Wata 11 da tuɓe rawanin wasu sarakuna a Sakkwato
Published: 18th, March 2025 GMT
An shiga wata 11 da Gwamnatin Jihar Sakkwato ƙarƙashin Gwamna Ahmad Aliyu ta tuɓe rawanin wasu sarakuna da take ganin sun yi abin da bai dace ba na shiga siyasa.
Tun bayan cire sarakunan, mutane sun yi tsammanin gwamnati za ta nada wadanda take muradi ne kai-tsaye domin su maye gurbin tubabbun sarakunan, amma shiru kamar ba wasu da ke jiran hukunci da sakayyar gwamnati mai ci.
Har yanzu gwamnati ba ta fito ta fadi dalilin rashin sake nada sababbin sarakunan ba domin ci gaba da wakilcin jama’a, ganin an bar garin kufai ba cikakken basarake.
A baya da ma sarukanan da aka tube sun jima suna dakon sakamakon bincikensu da gwamnatin ke yi, sai dai wasu jama’a musamman na ɓangaren jam’iyyar adawa na ganin bita da ƙulli ne gwamnatin ta yi musu.
Kakakin Gwamnatin Jihar Sakkwato, Abubakar Bawa ya ce, wadanda aka sauke daga mukamansu sun hada da iyayen kasar Unguwar Lalle da Yabo da Wamakko da Tulluwa da Illela da Dogon Daji, da Kebbe da Alkammu da Tambuwal da na Giyawa, a kananan hukumomi 10 na jihar.
Haka kuma an tube wasu iyayen kasa shida bisa dalilin cewa lokacin da aka nada su, an yi gaggawa ba a bi ka’ida ba.
Sai kuma wasu biyu da aka sauya wa wurin aiki, wadanda daya daga cikinsu ‘dan majalisar Sarkin Musulmi ne da sabon Magajin Gari da aka mayar masa sarautarsa ta da, yayin da za a ci gaba da gudanar da bincike a kan wasu iyayen kasar hudu.
Har ila yau, an amince da wasu iyayen ƙasa tara daga cikin wadanda aka bincika a kan su ci gaba da aikinsu.
To sai dai wasu jama’ar jiha musamman na ɓangaren jam’iyar adawa ta PDP na ganin wannan bai zo da mamaki ba domin da ma a cewarsu wannan gwamnatin ta ƙudiri aniyar cin zarafin sarakuna iyayen al’umma.
Hassan Sahabi Sanyinnawal kakakin jam’iyar ta adawa ce inda ya ce, rashin sanin aiki ne gwamnati ta ce, an naɗa wasu sarakuna ba bisa ka’ida ba.
Amma shi kuwa kakakin Gwamnatin Jihar Sakkwato kuma kakakin Jam’iyar APC mai mulki, Sambo Bello Danchadi ya ce, abin da gwamnati ta yi a kan ka’ida yake.
Jama’a da dama sun tofa albarkacin bakinsu a kan wannan lamarin, inda wasu suke ganin an yi daidai, duba da dalilan da aka bayar na tube sarakunan wasu kuma na ganin akasin haka, yayin da sauran iyayen kasa hudu da ake ci gaba da bincike a kansu ke dakon jiran sakamako.
An jima dai ana zargin sarakuna da tsoma hannu ga lamuran siyasa a Nijeriya, abin da kuma wasu lokuta yakan zo musu da mummunan sakamako.
Gaba dyaya gwamnati ta fita batun wannan lamari wanda ake ganin akwai buƙatar a tuna wa gwamnati domin lamari ne mai girma a wannan lokaci na matsalar tsaro, a ƙyale wasu jama’a ba cikakken sarki da ke kula da shige ficensu a yankinsu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Ma’aikatar Gona da tsaron abinci ta ƙasa ta dakatar da shirinta na gudanar da addu’a da azumi na kwanaki uku, bayan martani mai zafi daga jama’a. Tun da farko, an tsara addu’ar ne domin neman taimakon Ubangiji wajen tabbatar da tsaron (wadataccen) abinci a Nijeriya.
Wata takarda da ta bayyana ga jama’a, wadda Daraktar Gudanarwa ta Ma’aikatar, Mrs. Adedayo Modupe O., ta sanya wa hannu, ta gayyaci daraktoci da sauran manyan ma’aikata domin halartar wannan taron addu’a a shalƙwatar ma’aikatar a Abuja, a ranakun 16, 23 da 30 ga Yuni, 2025.
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025Sai dai cikin wata sabuwar sanarwa daga wannan darakta, an bayyana cewa an dakatar da shirin addu’ar har sai wani lokaci na gaba, ba tare da bayyana dalilin janye umurnin ba. Wannan matakin ya biyo bayan suka da jama’a suka yi a kafafen sada zumunta kan dacewar shirin.
Masu sukar sun bayyana cewa gwamnati ya kamata ta mai da hankali wajen samar da tsare-tsare na zahiri kamar gyaran dabarun noma, da tallafawa manoma da kuma inganta rarraba abinci, maimakon dogaro da addu’a wajen shawo kan matsalar yunwa da hauhawar farashin abinci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp