Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa
Published: 11th, March 2025 GMT
Gamayyar ƙungiyoyin manyan makarantu na gwamnatin Jihar Adamawa sun tsunduma yajin aikin sai baba ta gani a yau Talata, 11 ga watan Maris.
Ma’aikatan manyan makarantun da suka haɗa da masu karantarwa da waɗanda ba sa karantarwa sun shiga yajin aiki ne bayan wa’adin yajin aikin gargaɗi na kwanaki bakwai da ya ƙare a jiya Litinin.
Cikin wata sanarwa da shugaba, Maryam Abdullahi da kuma sakataren ƙungiyoyin, Kwamared Musa Yakubu suka sanyawa hannu, sun alaƙanta yajin aikin a matsayin martani da halin ko-in-kula da gwamnatin jihar ta nuna kan buƙatunsu.
Dangane da hakan gamayyar ƙungiyoyin ke kiran dukkan mambobinta da su tsunduma yajin aikin na sai baba ta gani.
Aminiya ta ruwaito cewa, yajin aikin ya shafi manyan makarantu daban-daban ciki har da kwalejojin ilimi da fasaha da na lafiya da ke faɗin Jihar Adamawa.
Ƙungiyoyin dai na neman gwamnatin ta mayar da mambobinsu kan tsarin albashin manyan makarantu da kuma tsarin sabon albashi mafi ƙanƙanta da kuma janye tsarin zaftare albashinsu da ake yi da sunan haraji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Adamawa manyan makarantu Yajin aiki manyan makarantu yajin aikin
এছাড়াও পড়ুন:
Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
Gwamnatin jihar Kano ta bayyana kudirinta na tallafawa shirin inganta ilimi na bunkasa Afirka (BEAR) III, wani shiri na hadin gwiwa da hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) da Jamhuriyar Koriya suka yi.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan wayar da kan jama’a ma’aikatar ilimi ta jihar Kano Balarabe Abdullahi Kiru, yace aikin yana da nufin haɓaka ilimin fasaha da na sana’a a faɗin Afirka, tare da mai da hankali kan ƙarfafa tsarin ilimin fasaha da na sana’a da horo (TVET).
Aikin zai mayar da hankali ne kan harkar noma, tare da mai da hankali kan sarrafa kayan noma da sarrafa su bayan girbi.
A cewar Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda, shirin na BEAR III ya yi daidai da ajandar Gwamna Abba Kabir Yusuf na inganta shirye-shiryen koyon sana’o’i don dogaro da kai.
Ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnatin jihar Kano za ta ci gaba da hada gwiwa da hukumar UNESCO da kasar Koriya ta Kudu domin bunkasa koyar da sana’o’i a makarantun furamare da na gaba da sakandare a fadin jihar.
Darakta a ma’aikatar ilimi ta tarayya Dr. (Mrs) M.A Olodo ta jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano domin gudanar da taro da masu ruwa da tsaki dangane da aiwatar da shirin na BEAR III.
Ta ba da tabbacin cewa ƙungiyar za ta yi amfani da mafi kyawun lokacin da ya rage don cimma manufofin aikin.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, an gina aikin na BEAR III akan ginshikai guda uku: sanya aikin ya dace da bukatun kasashe masu cin gajiyar shirin, da inganta TVET da ake bayarwa, da kuma kyautata fahimtarsa a tsakanin matasa.
Za a gudanar da aikin a kasashe hudu na yammacin Afirka: Najeriya, Ghana, Cote d’Ivoire, da Saliyo.
Rel/ Khadijah Aliyu