Aminiya:
2025-12-14@07:20:01 GMT

Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas

Published: 19th, March 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) a matsayin Mai Kula da Jihar Ribas.

An rantsar da shi ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Laraba.

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin Ribas 

Naɗin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Talata, bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin Jihar.

Bayan ayyana dokar ta-ɓacin, Tinubu ya sanar da cewa Vice Admiral Ibas ne zai jagoranci jihar na tsawon watanni shida.

Yayin jawabinsa, Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa dokar ta-ɓacin ba ta shafi ɓangaren shari’a ba, kuma kotuna za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta tanada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja

“Umarna ga jami’an tsaro har yanzu ita ce cewa dole ne a ceto dukkan daliban da sauran ‘yan Nijeriya da aka yi garkuwa da su a fadin kasar nan, a dawo da su gida cikin aminci. Dole ne mu tabbatar da an kirga duk wanda lamarin ya rutsa da shi.

“Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da aiki tare da Jihar Neja da sauran jihohi don tsare makarantu da kuma samar da ingantacciyar muhalli mai aminci da dacewa domin karatun ‘ya’yanmu.

“Daga yanzu, jami’an tsaro tare da gwamnonin jihohi dole su hana afkuwar garkuwa da mutane a nan gaba. Ya kamata yaranmu su daina zama abin hari ga mugayen ‘yan ta’adda da ke kokarin dakile iliminsu tare da jefa su da iyayensu cikin azaba marar misaltuwa.”

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba December 12, 2025 Manyan Labarai Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP December 12, 2025 Manyan Labarai Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa December 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — Turaki
  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest