Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas
Published: 19th, March 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) a matsayin Mai Kula da Jihar Ribas.
An rantsar da shi ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Laraba.
Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin RibasNaɗin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Talata, bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin Jihar.
Bayan ayyana dokar ta-ɓacin, Tinubu ya sanar da cewa Vice Admiral Ibas ne zai jagoranci jihar na tsawon watanni shida.
Yayin jawabinsa, Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa dokar ta-ɓacin ba ta shafi ɓangaren shari’a ba, kuma kotuna za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta tanada.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta ayyana dokar ta-baci a yankin, kwana biyu bayan yunkurin juyin mulki da bai yi nasara ba a kasar Jamhuriyar Benin.
Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya sanar da haka a yayin zaman majalisar tsaro ta hukumar karo na 55 a Abua.
Touray ya ce daukar matakin ya zama dole domin shawo kan barazanar da juyin mulki ke wa tsarin dimokuradiyya a yankin, wanda ke bukatar matakan zuba jari na gagagwa domin tabbatar da tsaron al’umma.
A yayin jawabinsa ga ministoci da manyan jami’an gwamnati da ke halartar taron, ya bayyana yadda yawaitar samun juyin mulki a Yammacin Afirka ke barazana ga tsaro da zaman lafiya a yankin.
Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato HOTUNA: Yadda dalibai 100 da aka sace a Neja suka dawoYa ce, “Babban barazana ga yankinmu sun haɗa da ci gaba da katsalandan na sojoji (kamar yadda aka gani kwanan nan a Guinea-Bissau da Jamhuriyar Benin); rashin bin ka’idojin sauyin mulki a Guinea inda shugaban soja ke ƙoƙarin zama farar hula; raguwar damar shiga zabe a ƙasashe da dama; ƙara karfin ’yan ta’adda, kungiyoyi masu laifi da ke dauke da makamai; da kuma matsin lamba na siyasar duniya da ke shafar diflomasiyya da haɗin kan ƙasashen mambobi.”
Touray ya jaddada cewa “zabe ya zama babban abin da ke tayar da rikici a cikin al’ummarmu.”
Ya kuma ambaci yunƙurin juyin mulki da aka yi kwanan nan da tattaunawa da ƙasashen AES (Burkina Faso, Mali da Nijar) da suka fice daga ECOWAS, yana mai nanata bukatar gaggawa ta haɗin gwiwar yankin wajen yaki da ta’addanci da laifukan da ke ketare iyaka.
Ya bayyana lamarin a matsayin abin da bai taɓa faruwa ba, yana gargadi da cewa, “Idan aka dubi wannan hali, ya dace mu bayyana cewa al’ummarmu tana cikin yanayin gaggawa.”
Touray ya bukaci a riƙa yin taron Majalisar Sulhu da Tsaro akai-akai a shekara mai zuwa, yana mai cewa ECOWAS dole ta “haɗa ƙarfi da ƙarfi don fuskantar barazanar ta’addanci da ’yan fashi, waɗanda ba sa mutunta iyakokin ƙasashe.”
Ya kuma bayyana muhimman wuraren da ministoci za su riƙa kula da su, ciki har da rikicin Guinea-Bissau, tafiyar da sauyin mulki, magance ƙara yawaitar cire mutane daga siyasa, da kuma kare haɗin kan yankin daga matsin lamba na waje.