Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa
Published: 11th, March 2025 GMT
Gamayyar ƙungiyoyin manyan makarantu na gwamnatin Jihar Adamawa sun tsunduma yajin aikin sai baba ta gani a yau Talata, 11 ga watan Maris.
Ma’aikatan manyan makarantun da suka haɗa da masu karantarwa da waɗanda ba sa karantarwa sun shiga yajin aiki ne bayan wa’adin yajin aikin gargaɗi na kwanaki bakwai da ya ƙare a jiya Litinin.
Cikin wata sanarwa da shugaba, Maryam Abdullahi da kuma sakataren ƙungiyoyin, Kwamared Musa Yakubu suka sanyawa hannu, sun alaƙanta yajin aikin a matsayin martani da halin ko-in-kula da gwamnatin jihar ta nuna kan buƙatunsu.
Dangane da hakan gamayyar ƙungiyoyin ke kiran dukkan mambobinta da su tsunduma yajin aikin na sai baba ta gani.
Aminiya ta ruwaito cewa, yajin aikin ya shafi manyan makarantu daban-daban ciki har da kwalejojin ilimi da fasaha da na lafiya da ke faɗin Jihar Adamawa.
Ƙungiyoyin dai na neman gwamnatin ta mayar da mambobinsu kan tsarin albashin manyan makarantu da kuma tsarin sabon albashi mafi ƙanƙanta da kuma janye tsarin zaftare albashinsu da ake yi da sunan haraji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Adamawa manyan makarantu Yajin aiki manyan makarantu yajin aikin
এছাড়াও পড়ুন:
Babu dalilin kai wa Iran farmaki — Putin
Shugaban Ƙasar Rasha, Vladimir Putin, ya ce babu wata hujja ko dalilin kai wa Iran hari.
Putin ya yi wannan furuci ne yayin wata tattaunawa da Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Agarachi a fadar Kremlin da ke birnin Moscow.
Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha Fararen hula sun yi garkuwa da sojoji 57 a ColumbiaA jawabin da ya gabatar a farkon tattaunawar wanda aka yada a gidan talabijin na gwamnatin Rasha, shugaba Putin ya ce: “Babu wata hujja ko dalili da zai sa a kai wa Iran farmaki.”
Ya ƙara da cewa “na ji daɗin zuwan ka [Agarachi] Moscow a yau. Wannan zai ba mu damar tattauna waɗannan batutuwa masu wahala da kuma hanyar shawo kan lamarin.”
A nasa jawabin, Ministan Harkokin Wajen na Iran ya ce ƙasarsa na da “ƙawance ta ƙut da ƙut” da Rasha.
Ya ce hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai wa Iran “sun saɓa wa dokoki da ƙa’idojin ƙasa da ƙasa.”
A farkon shekarar nan Iran da Rasha sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna.
Sai da ba ta haɗa da ƙawancen soji ba kuma ba ta buƙaci Rasha ta kai wa Iran ɗaukin kariya ba.