Tattalin Arzikin Al’Ummar Kasar Sin Na Tafiya Yadda Ya Kamata A Watan Jarairu Da Fabrairu
Published: 17th, March 2025 GMT
Yau Litinin da safe, ofishin yada labarai na majalisar gudanarwa ta Sin ya kira wani taron manema labarai, inda kakakin hukumar kididdiga ta Sin, Fu Linghui ya yi bayani kan yadda tattalin arzikin kasar ke gudana a cikin farkon watanni biyu na bana da suka gabata.
Kididdiga na nuna cewa, daga watan Janairu zuwa Fabrairu na bana, masana’antar samar da kayayyaki na samun saurin bunkasa, inda ribar da kamfanoni da masana’antu da ke iya samun ribar da ta zarce dala miliyan 2.
Daga cikinsu, masana’antar ba da hidima ta fi samun bunkasuwa, inda alkaluman ci gabanta suka karu da kashi 5.6% bisa na makamancin lokacin bara, kuma adadinsu shi ma ya karu da kashi 0.4% bisa na bara. Dadin dadawa, saurin sayar da kayayyaki a kasuwa ya karu matuka, ta yadda bangaren samar da kayayyaki da zuba jari ga sana’o’in kirkire-kirkire da sabbin fasahohi suka fi samun saurin bunkasuwa. Kazalika, shige da ficen kayayyaki na samun bunkasa ba tare da tangarda ba, kuma yanayin samar da guraben ayyukan yi na samun habaka yadda ya kamata, yayin da kuma farashin kayayyaki ke raguwa idan aka kwatanta da na makamancin lokacin bara.
A takaice dai, a wadannan watanni biyu da suka gabata, tattalin arzikin al’ummar Sinawa na bunkasa yadda ya kamata da samun ci gaba a kai a kai, duba da cewa ana ta aiwatar da kyawawan manufofi daga manyan fannoni. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Da yake ƙarin haske kan muhimman sassan da aka fi bai wa fifiko, Gwamnan ya bayyana cewa, ɓangaren tattalin arziƙi da ci gaban al’umma ne suka samu kaso mafi tsoka na kasafin kuɗin, inda aka ware sama da Naira biliyan 269 don sanya hannun jari a muhimman fannoni.
Fannin ayyuka, gidaje da sufuri ne ke kan gaba da Naira Biliyan 135.9, sai ruwa, muhalli da gandun daji da aka warewa Naira Biliyan 88.4, yayin da noma, kiwo da ƙungiyoyin gama ya samu Naira biliyan 20.57.
A fannin harkokin zamantakewa, an ware Naira biliyan 80 don samar da ayyukan ci gaba da gina jama’a, inda ilimi ya samu Naira biliyan 31.9, yayinda ilimi mai zurfi ya samu Naira biliyan 17.5.
Ɓangaren kiwon lafiya ya samu Naira biliyan 25.9, wanda hakan ke nuna yadda gwamnati ke ci gaba da zuba jari wajen samar da lafiya mai inganci.
Fannin gudanarwa ya samu Naira biliyan 19.63, sannan ɓangaren doka da shari’a aka ware masa Naira biliyan 2.17, fannin filaye ya samu Naira biliyan 6.46; shi kuwa fannin Kasuwanci, Masana’antu da Yawon Buɗe Ido ya samu Naira biliyan 4.02.
Yayin da sashen matasa da ci gaban wasanni ya samu Naira biliyan 3.33; harkokin mata da ci gaban a’umma Naira biliyan 1.28; fannin yaɗa Labarai da raya al’adu kuwa Naira biliyan 10.38.
Gwamna Yahaya ya bayyana ƙididdigar kasafin kuɗin na 2026 a matsayin na ɗorawa kan ci gaban da gwamnatinsa ta faro na gudanar da shugabanci nagari, Gwamna Inuwa Yahaya ya yi ƙira ga majalisar akan ta yi nazari tare da ƙalailaice ƙudurin tare da sanya gudunmawa da tabarrukinta.
“Aikin dake gabanmu shi ne mu samarwa al’ummarmu kasafin kuɗin da zai wanzar da fatansu ya zuwa zahiri da kuma kyautata makomarsu,” in ji shi.
Kasafin kuɗin na 2026 ya dace da tsarin ci gaban Jihar Gombe (DEVAGOM) da kuma tsarin tattalin arziƙin ƙasa baki ɗaya. Da yake tsokaci kan harkokin tattalin arziƙi a dunƙule, Gwamnan ya ce sauye-sauyen da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ɓullo da su, da suka haɗa da cire tallafin man fetur da sakin mara ga canjin kuɗaɗen waje, sun fara haifar da sakamako na ƙwarai.
A nasa jawabin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Gombe Rt. Hon. Muhammad Abubakar Luggerewo, ya yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa yadda gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da bin doka da oda, da gaskiya da kuma tsantseni wajen tafiyar da harkokin kuɗaɗen gwamnati.
Ya bada tabbacin duba kasafin akan lokaci da kuma gaggauta amincewa da ƙudurin kasafin na 2026.
Rt. Hon. Luggerewo ya kuma nuna jin daɗinsa da yadda jihar ke tafiyar da harkokin kasafin kuɗi, inda ya ce aiwatar da kasafin kuɗin 2025 ya samu nasarar fiye da kaso 60 cikin 100 ya zuwa ƙarshen watan Satumba, sannan ya yaba da yadda gwamnati ta samu ci gaba a fannin samar da ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, masana’antu, da sabunta birane.
“Za mu ci gaba da tallafawa manufofi da tsare-tsaren dake tabbatar da zaman lafiya, inganta ci gaban tattalin arziki da kyautata rayuwar jama’armu,” in ji kakakin.
A shekarar da ake ciki ta 2025, Gwamnatin Inuwa ta yi kasafi ne na fiye da Naira biliyan 369.9, inda daga baya aka yi bitarsa ya koma na fiye da Naira biliyan 451.6 biyo bayan samun ƙarin kuɗaɗen shiga fiye da yadda aka yi tsammani.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA