Gwamnan Neja Ya Musanta Rikici Da Mataimakinsa.
Published: 2nd, May 2025 GMT
Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago ya bayyana dangantakarsa da mataimakinsa, Kwamared Yakubu Garba a matsayin cikakkiya da jituwa.
Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai kan dangantakarsa da mataimakinsa bayan bikin ranar ma’aikata a Minna.
A cewarsa, “mu kungiya ce, ba za su iya karya mu ba, hankalinmu yana kan manufa, kuma za mu cimma ta.
Gwamnan ya bukaci al’ummar jihar da su ci gaba da marawa gwamnatinsa baya, tare da tabbatar da cewa wata sabuwar Nijar za ta yiwu.
Binciken da aka gudanar ya nuna cewa mataimakin gwamnan jihar Neja, Kwamared Yakubu Garba bai halarci bikin ranar ma’aikata ta bana a Minna ba wanda wasu al’ummar Nejar din suka yi zargin cewa rashin jituwar da ke tsakanin gwamnan jihar Neja da mataimakinsa tayi tsamari.
KARSHEN ALIYU LAWAL.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamna
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari
Naurorin tauraron dan adam sun nuna hoton yadda sojojin Amurka suke kara kusantar kasar venuzuwela ciki har da jiragen yaki masu kai hare-hare duk da yake cewa shugaban Amurka Dolad trump ya karyata batun da ake yi na yunkurin kai mata harin soji,
Wannan matakin yana daya daga cikin yadda sojojin ruwan Amurka suka mayar da hankali a yankin karebiya, wanda hakan ya haifar da damuwa a latin Amurka game da yiyuwar daukar matakin soji na bangare daya kan kasar Venuzuwela ba tare da izinin majalisar dinkin duniya ko kuma kasashen duniya ba,
Washington ta yi ikirarin cewa za ta kai hari kan masu fataucin miyagun kwayoyi ne sai dai masu sa ido kan alamuran yankin sun bayyana cewa yanayin yadda ake turawa da sojoji da makamai a yankin yana nuna shirin da ake yi ne na daukar matakin soji ko kuma matsin lamba kan gwamnati venuzuwela don ta mika wuya.
Ana sa bangaren shugaban kasar venuzuwela yayi kira ga kwamitin tsaro na majalisar dinkin duniya da ya dauki mataki kan harin da Amurka ta kai kan wasu jirage dake kusa da ita a matsayin haramtacce kuma ta kare yancin kasar venuzuela
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025 Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci