Aminiya:
2025-09-17@22:08:05 GMT

Gobarar rumbum makamai a Borno: Abin da ya kamata a yi

Published: 2nd, May 2025 GMT

Masana harkokin tsaro sun ja hankalin hukumomi su ɗauki matakan da suka dace, lura da abin da ke iya biyo bayan gobarar ma’ajiyar makamai a babban Barikin Sojoji na Giwa da ke Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Sun bayyana damuwa game da mummunan abin da ke iya biyo baya ta fuskoki daban-daban, tare da bayar da shawarar matakan da ya kamata a ɗauka domin daƙile ayyukan miyagu da ke iya ƙoƙarin cin gajiyar yanayin a matsayin wata dama ta aikata mugun laifi ko ta’addanci.

Damuwar ƙwararru kan ƙarsashi da karfin sojoji

Wani ƙwararre kan harkokin tsaro, Kabiru Adamu, ya ce illar wannan lamari ta wuce ɓarnar zahiri da kuma yiwuwar asarar rayuka.

Ya ce, “Lalacewar makamai, harsasai, da sauran muhimman kayan aikin soja a barikin babban asarar kayan aiki ne da ke iya shafar shirye-shiryen ayyukan soji kai tsaye da ma sauran ayyukan tsaro a yankin Arewa maso Gabas da kuma yankin Tafkin Chadi.”

Kabiru Adamu ya ƙara cewa hanyoyin samar da kayan aikin soji — waɗanda tuni suke cikin matsi saboda yanayin aiki mai wahala — za su iya samun ƙarin cikas, wanda zai sa gyarawa ya zama da wahala.

Kabiru Adamu ya kuma yi gargaɗi game da irin tasirin da lamarin zai iya yi a tunani da ƙwarin gwiwar sojoji. Ya ce, “Lamarin na iya raunana jin tsaro da kwanciyar hankalinsu, musamman tunda suna zaune ne a cikin barikin.

“Wannan na iya kawo raguwar ƙwarin gwiwa da ƙaruwar damuwa,da kuma raunana ruhin faɗa. Zai kuma iya jawo rashin amincewa da ka’idojin tsaro da kuma shugabannin da ke da alhakin tabbatar da su,” in ji shi.

Ya ƙara jaddada cewa cikas na wucin gadi da lamarin ya haifar na iya kawo tsaiko ga ayyukan rundunar Operation Hadin Kai har sai an maye gurbin kayan aiki da suka salwanta.

“Dangane da ƙoƙarin yaki da ta’addanci, wannan lamarin na iya zama koma baya. Yana iya karfafa ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP su ƙara kai wa sojoji da fararen hula hare-hare. Suna iya ganin lamarin a matsayin alamar rauni ko wata dama,” in ji shi.

Kabiru Adamu ya kuma nuna haɗarin raguwar amincewar jama’a, yana mai cewa “Ga fararen hula a Maiduguri, waɗanda tuni suke fuskantar barazanar ta’addanci koyaushe, abin da ya faru a Barikin Giwa na iya kawo fargaba game da tsaro gaba ɗaya da kuma rage sakin jiki da ikon sojoji na kare su — wanda zai iya shafar bayanan sirri da ake samu daga al’ummar yankin.”

Masanin ya kuma lura da  yiwuwar amfani da lamarin wajen yada farfaganda abokan gaba.

“Ƙungiyoyi kamar Boko Haram da ISWAP na iya nuna shi — ba tare da la’akari da ainihin dalilin ba — a matsayin nasara ko kuma wani aikin ikon Allah, su yi amfani da shi don ƙarfafa ɗaukar sabbin mayaƙa, da ƙarfafa ƙwarin gwiwa, da kuma rage amincewar jama’a ga gwamnati da jami’an tsaro.”

Don haka ya ce, “Dole ne sojojin su magance sakamakon lamarin cikin gaskiya da gaggawa. Karfafa ka’idojin tsaro da samar da ingantacciyar sadarwa suna da matuƙar muhimmanci wajen dawo da amincewa. Rashin yin hakan na iya ƙarfafa matsayin ’yan ta’adda da kuma tsawaita rikicin.”

Mun ɗauka harin ’yan ta’adda ne — Mazauna

Manyan fashe-fashe da ƙarar harbe-harbe da tartsatsin wuta da kuma hayaki da ke tashi sama, sakamakon gobarar ma’aajiyar makaman sun firgita mazauna unguwannin Polo, Fori, GRA, Unimaid, da sauran wurare, inda fita kan tituna, saboda fargabar yiwuwar harin Boko Haram.

Wani mazaunin gari, Adamu Yusuf, ya ce fashewar farko ta faru ne da tsakar dare, sai kuma harbe-harbe da suka biyo baya waɗanda suka kara musu tsoro.

Ya ce, “Mun yi magana da wani tsohon soja wanda ya kira abokin aikinsa a barikin, ya tabbatar da cewa gobara ce ta tashi a ma’ajiyar makamai. Amma karar hare-haren da ya biyo baya ya sa mana shakku.”

Kyari Bulama, wani makwabcin barikin, ya ce ƙarar fashewar da habe-harben ne suka tashe shi daga barci. Ya ce, “Mun zaci harin Boko Haram ne, muka yi ta guje-guje a gidan. Abin ya fi ban tsoro da na fito fita waje. Kusan kowa sun fito kan tituna, motoci da Keke NAPEP na guje-gujen barin yankin.”

A Jami’ar Maiduguri, ɗaruruwan ɗalibai sun gudu daga ɗakunansu na kwana suka koma cikin gari don guje wa yiwuwar harin ’yan ta’adda.

Wani dalibi ya ce, “Fashewar ta yi matuƙar ƙarfi, kuma kamar tana ƙara kusantowa. Mun fito da gaggawa daga ɗakunan kwananmu, amma jami’an tsaro ba su iya gaya mana abin da ke faruwa ba. Daga ƙarshe, mun samu labarin cewa ma’ajiyar makaman sojoji ne ta yi gobara.”

Aisami Lawan, wani mazaunin unguwar Polo, ya ce lamarin ya tuno musu da wani harin da ya faru a baya.

Ya ce, “Akwai matuƙar ban tsoro. Rabon da irin haka ya faru tun lokacin harin Boko Haram a barikin a shekarar 2014.”

Ya ƙara da cewa, “Alhamdulillah, ba mu samu labarin mutuwar fararen hula ba, amma akwai ƙaruwar fargabar cewa rayuwar sojoji da waɗanda ake tsare da su a barikin na cikin haɗari sosai.”

 

Ba hari ba ne — ’Yan sanda

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno ta bayyana cewa fashewar da ta faru, ba harin abokan gaba ba ne.

Kakakin rundunar, Kenneth Nahum Daso, ya ce bincike na farko ya nuna cewa fashewar ta samo asali ne daga ma’ajiyar makamai da ke cikin barikin.

Daso ya ce, “Bayan rahotannin fashewar da aka ji a Maiduguri, bincike na farko ya nuna cewa fashewar ta samo asali ne daga gobara a ma’ajiyar makamai da ke Barikin Giwa, ba harin makiya ba, kuma har yanzu ana ci gaba da tabbatar da tsaro,” in ji Daso.

Ya kara da cewa jami’an tsaro da kuma hukumar kashe gobara a halin yanzu suna wurin suna aiki don kashe gobarar da ta barke.

Gwamnatin Jihar Borno ta wata sanarwa daga Hukumar Kashe Gobara, karkashin Ma’aikatar Yada Labarai da Tsaro na Cikin Gida, ta tabbatar da cewa an shawo kan gobarar.

Sanarwar ta ce, “Gobarar ta shafi ma’ajiyar makamai a cikin barikin, kuma wasu makamai sun fashe, wanda ya haifar da kara mai karfi. Bincike na farko ya nuna cewa tsananin zafin da ake fama da shi a Maiduguri a wannan lokaci na shekara ƙila shi ne ya haifar da gobarar.”

Sanarwar ta kuma lura cewa tawagar hadin gwiwa ta masu ba da agajin gaggawa daga Hukumar Kashe Gobara ta Sojojin Najeriya, Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, da Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Borno sun mayar da martani cikin gaggawa kuma sun yi nasarar kashe gobarar.

 

Tsananin zafin rana ne ya haifar da fashewar — Sojoji

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da cewa fashewar ba harin ’yan ta’adda ba ne, sai dai sakamakon tsananin zafin rana.

Muƙaddashin Mataimakin Daraktan hulda da jama’a na rundunar HADIN KAI, Kyaftin Reuben Kovangiya, ya ce, “Tsananin zafin da ake fama da shi a Maiduguri a halin yanzu ya haifar da fashewar wasu harsasai a rumbum ajiyar makamai,” amma an shawo kan lamarin cikin gaggawa ta hanyar hadin gwiwar Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Borno da sauran masu ba da agajin gaggawa.

Ya ce, “An tura dakaru domin tabbatar da doka da oda tare da hana miyagun mutane amfani da halin da ake ciki.”

Kovangiya ya bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, ya kuma ba da tabbacin cewa an dauki duk matakan da suka dace don tabbatar da tsaro da kuma hana maimaituwar hakan a nan gaba.

Harin da aka taba kaiwa Barikin Giwa

A ranar 14 ga Maris, 2014, ɗaruruwan ’yan ta’adda sun kai hari mai ƙarfin gaske a Barikin Giwa da ke Maiduguri.

Daga baya, sojojin Najeriya suka sanar cewa sun yi nasarar fatattakar maharan, inda dakarun sama da na kasa suka kashe da yawa daga cikin ’yam ta’addan.

Wani ganau ya shaida wa kungiyar Amnesty International cewa mambobin kungiyar Civilian Joint Task Force (CJTF) sun kama wasu daga cikin waɗanda ake tsare da su da suka tsere a lokacin harin.

Wannan lamarin ya bar babban tabo a zukatan mazauna da yawa, kuma fashewar da ta faru kwanan nan a ranar Alhamis ta tuno musu harin na 2014, ta kuma sake tayar da fargaba a cikin al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Kashe Gobara ta ma ajiyar makamai cewa fashewar ya haifar da kashe gobara Barikin Giwa fashewar da tabbatar da Jihar Borno yan ta adda a ma ajiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani guda 20, tare da riguna ruwa (life jackets) 2,000, domin rage haɗurran da ke aukuwa sakamakon ambaliya da nutsewar jirage a sassan jihar.

An ƙaddamar da jiragen ne a ƙaramar hukumar Wamakko a ranar Laraba, inda gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirin gaggawa na tallafa wa al’ummar da ke fama da illar ambaliya da haɗurra a ruwa.

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB

“Mun dauki wannan mataki bayan rahotannin da muke samu na yawaitar hatsarurruka da rasa rayuka da dukiya sakamakon jiragen katako da mutane ke amfani da su,” in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

Gwamnan ya miƙa godiya ga shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, bisa hadin kai da goyon bayan da hukumar ke bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiya, tare da inganta ayyukan ceto da agaji a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, an horar da direbobin jiragen ruwan da za su riƙa kula da su, kafin a raba su zuwa ƙananan hukumomi goma (10) da suka fi fuskantar barazanar ambaliya da suka haɗa da: Goronyo, Shagari, Sabon-Birni, Wurno, Rabah, Wamakko, Silame, Kebbe, Tambuwal da Isa.

Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa za a hukunta duk wani da ya ɗauki lodi fiye da ƙima a cikin jiragen, yana mai cewa “wannan jirage da rigar ruwa na jama’a ne, kuma wajibi ne shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar da kula da su yadda ya kamata.”

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankunan da za a rabawa jiragen sun bayyana ra’ayinsu dangane da lamarin, inda wani Tanimu Goronyo, daga karamar hukumar Goronyo, ya ce: “Gwamnatin Sakkwato ta kauce hanya.

“Abin da muke bukata a yanzu shi ne hanyoyin mota da magudanan ruwa. Ambaliya tana mamaye yankunan mu ne saboda babu hanya. Idan gwamnati ta kashe wannan kuɗi wajen gina hanya, sai an fi cin moriya.”

Shi ma wani Muhammad Kabiru, daga Silame, ya bayyana farin cikinsa da sayen jiragen, sai dai ya roƙi gwamnati da ta mai da hankali wajen gina hanyoyin mota saboda abin da suka fi buƙata ke nan.

“Mu a Silame jirgi yana da amfani, amma hanyar mota ita ce babbar buƙatar mu. Idan aka samar da ita, ambaliya ba za ta hana mu zirga-zirga ba.”

Yayin da gwamnatin Sakkwato ke ɗaukar matakan gaggawa don rage hatsarurruka da ambaliya ke haifarwa, al’umma na ci gaba da neman tsarin da zai magance tushen matsalar – musamman samar da ingantattun hanyoyi da magudanan ruwa a karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar