HausaTv:
2025-05-22@10:10:24 GMT

Kamfanonin jiragen sama sun tsawaita dakatar da zirga-zirgar zuwa Isra’ila

Published: 22nd, May 2025 GMT

Manyan kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa da dama sun tsawaita dakatar da zirga-zirgar jiragensu zuwa yankunan Falasdinawa da Isra’ila ta mamaye, a daidai lokacin da kasar Yemen ta sha alwashin daukar mataki kan kasar.

Kamfanin jirgin sama na Air France ya sanar cewa, bayan dakatarwar da aka yi na tsawon watanni, zai ci gaba da dage zirga-zirgar jiragensa zuwa yankunan Falasdinu da aka mamaye har zuwa ranar 24 ga watan Mayu.

Da farko Air France ya yi niyyar dawo da zirga-zirgar jirage a wannan makon, amma ya zabi karin jinkirta hakan.

Kamfanin Lufthansa da SWISS, Austrian Airlines, Brussels Airlines da Eurowings, su ma sun tsawaita dakatar da zirga-zirgar jiragensu zuwa yankunan da aka mamaye.

“Saboda halin da ake ciki yanzu, kamfanin Lufthansa zai dakatar da zirga-zirgar jiragensa zuwa Tel Aviv har zuwa ranar Lahadi 8 ga watan Yuni,” maimakon ranar 25 ga Mayu.

Kamfanin jiragen sama na Burtaniya EasyJet, wanda ya hada da EasyJet UK, EasyJet Switzerland da EasyJet Turai, shi ma ya dage ci gaba da zirga-zirgar jiragensa har zuwa akalla 30 ga watan Yuni.

Sauran kamfanonin jiragen sama na Turai su ma sun bi sawu, suna tsawaita dakatarwa ko soke tashin jirage.

Yeman dai ta sha kai hare-hare a filin jirgin saman Ben Gurion, mafi muhimmanci ga Isra’ila, da makamai masu linzami domin nuna goyan baya ga al’ummar Gaza da shan ukuba daga Isra’ila.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: dakatar da zirga zirgar tsawaita dakatar jiragen sama

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’ar Ilorin Ta Yi Bikin Ranar Al’adu

Daraktan Cibiyar Nazarin Al’adu da Ƙirƙirar Ƙirƙira, Jami’ar Ilorin, Farfesa Olutoyin Ogunade, ya ba da shawarar a bayyana kowace Litinin a matsayin Ranar Al’adu a harabar jami’ar.

 

Farfesa Ogunade ya bayyana hakan ne a lokacin babban bikin ranar al’adu na jami’ar, mai taken “fayyace kyawawan Al’adun mu” a Ilorin.

 

Ya ce wannan shiri zai karfafa wa ma’aikata da dalibai kwarin gwiwar sanya tufafin nasu na asali.

 

A cewarsa, “Tsarin al’adu ba salo ba ne kawai, abin tunawa ne na kakanni da aka tsara.

 

Farfesa Ogunade ya bayyana cewa yin suturar al’ada ita ce bayyana ainihi, tunawa da kuma tsayayya da mamayar al’adu”, ya kara da cewa irin wadannan ayyukan sun tabbatar da tasiri a wasu wuraren ilimi.

 

Ya yi kira da a kaddamar da shirin sanya tufafin al’adu a karkashin cibiyar domin magance matsalolin da ake samu.

 

 

Farfesa Ogunade ya lura cewa aikin, zai ƙunshi haɗin gwiwa tare da masu zanen gida, tsofaffin ɗalibai, da masu tallafawa don yin kayan gargajiya cikin sauƙi da araha a fadin jami’ar.

 

Ya bayyana cewa dole ne mu fitar da kanmu daga sauran ƙa’idodin Yammacin Turai waɗanda har yanzu suke gaya mana yadda ake yin sutura, lura da cewa bai kamata a sanya tufafin al’adu don nunawa kawai ba amma a matsayin kayyyakin yau da kullun.

 

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Shugaban jami’ar Ilorin, Farfesa Wahab Egbewole SAN, wanda mataimakin shugaban jami’ar sashen gudanarwa, Farfesa Adegboyega Fawole ya wakilta, ya bayyana cewa bikin ranar al’adu ya sake jaddada sadaukarwar jami’ar wajen inganta ilimin al’adu, hada kai, da kuma alfahari.

 

Mataimakin shugaban, ya lura cewa al’adunmu daban-daban suna nuna abin da muke, gadonmu da imani, wanda ya haɗa mu a matsayin mutane ɗaya.

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’ar Ilorin Ta Yi Bikin Ranar Al’adu
  • Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma
  • Gaza : Birtaniya ta dakatar da tattaunawar cinikayya da Isra’ila
  • Queen Zeeshaq za ta shiga daga ciki
  • Tsohuwar mawaƙiyar Hausa Hip-hop za ta yi aure
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22
  • Yeman ta yi barazanar killace tashar jiragen ruwan Haifa ta Isra’ila
  • Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza
  • An cimma matsaya kan dakatar da haska fina-finai 22 a Kano