Aminiya:
2025-09-17@23:26:35 GMT

An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Yobe

Published: 8th, July 2025 GMT

Gwamna Mai Mala Buni, ya ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutane 48,000 domin jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ƙara ƙarfafa matakan kiwon lafiya a matakin farko a fadin Jihar Yobe.

Buni ya bayyana shirin fara samar da daidaito a bangaren kiwon lafiya wanda zai samar da inshorar lafiya ga mata masu rauni da yara ‘yan kasa da shekaru biyar sama da 38,000 a fadin jihar.

Dalilin da matan karkara a Kano suka fi son haihuwa a gida Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a Zariya

Gwamnan ya bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba yayin da ya kaddamar da wasu sabbin tsare-tsare da nufin fadada harkokin kiwon lafiya, musamman ga marasa galihu.

Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin jawabinsa a wajen babban taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Damaturu, wanda ya samu halartar sarakunan gargajiya da malaman addini, abokan hulda, ma’aikatan lafiya da manyan jami’an hukumar gudanarwa a bangaren samar da kiwon lafiya a matakin farko da kuma kungiyoyin farar hula.

Gwamna Buni ya bayyana manufarsa ta samar da lafiya mai rahusa a matsayin ginshikin ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin al’umma.

Ya amince da goyon bayan gwamnatin tarayya da abokan hulda da suka hada da Gidauniyar Bill and Melinda Gates, Aliko Dangote Foundation, UNICEF, da WHO da dai sauransu.

Gwamnan ya jaddada kudirin jihar na samar da kiwon lafiya, inda ya ba da misali da kafa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 142, samar da kayan aiki da magunguna, da daukar kwararrun ma’aikatan kiwon lafiya sama da 2,000 a fadin Jihar.

Ya bayyana irin nasarorin da jihar ta samu ciki har da fitowar ta a matsayin zakara ta shekarar 2024 a bangaren samar da kiwon lafiya a matakin farko a fadin kasar nan ta Champion leadership for Primary Health Care PHC  2024.

Ya kuma yi tsokaci kan kafa Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Jihar Yobe (YSCHMA) da Hukumar Kula da Magunguna ta Jihar Yobe (YODMA) don magance kuɗaɗen kula da lafiya da samar da magunguna.

Kazalika, ya bukaci sarakunan gargajiya da su ba da goyon baya tare da bayar da gudunmawa wajen karfafa ayyukan kiwon lafiya a matakin farko a yankunansu.

Gwamnan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su lura da batutuwan da aka tattauna a taron tare da magance kura-kuran da ake da su a yankunansu da kuma wuraren gudanar da ayyukansu domin kara inganta harkar kiwon lafiya a matakin farko a Jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: inshorar lafiya Jihar Yobe Kiwon Lafiya kiwon lafiya a matakin farko a

এছাড়াও পড়ুন:

Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare

Fitattun dalibai akalla 12 ne  daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare  a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).

A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.

Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.

A cewarsa, an zabo daliban 12 ne  sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.

Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.

“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.

Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.

A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.

Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar