Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas
Published: 19th, March 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya) a matsayin Mai Kula da Jihar Ribas.
An rantsar da shi ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Laraba.
Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya fice daga gidan gwamnatin RibasNaɗin ya biyo bayan ayyana dokar ta-baci a Jihar Ribas da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Talata, bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin Jihar.
Bayan ayyana dokar ta-ɓacin, Tinubu ya sanar da cewa Vice Admiral Ibas ne zai jagoranci jihar na tsawon watanni shida.
Yayin jawabinsa, Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa dokar ta-ɓacin ba ta shafi ɓangaren shari’a ba, kuma kotuna za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda doka ta tanada.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan jaridar Daily Trust da Trust TV sun lashe kyautar binciken ƙwaƙwaf ta Wole Soyinka ta bana
Jaridar Daily Trust da gidan talabijin na Trust TV, dukkansu mallakar kamfanin Media Trust, a bana ma sun sake yin fice bayan ’yan jaridansu suka lashe kyautar binciken kwakwaf ta Wole Soyinka ta bana.
’Yan jaridar na Daily Trust da Trust TV, Afeez Hanafi da Muslim Muhammad Yusuf, sun lashe gasar ne a matsayin zakaru a rukunin rahoton jarida da kuma na talabijin mafi daraja a bana a Najeriya.
Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a SakkwatoHanafi ya lashe rukuni na rubutu bisa labarinsa mai taken: “Bincike: Dan jarida ya samu ayyuka biyu da takardun bogi na Oluwole.”
Wanda ya zo na biyu da na uku a rukunin na rubutu su ne Kingsley Jeremiah da Ann Godwin, dukkansu daga jaridar The Guardian.
Sai dai kamar yadda aka saba, babu wanda ya lashe kyautar a rukuni na rediyo, kuma babu wanda ya fito a matsayin na biyu ko na uku.
A rukuni na yanar gizo, Theophilus Adeokun na National Record ya lashe gaba ɗaya da labarinsa mai taken: “Dangote, a neman makamashi mai arha, yana zubar da guba cikin kogunan Binuwai.”
Wanda ya yi na biyu shi ne Kunle Adebajo daga HumAngle, yayin da Isah Ismaila, shi ma daga HumAngle din ya zo na uku.
A rukunin hoto kuwa, Elliot Ovadje na jaridar Punch ya fito a matsayin zakara, sannan shi ɗin ne ya sake fitowa a matsayin na biyu da na uku.
A bangaren girmamawa, tsohon Alkalin Kotun Ƙoli, Justice Ayo Salami, ya samu kyautar mai rajin kare hakkin dan Adam, yayin da fitaccen marubuci kuma mawaki, Odia Ofeimun, ya samu kyautar kwarewa a aikin jarida.
Tun kafin gabatar da kyaututtuka, shugabar alkalai ta shekarar 2025, Abigail Ogwezzy‑Ndisika, a jawabinta ta ce an samu shigar da rubuce‑rubuce 180, amma aka tace su zuwa 129.
Ta jaddada abubuwan da aka yi amfani da su wajen tantance kowanne rubutu da suka hada da jarumta, zurfi, daidaito, tasiri da kuma jajircewa ga muradun jama’a.
“Mun yi wannan aikin ne daban‑daban kuma ba tare da katsalandan ba, ta amfani da wasu ka’idoji da suka shafi rufe batutuwan cin hanci, take hakkin ɗan adam, laifuka da ayyukan ɓoye, da kuma kyawawan hanyoyin binciken jarida,” in ji ta.
Marubucin da aka saka wa gasar sunansa kuma mai lambar yabo ta Nobel, Wole Soyinka, ya taya dukkan wadanda suka samu kyautar murna, yana mai gargadin kada su yi sakaci.
“Wasu daga cikin jaruman da za su ceci wannan ƙasa za a same su a cikin kafafen yada labarai. Amma a lokaci guda, dole ne in roƙi kafafen yada labarai su yi dada takatsantsan, su yi bincike mai zurfi kan abin da suke wallafawa. Akwai labarai masu yawa da ake wallafawa da ba daidai ba ne,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga jaridun da su inganta rahotanninsu, yana nuna damuwa kan yawan labaran karyar da ke yawo a kafafen sada zumunta.