Aminiya:
2025-06-16@01:58:20 GMT

Ɗan Afirka da yake da ‘ya’ya 104 da jikoki 144

Published: 19th, March 2025 GMT

Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga, wani mutum ne daga wani karamin kauye a Tanzaniya, wanda yake da iyali na musamman.

Ya auri mata 16, yana da ’ya’ya sama da 100 da jikoki 144.

A kwanakin nan, maza da yawa suna ta kokarin samun iyali da neman haihuwa, duk da ana kallon karuwar iyali kamar karin matsin rayuwa ne mai yawa.

DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna An shiga zaman ɗar-ɗar yayin da sojoji suka mamaye Gidan Gwamnatin Ribas

Kula da yara sama da biyu ko uku abu ne da ba za a yi tsammani ba ga galibin matasa, amma kuma akwai maza irin su Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga wadanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen fadada iyalansu gwargwadon iko.

Mutumin ɗan asalin wani ƙaramin ƙauye ne da ke Njombe a kasar Tanzaniya, a halin yanzu yana da mata 16, ‘ya’ya 104 da jikoki 144.

Gidansa kamar wani dan karamin kauye ne, inda kowace mace daga cikin matansa take da bangarenta kuma iyalansa suna yawo a ko’ina, suna gudanar da sana’o’i, suna kula da dimbin yara.

A wata hira da ya yi da Afrimax kwanan nan, Ernesto Kapinga ya ce, ya fara fadada iyalinsa ne bisa bukatar mahaifinsa.

Ya auri matarsa ta farko a shekara ta 1961, kuma ya haifi da na farko bayan shekara guda, amma mahaifinsa ya gaya masa cewa, mace daya ba ta isa ba.

Sai ya ce zai ba shi sadaki idan ya amince ya auri karin mata don ya samu haihuwar yara da yawa.

“Danginmu ba su da yawa, ina so ka fadada su,” mahaifin Kapinga ya fada masa, kuma ya amince da hakan.

Mahaifinsa ya biya sadakin matansa biyar na farko, amma bai tsaya nan ba. A ƙarshe Ernesto ya auri mata 20.

Wasu sun zabi barinsa a wani lokaci, wasu kuma sun rasu, amma yau yana zaune da mata 16, bakwai daga cikinsu masu kananan shekaru ne.

Matan Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga sun bayyana cewa, ya kasance miji na gari.

Ɗaya daga cikin matansa ta bayyana wa ’yar’uwarsa irin kyakkyawar rayuwar da take yi tare da shi, don haka suka yanke shawarar zama da shi.

“A nan, kowa yana da rawar da yake takawa,” in ji magidancin.

“Kowace mace tana da gidanta da kicin dinta, babu gasa a tsakaninsu.

“Kowacce ta san wurinta, tare muke noma, muna ci tare, muna aiki tare .

“Wannan ba gida ba ne kawai, tsari ne da ake bi kuma yana aiki.

“To ta yaya mutum zai samar da daruruwan daruwan mutane abincin da za su ci?.

To a fili yake cewa, dukakan iyali suna dogara ne da aikinsu don samun abinci, kuma sun dogara kacokan ga amfanin gonakinsu da dabbobinsu wajen samun abinci.

Suna shuka masara da wake da rogo da ayaba, kuma abin da ya yi rara, sukan yi kasuwancinsa.

“Mutane suna tunanin ina sarrafa komai,” in ji Kapinga.

“Amma gaskiyar magana ita ce, matana suna hada kan wannan iyali, ni kawai ina yi musu jagoranci ne.”

Matan sun bayyana cewa, a koyaushe suna bayyana matsalolinsu kuma ba sa barin fushi ya yi barazana ga hadin kan gida.

Idan ba za su iya daidaita al’amura a tsakaninsu ba, sai su kawo al’amura ga Ernesto kuma ya saurare su, ba ya goyon bayan wani bangare, amma yana ba su shawara kawai.

A bayyane yake, wannan tsarin iyalin yana aiki daidai ya zuwa yanzu.

Wani abin sha’awa shi ne, Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga ya yarda cewa, a wasu lokuta yakan manta sunayen ‘ya’yansa da jikokinsa, yana mai cewa yakan tuna sunayensu 50 daga cikinsu. Ya ce yakan tuna sauran idan ya ga fuskokinsu.

Iyalan Kapinga sun kasance babban dangin da ya fi girma, amma ya rasa yara 40 sakamakon rashin lafiya da hadura.

Yana bakin ciki idan ya tuna da su, amma ya ci gaba da rayuwarsa don yana da ‘ya’ya da yawa a raye wadanda ke bukatar kulawarsa koyaushe.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

  Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa

Na’urorin kakkabo jiragen sama na Iran sun kakkabo jirgin sama na HKI samfurin F-35  a yammacin kasar, wanda shi ne karo na uku a cikin sa’oi 24.

Kamfanin dillancin labarun Tasnim ya nakalto majiyar tsaro na cewa; dakarun kare samaniyar jamhuriyar musulunci sun harbo jirgin sama samfurin F-35,kuma matukinsa ya fito ta hanyar amfani da lemar ceto.

 Bayan wani lokaci daga faduwar jrigin da kuma fitowar matukinsa daga ciki, sojojin kasa na jamhuriyar musulunci ta Iran sun kama shi.

A jiya Juma’a ma dai daakrun kare sararin samaniyar jamhuriyar musulunci ta Iran, sun kakkabo jiragen saman na ‘yan sahayoniya wadanda kirar Amurka ne, kuma daya daga cikin jiragen yakin da take alfahari da su.

Shi dai jirgin yakin na Amurka samfurin F-35 yana da layar zana, kuma da wuya na’urar hangen nesa-Radar- ta iya tsinkayo shi. Kudin kowane daya daga cikin wadannan jiragen shi ne dalar Amurka miliyan 100.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6