Aminiya:
2025-12-07@12:51:26 GMT

Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas

Published: 19th, March 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) a matsayin Mai Kula da Jihar Ribas.

An rantsar da shi ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Laraba.

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas 

Naɗin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Talata, bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin Jihar.

Bayan ayyana dokar ta-ɓacin, Tinubu ya sanar da cewa Vice Admiral Ibas ne zai jagoranci jihar na tsawon watanni shida.

Yayin jawabinsa, Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa dokar ta-ɓacin ba ta shafi ɓangaren shari’a ba, kuma kotuna za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta tanada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200

Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Godswill Akpabio ya shigar da Sanata Natasha Akpoti ƙara a kotu kan zargin ɓata masa suna yana mai neman ta biya shi diyyar naira biliyan 200.

Sanata Natasha mai wakiltar jihar Kogi ta tabbatar da karɓar sammacin a shafukanta na sada zumunta, inda ta nuna jin daɗinta tana mai cewa ta samu damar bayyana hujjojinta kan zargin yunƙurin lalata da ta zarge shi da yi a baya.

“Yau 5 ga watan Disamban 2025, na karɓi sabon sammacin kotu kan ƙarar diyya ta naira biliyan 200 da Sanata Godswill Akpabio ya kai ni game da ɓata masa suna da zargin lalata,” a cewar Natasha.

“Na yi farin ciki da Sanata Akpabio ya taso da wannan batu saboda kwamatin ɗa’a na majalisa ya ƙi amincewa ya saurare ni kan batun sakamakon matar Akpabio ta shigar da ni ƙara a kotu.”

A watan Fabrairun 2025 ne Natasha ta zargi Akpabio da neman yin lalata da ita bayan rikicin da ya ɓarke a tsakaninsu, wanda ya kai ga dakatar da ita daga zaman majalisar na tsawon wata shida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC
  • Najeriya: Tinubu Ya Nada Wasu Karin Jakadu 65, Sanatoci Da Tsoffin Gwamnoni Na Daga Cikinsu
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya