Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-01@09:21:14 GMT

Gwamnan Jigawa Ya Halarci Taron Ranar Ma’aikata Ta Bana

Published: 2nd, May 2025 GMT

Gwamnan Jigawa Ya Halarci Taron Ranar Ma’aikata Ta Bana

Gwamna Umar Namadi ya bi sahun kungiyoyin kwadago domin tunawa da irin gudunmawar da ma’aikata ke bayarwa wajen ci gaban jihar Jigawa.

 

Da yake gabatar da jawabinsa, Gwamna Namadi ya yaba da jajircewar ma’aikatan Jigawa, inda ya bayyana ma’aikata a matsayin masu kawo ci gaba.

 

Ya bayyana cewa, ma’aikata a dukkan bangarori suna aiki da gaske a matsayin injin da ke ba da kuzarin motsa al’umma zuwa ga ci gaba.

 

Ya kuma kara jaddada kudirin gwamnatinsa na samar da walwalar ma’aikata, inda ya bayar da misali da nasarorin da aka samu da suka hada da aiwatar da mafi karancin albashi na Naira 70,000, gina gidaje masu saukin kudi ga ma’aikatan gwamnati, da kuma shigar da sama da Naira biliyan 7 a cikin shirin bayar da gudunmawar fansho na jihar.

 

Gwamnan ya karkare da sako mai ratsa jiki ga ma’aikata, yana mai cewa, “Watakila ba za ku ji dadin aikinku dari bisa dari ba, amma ina tabbatar muku, guminku ba zai tafi a banza ba.

 

Kwamared Sunusi Alhassan Maigatari, wanda ya yi magana a madadin kungiyar kwadagon, ya amince da wannan ci gaba, inda ya bayyana Gwamna Namadi a matsayin gwamnan al’umma.

 

Ya kuma yabawa ajandar gwamnati mai dauke da abubuwa 12, wadanda suka samar da fa’idodi masu inganci da suka hada da daukar dimbin ma’aikata a sassa masu muhimmanci, shirin ba da lamuni na noma ga ma’aikata, da kafa shagunan dake sayarda kaya da rahusa domin dakile matsalolin tattalin arziki.

 

USMAN MZ/Dutse

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwanan baya, kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya shirya taron bita tare da wadanda ba ’yan jam’iyyar ba, dangane da yanayin tattalin arzikin kasar, da kuma ayyukan tattalin arziki da za a aiwatar a rabin shekarar bana ta biyu, domin sauraren ra’ayoyinsu.

Xi Jinping, babban sakataren jam’iyyar ne ya shugabanci taron tare da ba da muhimmin jawabi, inda ya ce, dole ne a zage damtse wajen gudanar da ayyukan tattalin arziki a rabin shekarar bana ta biyu, kuma a tabbatar da gudanar da ayyukan ba tare da tangarda ba, kana a aiwatar da cikakken sabon tunanin raya kasa daga dukkan fannoni, da gaggauta kafa tsarin raya kasa, da kiyaye aiwatar da manufofi ba tare da matsala ba, da inganta aiwatar da manufofi tare da yin hangen nesa da sanin ya kamata.

Shugaban na Sin ya ce, ya zama wajabi a mayar da muhimmanci ga samar da guraben aikin yi, da kwantar da hankulan kamfanoni, da tafiyar da harkokin kasuwanci, da samar da tabbaci game da hasashen da ake yi kan tattalin arziki, da karfafa sayayya, da dakatar da yin takara maras dacewa, da kawar da cikas a kasuwar gida, da rungumar wani sabon tsarin ci gaba mai “zagaye biyu”, wato wanda zai tanadi amfani da kasuwar gida a matsayin jigo, tare da barin kasuwannin gida da na waje su karfafi junansu, a kokarin cimma manufar raya tattalin arziki, da zamantakewar al’ummar kasar a bana, da samun nasarar kammala shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 14. (Tasallah Yuan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato
  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16