Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-01@09:19:41 GMT

Gwamnan Neja Ya Musanta Rikici Da Mataimakinsa.

Published: 2nd, May 2025 GMT

Gwamnan Neja Ya Musanta Rikici Da Mataimakinsa.

Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago ya bayyana dangantakarsa da mataimakinsa, Kwamared Yakubu Garba a matsayin cikakkiya da jituwa.

 

Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai kan dangantakarsa da mataimakinsa bayan bikin ranar ma’aikata a Minna.

 

A cewarsa, “mu kungiya ce, ba za su iya karya mu ba, hankalinmu yana kan manufa, kuma za mu cimma ta.

 

Gwamnan ya bukaci al’ummar jihar da su ci gaba da marawa gwamnatinsa baya, tare da tabbatar da cewa wata sabuwar Nijar za ta yiwu.

 

Binciken da aka gudanar ya nuna cewa mataimakin gwamnan jihar Neja, Kwamared Yakubu Garba bai halarci bikin ranar ma’aikata ta bana a Minna ba wanda wasu al’ummar Nejar din suka yi zargin cewa rashin jituwar da ke tsakanin gwamnan jihar Neja da mataimakinsa tayi tsamari.

 

KARSHEN ALIYU LAWAL.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16

Gwamna Lawal ya taya sabon sarki murna, tare da roƙon Allah Ya bashi hikima da ikon yin jagoranci na gari.

Ya kuma buƙace shi da ya ci gaba da bin kyawawan ɗabi’u da tafarkin tsofaffin sarakuna domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a masarautar Gusau.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
  • Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16