Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas
Published: 19th, March 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) a matsayin Mai Kula da Jihar Ribas.
An rantsar da shi ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Laraba.
Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin RibasNaɗin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Talata, bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin Jihar.
Bayan ayyana dokar ta-ɓacin, Tinubu ya sanar da cewa Vice Admiral Ibas ne zai jagoranci jihar na tsawon watanni shida.
Yayin jawabinsa, Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa dokar ta-ɓacin ba ta shafi ɓangaren shari’a ba, kuma kotuna za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta tanada.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia, Mohammed Haliru Arabo, na tsawon wata uku, kan rikicin shugabanci.
Shugaban Majalisar, Danladi Jatau, ne ya sanar da hakan a ranar Talata a Lafia, bayan Shugaban Kwamitin Majalisar kan Harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu, Musa Ibrahim Abubakar, ya gabatar da korafi kan rikicin mulki da ke faruwa a karamar hukumar.
Jatau ya ce matakin ya zama dole domin ba da damar gudanar da bincike kan yadda ake tafiyar da mulkin karamar hukumar, wanda ya ce yana shafar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
Ya bayyana cewa dakatarwar ta yi daidai da sashe na 7 da na 128 na kundin tsarin mulkin 1999 da aka yi wa kwaskwarima, wanda ya ba majalisa ikon sanya ido kan harkokin mulki.
Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a SakkwatoA cewarsa: “Domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Lafia, dole ne mu gudanar da bincike kan abin da ke faruwa. Bisa ikon da kundin tsarin mulki ya ba mu, shugaban karamar hukumar Lafia ya dakata na tsawon wata uku. Za a ci gaba da gudanar da harkokin karamar hukumar har sai an kammala bincike.”
Kwamitin harkokin kananan hukumomi da masarautu ya samu umarni da ya gudanar da binciken cikin wannan lokaci. A yayin dakatarwar, mataimakin shugaban karamar hukumar, Uba Arikya, zai rike ragamar mulki.
Tun da farko, Musa Ibrahim Abubakar ya gabatar da kudiri a matsayin gaggawa, inda ya nuna damuwa kan yadda aka dakatar da shugaban karamar hukumar na tsawon wata shida ba tare da bin ka’ida ba. Ya ce hakan ya saba wa kundin tsarin mulki, kuma yana haifar da rashin tabbas a siyasar yankin.
Ya jaddada bukatar majalisar jihar ta shiga tsakani domin tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin kudi da mulkin karamar hukumar.
Kwamitin ya kuma bukaci majalisar ta yi nazari sosai kan lamarin domin kawo karshen rashin tabbas da rikicin da ya kunno kai a Lafia.