Aminiya:
2025-12-13@16:05:29 GMT

Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas

Published: 19th, March 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) a matsayin Mai Kula da Jihar Ribas.

An rantsar da shi ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Laraba.

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas 

Naɗin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Talata, bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin Jihar.

Bayan ayyana dokar ta-ɓacin, Tinubu ya sanar da cewa Vice Admiral Ibas ne zai jagoranci jihar na tsawon watanni shida.

Yayin jawabinsa, Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa dokar ta-ɓacin ba ta shafi ɓangaren shari’a ba, kuma kotuna za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta tanada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Abubuwan Da Ba Ku Ji Ba Kan Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi December 13, 2025 Labarai Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani December 13, 2025 Manyan Labarai Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman December 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest