An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Yobe
Published: 8th, July 2025 GMT
Gwamna Mai Mala Buni, ya ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutane 48,000 domin jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ƙara ƙarfafa matakan kiwon lafiya a matakin farko a fadin Jihar Yobe.
Buni ya bayyana shirin fara samar da daidaito a bangaren kiwon lafiya wanda zai samar da inshorar lafiya ga mata masu rauni da yara ‘yan kasa da shekaru biyar sama da 38,000 a fadin jihar.
Gwamnan ya bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba yayin da ya kaddamar da wasu sabbin tsare-tsare da nufin fadada harkokin kiwon lafiya, musamman ga marasa galihu.
Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin jawabinsa a wajen babban taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Damaturu, wanda ya samu halartar sarakunan gargajiya da malaman addini, abokan hulda, ma’aikatan lafiya da manyan jami’an hukumar gudanarwa a bangaren samar da kiwon lafiya a matakin farko da kuma kungiyoyin farar hula.
Gwamna Buni ya bayyana manufarsa ta samar da lafiya mai rahusa a matsayin ginshikin ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin al’umma.
Ya amince da goyon bayan gwamnatin tarayya da abokan hulda da suka hada da Gidauniyar Bill and Melinda Gates, Aliko Dangote Foundation, UNICEF, da WHO da dai sauransu.
Gwamnan ya jaddada kudirin jihar na samar da kiwon lafiya, inda ya ba da misali da kafa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 142, samar da kayan aiki da magunguna, da daukar kwararrun ma’aikatan kiwon lafiya sama da 2,000 a fadin Jihar.
Ya bayyana irin nasarorin da jihar ta samu ciki har da fitowar ta a matsayin zakara ta shekarar 2024 a bangaren samar da kiwon lafiya a matakin farko a fadin kasar nan ta Champion leadership for Primary Health Care PHC 2024.
Ya kuma yi tsokaci kan kafa Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Jihar Yobe (YSCHMA) da Hukumar Kula da Magunguna ta Jihar Yobe (YODMA) don magance kuɗaɗen kula da lafiya da samar da magunguna.
Kazalika, ya bukaci sarakunan gargajiya da su ba da goyon baya tare da bayar da gudunmawa wajen karfafa ayyukan kiwon lafiya a matakin farko a yankunansu.
Gwamnan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su lura da batutuwan da aka tattauna a taron tare da magance kura-kuran da ake da su a yankunansu da kuma wuraren gudanar da ayyukansu domin kara inganta harkar kiwon lafiya a matakin farko a Jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: inshorar lafiya Jihar Yobe Kiwon Lafiya kiwon lafiya a matakin farko a
এছাড়াও পড়ুন:
An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya ce gwamnatin tarayya za ta gudanar da aikin samar da wutar lantarki ga jami’ar tarayya ta Kashere da ke jihar Gombe domin tabbatar da samar da isasshen wutar lantarki domin inganta harkokin ilimi.
Shugaban ya bayyana hakan ne a wajen taron hadaka karo na uku na jami’ar tarayya ta Kashere da ke karamar hukumar Akko a jihar Gombe.
Shugaba Bola Tinubu ya kuma bayyana cewa ma’aikatar albarkatun ruwa ta tarayya za ta fara aikin gina madatsar ruwa a kogin Kashere domin tallafa wa shirin koyar da aikin gona na jami’ar da inganta samar da ruwa ga al’ummomin da ke kewaye.
Ya jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta samar da ingantaccen ilimi ta hanyar shiga tsakani na asusun bayar da lamuni na ilimi na kasa (NELFUND).
Ya kuma bukaci jami’o’in Najeriya da su binciko tsarin samar da kudade mai ɗorewa yana mai cewa dole ne zamanin dogaro da kai ga ayyukan gwamnati ya ba da dama ga sabbin hanyoyin samar da kudaden shiga, da haɗin gwiwar dabarun bunƙasa dukiyoyi da kuma asusun bayar da tallafi na gari.
A jawabinsa na maraba, Shugaban jami’ar tarayya ta Kashere, farfesa Umar Pate, ya bayyana cewa martabar jami’ar tana karuwa ne saboda shekaru masu yawa na tsare-tsare da hangen nesa na Hukumar gudanarwar jami’ar.
Ya ce cibiyar ta ba da fifikon dacewa da ilimi ta hanyar ingantaccen ayyukan bincike da haɗin gwiwa tare da sahihan cibiyoyi na ƙasa da ƙasa.
HUDU Shehu