Ɗan Afirka da yake da ‘ya’ya 104 da jikoki 144
Published: 19th, March 2025 GMT
Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga, wani mutum ne daga wani karamin kauye a Tanzaniya, wanda yake da iyali na musamman.
Ya auri mata 16, yana da ’ya’ya sama da 100 da jikoki 144.
A kwanakin nan, maza da yawa suna ta kokarin samun iyali da neman haihuwa, duk da ana kallon karuwar iyali kamar karin matsin rayuwa ne mai yawa.
Kula da yara sama da biyu ko uku abu ne da ba za a yi tsammani ba ga galibin matasa, amma kuma akwai maza irin su Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga wadanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen fadada iyalansu gwargwadon iko.
Mutumin ɗan asalin wani ƙaramin ƙauye ne da ke Njombe a kasar Tanzaniya, a halin yanzu yana da mata 16, ‘ya’ya 104 da jikoki 144.
Gidansa kamar wani dan karamin kauye ne, inda kowace mace daga cikin matansa take da bangarenta kuma iyalansa suna yawo a ko’ina, suna gudanar da sana’o’i, suna kula da dimbin yara.
A wata hira da ya yi da Afrimax kwanan nan, Ernesto Kapinga ya ce, ya fara fadada iyalinsa ne bisa bukatar mahaifinsa.
Ya auri matarsa ta farko a shekara ta 1961, kuma ya haifi da na farko bayan shekara guda, amma mahaifinsa ya gaya masa cewa, mace daya ba ta isa ba.
Sai ya ce zai ba shi sadaki idan ya amince ya auri karin mata don ya samu haihuwar yara da yawa.
“Danginmu ba su da yawa, ina so ka fadada su,” mahaifin Kapinga ya fada masa, kuma ya amince da hakan.
Mahaifinsa ya biya sadakin matansa biyar na farko, amma bai tsaya nan ba. A ƙarshe Ernesto ya auri mata 20.
Wasu sun zabi barinsa a wani lokaci, wasu kuma sun rasu, amma yau yana zaune da mata 16, bakwai daga cikinsu masu kananan shekaru ne.
Matan Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga sun bayyana cewa, ya kasance miji na gari.
Ɗaya daga cikin matansa ta bayyana wa ’yar’uwarsa irin kyakkyawar rayuwar da take yi tare da shi, don haka suka yanke shawarar zama da shi.
“A nan, kowa yana da rawar da yake takawa,” in ji magidancin.
“Kowace mace tana da gidanta da kicin dinta, babu gasa a tsakaninsu.
“Kowacce ta san wurinta, tare muke noma, muna ci tare, muna aiki tare .
“Wannan ba gida ba ne kawai, tsari ne da ake bi kuma yana aiki.
“To ta yaya mutum zai samar da daruruwan daruwan mutane abincin da za su ci?.
To a fili yake cewa, dukakan iyali suna dogara ne da aikinsu don samun abinci, kuma sun dogara kacokan ga amfanin gonakinsu da dabbobinsu wajen samun abinci.
Suna shuka masara da wake da rogo da ayaba, kuma abin da ya yi rara, sukan yi kasuwancinsa.
“Mutane suna tunanin ina sarrafa komai,” in ji Kapinga.
“Amma gaskiyar magana ita ce, matana suna hada kan wannan iyali, ni kawai ina yi musu jagoranci ne.”
Matan sun bayyana cewa, a koyaushe suna bayyana matsalolinsu kuma ba sa barin fushi ya yi barazana ga hadin kan gida.
Idan ba za su iya daidaita al’amura a tsakaninsu ba, sai su kawo al’amura ga Ernesto kuma ya saurare su, ba ya goyon bayan wani bangare, amma yana ba su shawara kawai.
A bayyane yake, wannan tsarin iyalin yana aiki daidai ya zuwa yanzu.
Wani abin sha’awa shi ne, Mzee Ernesto Muinuchi Kapinga ya yarda cewa, a wasu lokuta yakan manta sunayen ‘ya’yansa da jikokinsa, yana mai cewa yakan tuna sunayensu 50 daga cikinsu. Ya ce yakan tuna sauran idan ya ga fuskokinsu.
Iyalan Kapinga sun kasance babban dangin da ya fi girma, amma ya rasa yara 40 sakamakon rashin lafiya da hadura.
Yana bakin ciki idan ya tuna da su, amma ya ci gaba da rayuwarsa don yana da ‘ya’ya da yawa a raye wadanda ke bukatar kulawarsa koyaushe.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
Wani abin fashewa da ake zargin bam ne ya kashe aƙalla mutum 26, ciki har da mata da yara a kan hanyar Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a lokacin da motoci suka tayar da bama-baman da aka ɗana a gefen hanyar, da ya rutsa da maza 16 da mata huɗu da ƙananan yara guda shida.
Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47 An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalMajiyoyi, ciki har da wani babba soja, sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu da harin na baya bayan da safiyar ranar Talata.
Sun bayyana cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su suna kan hanyarsu ta tafiya Gamboru Ngala ne daga Rann lokacin da suka isa inda ‘yan ta’addan Boko Haram suka ɗana bam ɗin.
Bayanai sun ce baya ga mutum 26 da suka mutu, ƙarin mutum uku sun ji munanan raunuka.
“Mun tura wasu masu ba da agajin gaggawa inda lamarin ya auku domin kwashe mutane tare da tabbatar da tsaron sauran fararen-hula a wurin,” kamar yadda wata majiyar sojin da ba ta yarda a bayyana sunanta ba ta shaida wa Anadolu.
Ali Abass, wani ganau wanda ke tafiya a kan hanyar a lokacin da lamarin ya auku, ya ce sojojin da ‘yan sa-kai sun kai waɗanda suka jikkata wani asibiti. Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin ‘yan’uwansa na cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Harin yana zuwa ne yayin da hare-hare ke ƙara ƙaruwa a yankin Tafkin Chadi, inda ‘yan ta’addan Boko Haram ke ƙara ƙaddamar da hare-haren bama-bamai da kwanton-ɓauna kan motocin fararen-hula da na sojoji.
An ba da rahoton hare-hare irin wannan a ranakun 21 ga watan Maris da 12 ga watan Afrilu. Kawo safiyar ranar Talata dai, jami’an tsaro a Borno ba su fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.