Gobara ta kashe yara 3, ta jikkata 13 a Yobe
Published: 19th, March 2025 GMT
Rahotanni sun nuna cewa gobara ta kashe yara uku tare da jikkata wasu 13 a ƙauyuka tara na Jihar Yobe, tsakanin watan Janairu zuwa Maris ɗin 2025.
Gobarar ta kuma lalata gidaje 86, inda ta bar mutane da dama ba tare da matsuguni ba.
Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas Ba tarbiyya nake koyarwa ba — Sadiq Sani SadiqBabban sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Yobe (YOSEMA), Dokta Mohammed Goje, ya bayyana cewa rashin kula da wutar lantarki, amfani da gas, ƙonewar daji, da kuma zubar da shara ba bisa ƙa’ida ba, ke haddasa yawan gobara a jihar.
Ya ce lamarin ya fi shafar yankunan Damaturu, Gulani, da Yusufari, inda mazauna ke kokawa kan asarar da suka yi.
Domin magance matsalar, hukumar YOSEMA ta fara wayar da kan jama’a kan hanyoyin kauce wa gobara.
Haka kuma, sun kafa kwamitoci da za su taimaka wajen kare lafiyar al’umma, musamman a lokacin rani da hunturu.
Dokta Goje ya ce hukumar, tare da haɗin gwiwar Hukumar Kashe Gobara ta jihar, za su ɗauki matakan hana ƙone daji da kuma bin ƙa’idojin zubar da shara domin rage haɗuran gobara.
A gefe guda, Gwamna Mai Mala Buni ya umarci hukumar YOSEMA da ta tantance ɓarnar da gobarar ta yi, domin sanin irin taimakon da waɗanda lamarin ya shafa suke buƙata.
Gwamnan ya tabbatar wa waɗanda abin ya shafa cewa za a tallafa musu.
A halin yanzu, hukumomi na ci gaba da faɗakar da jama’a kan muhimmancin kiyaye dokokin kare gobara domin gujewa aukuwar irin wannan iftila’i a gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara gwamnati rasuwa shara yara
এছাড়াও পড়ুন:
HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a Zariya
Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), reshen Jihar Kaduna, ta ƙone fiye da tan 52,000 na miyagun ƙwayoyi a bainar jama’a a ƙauyen Karofi da ke Kufena, a kan tsohuwar hanyar Birnin Gwari da ke Zariya.
An gudanar da bikin ƙone kayan ne a wannan Alhamis ɗin, inda Birgediya Janar Buba Marwa (Rtd.), Shugaban NDLEA kuma Babban Jami’in Gudanarwa, ya jaddada cewa hukumar ta duƙufa domin kawar da barazanar miyagun ƙwayoyi daga cikin al’umma.
Ina girmama sojojin Nijeriya — Wike Bebejin Katsina, Alhaji Nuhu Yashe ya rasuYa bayyana cewa, “Miyagun ƙwayoyi suna lalata tarbiyyar matasa a hankali, ba tare da an farga ba. Kowace tan ɗaya da aka ƙone, an ceto rayukan mutane da dama daga halaka.”
Shugaban hukumar, wanda Mataimakin Daraktan Harkokin Miyagun ƙwayoyi, Suleiman Ningi, ya wakilta, ya yi gargadi ga masu safarar miyagun ƙwayoyi da su daina kasuwancin kayan haram, su koma safarar kayan halal, ko kuma su fuskanci hukunci mai tsanani.
Janar Marwa ya ce NDLEA na ci gaba da fatattakar manyan dillalan miyagun ƙwayoyi da ƙungiyoyin su, tare da ƙarfafa wayar da kai a kan illolin kayan laifi.
Ya yaba wa rundunar NDLEA ta Jihar Kaduna bisa ƙoƙarinta, tare da gode wa Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, saboda goyon bayan da yake bayarwa, ciki har da ba da motocin aiki da fili domin gina bariki ga hukumar.
Shugaban NDLEA ya roƙi iyaye, shugabannin al’umma da na addini, da su ƙara ƙaimi wajen wayar da kan mutane kan illar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi, yana mai cewa, “Yaƙin da ake yi da miyagun ƙwayoyi yaƙin ceto rayuka da makomar ƙasa ne.”
Kwamandan NDLEA na Jihar Kaduna, Mohammed Tukur, ya bayyana cewa bikin ƙone miyagun ƙwayoyi na nuna jajircewar hukumar wajen kare al’umma daga illolin sha da safarar su.
Ya ce wannan mataki shi ne “ƙarshe a jerin matakan aiwatar da doka”, domin tabbatar da cewa waɗannan ƙwayoyi masu haɗari sun ɓace gaba ɗaya daga hannun mutane, don hana su cutar da matasa ko ƙarfafa ayyukan laifi.
Kwamandan ya bayyana cewa miyagun ƙwayoyin da aka ƙone sun haɗa da Tramadol, Wiwi (Cannabis), da Hodar Iblis da an kiyasta darajar su za ta kai Naira biliyan biyar.
Ya bayyana cewa wannan gagarumar nasara ta samu ne sakamakon ƙoƙarin jami’an NDLEA tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro irin su sojoji, hukumar kwastam, DSS, da ‘yan sanda.
Ya ce, “Wannan aiki shaida ce ta gaskiya, riƙon amana, da ƙwarewar NDLEA. A yau, muna sake tabbatar da sakonmu cewa Jihar Kaduna ba mafakar masu safarar ko masu amfani da miyagun ƙwayoyi ba ce.”
Tukur ya jaddada biyayyarsu wajen dawo da zaman lafiya da kare makomar matasan jihar.
A nasa jawabin, Gwamna Uba Sani ya yaba wa NDLEA bisa ƙoƙarinta wajen ganin cewa an tsarkake Jihar Kaduna daga miyagun ƙwayoyi.
Gwamnan ya ce yawan ƙwayoyin da aka ƙone na nuna tsananin ƙoƙarin da ake yi wajen tabbatar da doka a jihar, tare da jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa dukkan hukumomin tsaro wajen yaƙi da laifuka da duk wata barazanar tsaron al’umma a jihar.