Haka kuma, an ce ta ƙara da cewa: “Mu tambayi Shugaban Majalisar Dattawa, me ya sa ya janye jami’an tsarona tun farko, idan ba don ya sa a kai min hari ba? Ya ce a kashe ni, amma a kashe ni a Kogi.”

Gwamnati ta bayyana cewa waɗannan kalaman suna da nufin ɓata suna, kuma hakan ya saɓa da Sashe na 391 na Dokar Laifuka 89, Dokokin Tarayya na shekarar 1990.

Hukuncin laifin yana ƙarƙashin Sashe na 392 na wannan doka.

A wani tuhumar daban, an zargi Sanata Natasha da yin irin waɗannan kalaman game da Akpabio a cikin wata tattaunawa ta waya da wata Sandra C. Duru a Abuja, a ranar 27 ga watan Maris, 2025.

An ƙara tsaurara tsaro a wajen kotun, inda magoya bayanta da dama suka hallara don nuna goyon baya gare ta.

Daga cikin waɗanda suka halarta akwai mijinta, Emmanuel Uduaghan; tsohuwar Ministar Ilimi, Dokta Oby Ezekwesili; da mashahuriyar mai rajin kare haƙƙin ɗan adam, Aisha Yesufu.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da tsohon Gwamna Yahaya Bello, na cikin jerin shaidu da za a kira a shari’ar.

Sanata Natasha ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba game da tuhumar a yanzu.

An ɗage sauraron ƙarar zuwa wata rana da ba a bayyana ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yahaya Bello Zargi

এছাড়াও পড়ুন:

An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano

Wata kotun shari’ar Musulunci da ke Kofar Kudu a Jihar Kano, ta yanke wa wasu mutum bakwai hukuncin ɗauri, bayan da suka ji wa wani ɗan sanda rauni yayin da ake ƙoƙarin cafke su.

Al’ummar unguwannin Tudun Maliki da Sheka ne suka kai rahoton mutanen, inda suka zarge su da sayar da miyagun ƙwayoyi.

’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara

A kotun, an gurfanar da su kan laifukan haɗa baki domin tayar da hankali, jikkata mutum, hana ‘yan sanda yin aikinsu yadda ya dace, da kuma ɓoye wanda ake zargi.

Lauyan gwamnati, Barrista Aliya Ibrahim Aminu ce, ta karanta musu tuhumar a gaban kotu.

Ɗaya daga cikinsu ya musanta laifin, yayin da Idris Ado da wasu mutum biyar suka amsa wasu daga cikin tuhumar amma suka ƙi amincewa da sauran.

Alƙalin kotun, Khadi Shamsuddeen Ado Abdullahi Unguwar Gini, ya yanke musu hukuncin ɗaurin wata uku bisa laifin farko, da wata uku a laifi na biyu.

Haka kuma ya ƙara yanke musu hukuncin ɗaurin wata uku tare da tarar Naira 15,000.

Za a yi wa kowannensu bulala 20.

Baya ga haka kuma, kotun ta umarce su da su yi wata shida a ƙarƙashin kulawa, inda za su riƙa share magudanan ruwa a unguwanninsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan Akpabio
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
  • Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga