Aminiya:
2025-07-11@09:44:15 GMT

Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas

Published: 19th, March 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) a matsayin Mai Kula da Jihar Ribas.

An rantsar da shi ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Laraba.

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas 

Naɗin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Talata, bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin Jihar.

Bayan ayyana dokar ta-ɓacin, Tinubu ya sanar da cewa Vice Admiral Ibas ne zai jagoranci jihar na tsawon watanni shida.

Yayin jawabinsa, Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa dokar ta-ɓacin ba ta shafi ɓangaren shari’a ba, kuma kotuna za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta tanada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Yahudawan Iran Ya Tuhumi Isra’ila Da Fakewa A Karkashin Addini

Shugaban yahudawan Iran Rabbi Younes Hamami Lalezar ya  ce, Isra’ila tana amfani da addini yahudanci domin cimma manufofinta, tana kuma bayyana Iran a matsayin wacce take fada da addinin yahudanci,alhali a cikin iran da akwai zaman lafiya tsakanin Mabiya dukkanin addinai.

Haka nan kuma ya ce, kiyayyar da Isra’ila take da shi akan Iran ne, yake sa take jinginawa Iran din kin jinin yahduawa,wanda aikin ‘yan sahayoniya ne su samar da rabuwar kawuna a tsakanin al’ummar Iran bisa addini da kuma kabila.

Isra’ila tana bayyana kanta a matsayin mai bai wa yahudawa kariya, sai dai  da dama daga cikin Mabiya addinin yahudanci, wadanda ba ‘yan sahayoniya ba, suna zarginta da amfani da addini saboda manufofi na siyasa.

Fiye da  shekaru  2,700, yahudawa suke rayuwa a cikin Iran,kuma suna da wuraren bautarsu da harkokinsu na yau da kullum ba tare da tsangwama ba.

Rabbi Younes Hamami Lalezar ya kuma ce: A Iran, yahudawa suna aiki, suna yin bautarsu, da rayuwa a ko’ina, suna da dakunansu na ibada -Synagogues- a cikin sauki da ‘yanci ba tare da wata kariya ta jami’an tsaro kamar yadda yake a cikin kasashen turai ba.

Haka nan kuma ya ce, yadda muke rayuwa ta girmama juna a tsakanin musulmi, yahudawa, da kiristoci, shi ne babban abinda yake bayyana hakikaninmu, don haka duk wani zargi na kin jinin yahudawa ba shi da madogara.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Yahudawan Iran Ya Tuhumi Isra’ila Da Fakewa A Karkashin Addini
  • Kotun ƙoli ta tabbatar da Okpebholo a matsayin gwamnan Edo
  • Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo a Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
  • Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — Hadimi
  • Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha
  • An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato
  • ACReSAL Ta Kaddamar da Kamfen  Kula Da Sauyin Yanayi A Makarantu
  • Gamayyar ‘Yan Adawa Sun Kaddamar ADC A Gombe  
  • Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa