Haka kuma, an ce ta ƙara da cewa: “Mu tambayi Shugaban Majalisar Dattawa, me ya sa ya janye jami’an tsarona tun farko, idan ba don ya sa a kai min hari ba? Ya ce a kashe ni, amma a kashe ni a Kogi.”

Gwamnati ta bayyana cewa waɗannan kalaman suna da nufin ɓata suna, kuma hakan ya saɓa da Sashe na 391 na Dokar Laifuka 89, Dokokin Tarayya na shekarar 1990.

Hukuncin laifin yana ƙarƙashin Sashe na 392 na wannan doka.

A wani tuhumar daban, an zargi Sanata Natasha da yin irin waɗannan kalaman game da Akpabio a cikin wata tattaunawa ta waya da wata Sandra C. Duru a Abuja, a ranar 27 ga watan Maris, 2025.

An ƙara tsaurara tsaro a wajen kotun, inda magoya bayanta da dama suka hallara don nuna goyon baya gare ta.

Daga cikin waɗanda suka halarta akwai mijinta, Emmanuel Uduaghan; tsohuwar Ministar Ilimi, Dokta Oby Ezekwesili; da mashahuriyar mai rajin kare haƙƙin ɗan adam, Aisha Yesufu.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da tsohon Gwamna Yahaya Bello, na cikin jerin shaidu da za a kira a shari’ar.

Sanata Natasha ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba game da tuhumar a yanzu.

An ɗage sauraron ƙarar zuwa wata rana da ba a bayyana ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yahaya Bello Zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin ta sake neman Amurka, da ta daina zarginta, da dora mata laifi, ya kamata kasar Amurka ta taka rawa wajen tsagaita bude wuta, da kara azama ga gudanar da shawarwarin shimfida zaman lafiya. Jami’in ya ce, ana bukatar hadin kai wajen warware rikicin Ukraine, a maimakon rarrabuwar kawuna da yin fito-na-fito. (Tasallah Yuan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi
  • Kano Za Ta Mayar Da Gidan Yarin Kurmawa Zuwa Gidan Tarihi – Gwamnati
  • Bloomberg: FBI ta sake canza sunan Trump daga Fayilolin da ke da alaƙa da shari’ar Epstein
  • Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
  • Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
  • Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
  • An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
  • Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
  • Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine