Gwamnan Jigawa Ya Halarci Taron Ranar Ma’aikata Ta Bana
Published: 2nd, May 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi ya bi sahun kungiyoyin kwadago domin tunawa da irin gudunmawar da ma’aikata ke bayarwa wajen ci gaban jihar Jigawa.
Da yake gabatar da jawabinsa, Gwamna Namadi ya yaba da jajircewar ma’aikatan Jigawa, inda ya bayyana ma’aikata a matsayin masu kawo ci gaba.
Ya bayyana cewa, ma’aikata a dukkan bangarori suna aiki da gaske a matsayin injin da ke ba da kuzarin motsa al’umma zuwa ga ci gaba.
Ya kuma kara jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da walwalar ma’aikata, inda ya bayar da misali da nasarorin da aka samu da suka hada da aiwatar da mafi karancin albashi na Naira 70,000, gina gidaje masu saukin kudi ga ma’aikatan gwamnati, da kuma shigar da sama da Naira biliyan 7 a cikin shirin bayar da gudunmawar fansho na jihar.
Gwamnan ya karkare da sako mai ratsa jiki ga ma’aikata, yana mai cewa, “Watakila ba za ku ji dadin aikinku dari bisa dari ba, amma ina tabbatar muku, guminku ba zai tafi a banza ba.
Kwamared Sunusi Alhassan Maigatari, wanda ya yi magana a madadin kungiyar kwadagon, ya amince da wannan ci gaba, inda ya bayyana Gwamna Namadi a matsayin gwamnan al’umma.
Ya kuma yabawa ajandar gwamnati mai dauke da abubuwa 12, wadanda suka samar da fa’idodi masu inganci da suka hada da daukar dimbin ma’aikata a sassa masu muhimmanci, shirin ba da lamuni na noma ga ma’aikata, da kafa shagunan dake sayarda kaya da rahusa domin dakile matsalolin tattalin arziki.
USMAN MZ/Dutse
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
Sojojin kasar Iran sun cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan HKI a dazuda nan nan, wayo yau lahadi a ci gaba da musayar wauta da suke yi da sojojin HKI kwanaki uku da suka gabata.
Kamfanin dillancin labaran kare kai na kasar Iran Tasnim ya nakalto sojojin kasar na cewa sun cilla makamai masu linzami da Drones a karon farko da rana ido na ganin ido a kan HKI kuma tuna makaman sun fada a inda yakamata su fada a cikin haramtacciyar kasar.
A safiyar ranar jumma’a ce sojojin HKI suka kai hare-hare kan birnin Tehran inda suka kai manya-manyan jami’an sojojin kasar ga shahada, sannan suka kashe mutane fararen hula wadanda basu da laifi.
Bayan haka ne sojojin JMI suka fara maida martani a daren Asabar da daren lahadi, amma a wannan karon sun kai hare haren ne da ranar Lahadi ido na ganin ido.
Hare-haren wadanda aka basu suna “Alkawalin gaskiya Na 3 zasu ci gaba matakar HKI ta ci gaba da kaiwa Iran hare hare.