Janairu zuwa Maris ɗin 2025.
Gobarar ta kuma lalata gidaje 86, inda ta bar mutane da dama ba tare da matsuguni ba.
Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas Ba tarbiyya nake koyarwa ba — Sadiq Sani SadiqBabban sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Yobe (YOSEMA), Dokta Mohammed Goje, ya bayyana cewa rashin kula da wutar lantarki, amfani da gas, ƙonewar daji, da kuma zubar da shara ba bisa ƙa’ida ba, ke haddasa yawan gobara a jihar.
Ya ce lamarin ya fi shafar yankunan Damaturu, Gulani, da Yusufari, inda mazauna ke kokawa kan asarar da suka yi.
Domin magance matsalar, hukumar YOSEMA ta fara wayar da kan jama’a kan hanyoyin kauce wa gobara.
Haka kuma, sun kafa kwamitoci da za su taimaka wajen kare lafiyar al’umma, musamman a lokacin rani da hunturu.
Dokta Goje ya ce hukumar, tare da haɗin gwiwar Hukumar Kashe Gobara ta jihar, za su ɗauki matakan hana ƙone daji da kuma bin ƙa’idojin zubar da shara domin rage haɗuran gobara.
A gefe guda, Gwamna Mai Mala Buni ya umarci hukumar YOSEMA da ta tantance ɓarnar da gobarar ta yi, domin sanin irin taimakon da waɗanda lamarin ya shafa suke buƙata.
Gwamnan ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa za a tallafa musu.
A halin yanzu, hukumomi na ci gaba da faɗakar da jama’a kan muhimmancin kiyaye dokokin kare gobara domin gujewa aukuwar irin wannan iftila’i a gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara gwamnati rasuwa shara yara
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta tabbatar da mutuwar wasu jami’anta guda biyar a ƙauyen Sabon Sara da ke Ƙaramar Hukumar Darazo, sakamakon harin da wasu ’yan bindiga suka kai.
Kakakin rundunar, CSP Ahmed Wakil ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranae Lahadi.
An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu Ɗalibai 50 da aka sace a Neja sun kuɓuta — CAN“‘Yan sanda biyar sun rasu, biyu sun jikkata, amma an yi nasarar kashe wasu daga cikin ’yan bindigar a ƙauyen Sabon Sara, Ƙaramar Hukumar Darazo, a jihar Bauchi.”
Wakil, ya ƙara da cewa, “Ma’aikatanmu suna jajircewa kuma sun samu nasarar kashe wasu daga cikin ’yan bindigar yayin musayar wuta.”
Ya bayyana ’yan sanda suna aikin sintiri lokacin da aka kai musu harin.
Wakil, ya bayyana sunayen ’yan sandan da suka rasa rayukansu; DSP Ahmad Muhammad (SID), ASP Mustapha Muhammad (10 PMF), Amarhel Yunusa (10 PMF), Idris Ahmed (10 PMF), da Kofur Isah Muazu (AKU).
’Yan sandan da suka ji rauni sun haɗa da Isah Musa (SID) da Insifekta Yusuf Gambo (SID).
Ya ƙara da cewa, “Bayan samun rahoton, Shugaban ’yan sandan Ƙaramar Hukumar, SP Auwalu Ilu, ya jagoranci tawaga tare da ceto waɗanda suka jikkata.
“Sun kai waɗanda suka rasu Babban Asibitin Darazo, inda aka ajiye gawarwakin a ɗakin ajiyar gawa.
“Ana ƙokarin kama waɗanda suka aikata wannan mummunan laifi tare da hukunta su,” in ji Wakil.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya ziyarci wajen da lamarin ya faru, sannan miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu.
“Aikin nan ba abu ne mai sauƙi ba. Duk da haka, bisa doka, za mu ci gaba da jajircewa ba dare ba rana don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.”