Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas
Published: 19th, March 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) a matsayin Mai Kula da Jihar Ribas.
An rantsar da shi ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Laraba.
Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin RibasNaɗin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Talata, bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin Jihar.
Bayan ayyana dokar ta-ɓacin, Tinubu ya sanar da cewa Vice Admiral Ibas ne zai jagoranci jihar na tsawon watanni shida.
Yayin jawabinsa, Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa dokar ta-ɓacin ba ta shafi ɓangaren shari’a ba, kuma kotuna za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta tanada.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa har yanzu yana nan daram a jam’iyyar PDP.
Ya yi wannan bayani ne a Abuja a ranar Juma’a yayin da yake mayar da martani kan ficewar wasu ’yan majalisar dokoki na Jihar Rivers daga PDP zuwa jam’iyyar APC.
Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15A ranar Juma’a, ‘yan majalisar Ribas guda 16, ciki har da Kakakin Majalisar, Martins Amaewhule, da suka sauya sheƙa zuwa APC.
Amaewhule, ya ce ya yanke shawarar komawa APC ne saboda rarrabuwar kai da aka samu a PDP.
Hakazalika, kakakin ya ce yana son ya yi aiki tare da Shugaba Bola Tinubu, bayan ya gano yana da kyakkyawan tsari na ciyar da ƙasar nan gaba.
Da yake magana da manema labarai bayan duba wasu ayyuka a Abuja, Wike, ya ce ’yan majalisun ba su tuntuɓe shi game da batun sauya sheƙarsu ba, amma ya ce suna da ’yancin zaɓen abin da suke so.
Ya ƙara da cewa ba duka ’yan majalisar ne suka fice daga PDP ba.
Ya ce, “Ni har yanzu ina PDP. Ba dukkaninsu ne suka fice daga jam’iyyar PDP ba. Ina ganin 16 ko 17 ne suka fice daga cikin 27. Har yanzu muna da kusan mutum 10, kuma za mu ci gaba da aiki tare da su.”
Wike, ya bayyana lamarin a matsayin abin baƙin ciki, amma ya ce kowa na da ’yancin zaɓen abin da yake so.
Ya ɗora alhakin ficewarsu kan rikicin cikin gida da PDP ke fama da shi, inda ya bayyana cewa kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya bai wa mutane damar barin jam’iyyar idan ta rabu gida biyu.
Ya ce tun da farko ya bai wa shugabancin PDP shawara su gyara jam’iyyar, tare da gargaɗin cewa idan ba a ɗauki mataki ba jam’iyyar za ta ci gaba da yin asara.
Wike, ya ƙara da cewa suna ci gaba da ƙoƙari domin sauran mambobin PDP su haɗa kai don yaƙar jam’iyyun adawa.