Aminiya:
2025-11-02@06:07:20 GMT

Gobarar rumbum makamai a Borno: Abin da ya kamata a yi

Published: 2nd, May 2025 GMT

Masana harkokin tsaro sun ja hankalin hukumomi su ɗauki matakan da suka dace, lura da abin da ke iya biyo bayan gobarar ma’ajiyar makamai a babban Barikin Sojoji na Giwa da ke Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Sun bayyana damuwa game da mummunan abin da ke iya biyo baya ta fuskoki daban-daban, tare da bayar da shawarar matakan da ya kamata a ɗauka domin daƙile ayyukan miyagu da ke iya ƙoƙarin cin gajiyar yanayin a matsayin wata dama ta aikata mugun laifi ko ta’addanci.

Damuwar ƙwararru kan ƙarsashi da karfin sojoji

Wani ƙwararre kan harkokin tsaro, Kabiru Adamu, ya ce illar wannan lamari ta wuce ɓarnar zahiri da kuma yiwuwar asarar rayuka.

Ya ce, “Lalacewar makamai, harsasai, da sauran muhimman kayan aikin soja a barikin babban asarar kayan aiki ne da ke iya shafar shirye-shiryen ayyukan soji kai tsaye da ma sauran ayyukan tsaro a yankin Arewa maso Gabas da kuma yankin Tafkin Chadi.”

Kabiru Adamu ya ƙara cewa hanyoyin samar da kayan aikin soji — waɗanda tuni suke cikin matsi saboda yanayin aiki mai wahala — za su iya samun ƙarin cikas, wanda zai sa gyarawa ya zama da wahala.

Kabiru Adamu ya kuma yi gargaɗi game da irin tasirin da lamarin zai iya yi a tunani da ƙwarin gwiwar sojoji. Ya ce, “Lamarin na iya raunana jin tsaro da kwanciyar hankalinsu, musamman tunda suna zaune ne a cikin barikin.

“Wannan na iya kawo raguwar ƙwarin gwiwa da ƙaruwar damuwa,da kuma raunana ruhin faɗa. Zai kuma iya jawo rashin amincewa da ka’idojin tsaro da kuma shugabannin da ke da alhakin tabbatar da su,” in ji shi.

Ya ƙara jaddada cewa cikas na wucin gadi da lamarin ya haifar na iya kawo tsaiko ga ayyukan rundunar Operation Hadin Kai har sai an maye gurbin kayan aiki da suka salwanta.

“Dangane da ƙoƙarin yaki da ta’addanci, wannan lamarin na iya zama koma baya. Yana iya karfafa ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP su ƙara kai wa sojoji da fararen hula hare-hare. Suna iya ganin lamarin a matsayin alamar rauni ko wata dama,” in ji shi.

Kabiru Adamu ya kuma nuna haɗarin raguwar amincewar jama’a, yana mai cewa “Ga fararen hula a Maiduguri, waɗanda tuni suke fuskantar barazanar ta’addanci koyaushe, abin da ya faru a Barikin Giwa na iya kawo fargaba game da tsaro gaba ɗaya da kuma rage sakin jiki da ikon sojoji na kare su — wanda zai iya shafar bayanan sirri da ake samu daga al’ummar yankin.”

Masanin ya kuma lura da  yiwuwar amfani da lamarin wajen yada farfaganda abokan gaba.

“Ƙungiyoyi kamar Boko Haram da ISWAP na iya nuna shi — ba tare da la’akari da ainihin dalilin ba — a matsayin nasara ko kuma wani aikin ikon Allah, su yi amfani da shi don ƙarfafa ɗaukar sabbin mayaƙa, da ƙarfafa ƙwarin gwiwa, da kuma rage amincewar jama’a ga gwamnati da jami’an tsaro.”

Don haka ya ce, “Dole ne sojojin su magance sakamakon lamarin cikin gaskiya da gaggawa. Karfafa ka’idojin tsaro da samar da ingantacciyar sadarwa suna da matuƙar muhimmanci wajen dawo da amincewa. Rashin yin hakan na iya ƙarfafa matsayin ’yan ta’adda da kuma tsawaita rikicin.”

Mun ɗauka harin ’yan ta’adda ne — Mazauna

Manyan fashe-fashe da ƙarar harbe-harbe da tartsatsin wuta da kuma hayaki da ke tashi sama, sakamakon gobarar ma’aajiyar makaman sun firgita mazauna unguwannin Polo, Fori, GRA, Unimaid, da sauran wurare, inda fita kan tituna, saboda fargabar yiwuwar harin Boko Haram.

Wani mazaunin gari, Adamu Yusuf, ya ce fashewar farko ta faru ne da tsakar dare, sai kuma harbe-harbe da suka biyo baya waɗanda suka kara musu tsoro.

Ya ce, “Mun yi magana da wani tsohon soja wanda ya kira abokin aikinsa a barikin, ya tabbatar da cewa gobara ce ta tashi a ma’ajiyar makamai. Amma karar hare-haren da ya biyo baya ya sa mana shakku.”

Kyari Bulama, wani makwabcin barikin, ya ce ƙarar fashewar da habe-harben ne suka tashe shi daga barci. Ya ce, “Mun zaci harin Boko Haram ne, muka yi ta guje-guje a gidan. Abin ya fi ban tsoro da na fito fita waje. Kusan kowa sun fito kan tituna, motoci da Keke NAPEP na guje-gujen barin yankin.”

A Jami’ar Maiduguri, ɗaruruwan ɗalibai sun gudu daga ɗakunansu na kwana suka koma cikin gari don guje wa yiwuwar harin ’yan ta’adda.

Wani dalibi ya ce, “Fashewar ta yi matuƙar ƙarfi, kuma kamar tana ƙara kusantowa. Mun fito da gaggawa daga ɗakunan kwananmu, amma jami’an tsaro ba su iya gaya mana abin da ke faruwa ba. Daga ƙarshe, mun samu labarin cewa ma’ajiyar makaman sojoji ne ta yi gobara.”

Aisami Lawan, wani mazaunin unguwar Polo, ya ce lamarin ya tuno musu da wani harin da ya faru a baya.

Ya ce, “Akwai matuƙar ban tsoro. Rabon da irin haka ya faru tun lokacin harin Boko Haram a barikin a shekarar 2014.”

Ya ƙara da cewa, “Alhamdulillah, ba mu samu labarin mutuwar fararen hula ba, amma akwai ƙaruwar fargabar cewa rayuwar sojoji da waɗanda ake tsare da su a barikin na cikin haɗari sosai.”

 

Ba hari ba ne — ’Yan sanda

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno ta bayyana cewa fashewar da ta faru, ba harin abokan gaba ba ne.

Kakakin rundunar, Kenneth Nahum Daso, ya ce bincike na farko ya nuna cewa fashewar ta samo asali ne daga ma’ajiyar makamai da ke cikin barikin.

Daso ya ce, “Bayan rahotannin fashewar da aka ji a Maiduguri, bincike na farko ya nuna cewa fashewar ta samo asali ne daga gobara a ma’ajiyar makamai da ke Barikin Giwa, ba harin makiya ba, kuma har yanzu ana ci gaba da tabbatar da tsaro,” in ji Daso.

Ya kara da cewa jami’an tsaro da kuma hukumar kashe gobara a halin yanzu suna wurin suna aiki don kashe gobarar da ta barke.

Gwamnatin Jihar Borno ta wata sanarwa daga Hukumar Kashe Gobara, karkashin Ma’aikatar Yada Labarai da Tsaro na Cikin Gida, ta tabbatar da cewa an shawo kan gobarar.

Sanarwar ta ce, “Gobarar ta shafi ma’ajiyar makamai a cikin barikin, kuma wasu makamai sun fashe, wanda ya haifar da kara mai karfi. Bincike na farko ya nuna cewa tsananin zafin da ake fama da shi a Maiduguri a wannan lokaci na shekara ƙila shi ne ya haifar da gobarar.”

Sanarwar ta kuma lura cewa tawagar hadin gwiwa ta masu ba da agajin gaggawa daga Hukumar Kashe Gobara ta Sojojin Najeriya, Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, da Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Borno sun mayar da martani cikin gaggawa kuma sun yi nasarar kashe gobarar.

 

Tsananin zafin rana ne ya haifar da fashewar — Sojoji

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da cewa fashewar ba harin ’yan ta’adda ba ne, sai dai sakamakon tsananin zafin rana.

Muƙaddashin Mataimakin Daraktan hulda da jama’a na rundunar HADIN KAI, Kyaftin Reuben Kovangiya, ya ce, “Tsananin zafin da ake fama da shi a Maiduguri a halin yanzu ya haifar da fashewar wasu harsasai a rumbum ajiyar makamai,” amma an shawo kan lamarin cikin gaggawa ta hanyar hadin gwiwar Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Borno da sauran masu ba da agajin gaggawa.

Ya ce, “An tura dakaru domin tabbatar da doka da oda tare da hana miyagun mutane amfani da halin da ake ciki.”

Kovangiya ya bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, ya kuma ba da tabbacin cewa an dauki duk matakan da suka dace don tabbatar da tsaro da kuma hana maimaituwar hakan a nan gaba.

Harin da aka taba kaiwa Barikin Giwa

A ranar 14 ga Maris, 2014, ɗaruruwan ’yan ta’adda sun kai hari mai ƙarfin gaske a Barikin Giwa da ke Maiduguri.

Daga baya, sojojin Najeriya suka sanar cewa sun yi nasarar fatattakar maharan, inda dakarun sama da na kasa suka kashe da yawa daga cikin ’yam ta’addan.

Wani ganau ya shaida wa kungiyar Amnesty International cewa mambobin kungiyar Civilian Joint Task Force (CJTF) sun kama wasu daga cikin waɗanda ake tsare da su da suka tsere a lokacin harin.

Wannan lamarin ya bar babban tabo a zukatan mazauna da yawa, kuma fashewar da ta faru kwanan nan a ranar Alhamis ta tuno musu harin na 2014, ta kuma sake tayar da fargaba a cikin al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Kashe Gobara ta ma ajiyar makamai cewa fashewar ya haifar da kashe gobara Barikin Giwa fashewar da tabbatar da Jihar Borno yan ta adda a ma ajiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Sai dai don neman cimma burinta na “sake mayar da kasar Amurka zakaran gwajin dafi”, kasar Amurka ta sha daukar matakai na dakile ci gaban kasar Sin, ciki har da katse huldar tattalin arziki da ita da ma sanya takunkumai ga kamfanoninta masu ci gaban kimiyya da sauransu, duk da hakan, kasar Sin ta kiyaye bunkasar tattalin arzikinta yadda ya kamata, har ma karuwar tattalin arzikinta ta kai kaso 5.2% a cikin watanni tara na farkon bana, lamarin da ya shaida inganci da juriya na tattalin arzikin kasar. A kwanan nan, kasar Sin ta zartas da shawarwarin da aka gabatar game da tsara shirin raya tattalin arziki da zaman al’umma cikin shekaru biyar masu zuwa, kuma bisa ga shawarwarin, za a tsara shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15 na kasar. Cikin sama da shekaru 70 da suka wuce, kasar Sin ta yi ta kokarin aiwatar da shirye-shiryen ba tare da kasala ba, ba don neman kalubalantar wata ko maye gurbinta ba, amma don mai da hankali a kan raya kanta da kuma bayar da damammaki na samun ci gaba ga sauran kasashen duniya.

 

Ganawar da aka yi a wannan karo ta kasance ta farko a tsakanin shugabannin kasashen biyu tun bayan da shugaba Trump ya sake hawa karagar mulkin kasar Amurka. Kafin wannan kuma, shugabannin biyu sun taba tattaunawa da juna ta wayar tarho har sau uku, don nuna alkiblar bunkasar huldar kasashensu. Tun bayan watan Mayun da ya gabata, bisa daidaiton da shugabannin biyu suka cimma, tawagogin kasashen biyu sun gudanar da shawarwarin tattalin arziki da cinikayya har sau biyar. A sabon zagayen shawarwarin da aka gudanar a baya bayan nan a birnin Kuala Lumpur, sassan biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan batutuwan tattalin arziki da ciniki da ke janyo hankulansu duka, tare da cimma matsaya daya a kan matakan da za a dauka. Lallai ta hanyar yin shawarwari da juna cikin daidaito, sassan biyu sun kai ga karfafa fahimtar juna da amincewa da juna, hakan kuma ya shaida cewa, yin shawarwari da juna ya fi yin gaba da juna, kuma Sin da Amurka suna iya raya kansu tare da tabbatar da ci gabansu na bai daya.

 

Kasancewarsu kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, alhakin da ke rataya a wuyan Sin da Amurka ne su gano hanyar da ta dace ta cudanya da juna. Kasashen biyu za su iya karfafa ginshikin huldarsu da samar da kyakkyawan yanayi na bunkasa kansu, tare da samar da karin tabbas da kwarin gwiwa ga duniya, muddin sun tabbatar da daidaiton da shugabanninsu suka cimma, kuma suka yi hangen nesa tare da nacewa ga yin shawarwari da juna wajen daidaita sabaninsu, da kuma inganta hadin gwiwarsu da mu’amala da juna a kai a kai.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayinmu Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu October 17, 2025 Ra'ayinmu Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai October 10, 2025 Ra'ayinmu Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan September 7, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri
  • Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati