Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
Published: 19th, June 2025 GMT
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce matsalar da ke addabar jam’iyyar PDP ba ta tsaya kan Atiku Abubakar kaɗai ba, face tana da nasaba da girman kai tsakanin shugabannin jam’iyyar.
Da yake magana da manema labarai a ranar Laraba, Gwamna Lawal ya ce: “Kowa yana da nasa matsalar; ba kan Atiku Abubakar kawai ba ne; ta wuce hakan.
“Matsala ce daga cikin gida… Na ga matsalar tana da alaƙa da girman kai, ba a bar kowa a baya ba.”
Da aka tambaye shi ko yana daga cikin masu haddasa matsala a cikin jam’iyyar, ya amsa cewa yana ciki.
Gwamna Lawal, wanda shi ne gwamnan PDP na farko a Jihar Zamfara, ya ce yana da yaƙinin cewa har yanzu za a iya gudanar da zaɓe na gaskiya a Najeriya.
“E, har yanzu za a iya gudanar da zaɓe na gaskiya… Shi ya sa aka zaɓe ni a matsayin gwamnan Jihar Zamfara.”
PDP na fama da rikici tun bayan rashin nasararta a zaɓen 2023. Manyan ’yan jam’iyyar da dama sun sauya sheƙa zuwa APC, ciki har da gwamnoni daga jihohin Akwa Ibom da Delta. Wannan ya rage ƙarfin jam’iyyar a wasu yankuna.
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya fara tuntubar wasu manyan ’yan siyasa irin su Peter Obi da Nasir El-Rufai don kafa haɗaka kafin zaɓen 2027.
Ya ce yana yin haka ne domin guje wa Najeriya komawa jam’iyya ɗaya.
Amma wasu jagororin PDP ba sa goyon bayan wannan ƙawancen.
Jigo a jam’iyyar, Bode George, ya ce yana da kyakkyawan fata cewa PDP za ta iya warware rikicinta na cikin gida kafin taron jam’iyyar karo na 100.
INEC ta ƙi aminta da babban taron PDPA gefe guda kuma, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, (INEC), ta ƙi amincewa da gayyatar taronta saboda rashin cika sharuɗan da doka ta gindaya.
Gayyatar ta samu sa hannun mukaddashin shugaban jam’iyyar kaɗai, ba tare da na sakataren jam’iyyar ba, wanda doka ta buƙata.
Ana sa ran taron da aka tsara yi a ranar 30 ga watan Yuni, 2025 zai tattauna kan rikice-rikicen PDP na cikin gida, batun shugabanci, da kuma yadda za a ware tikitin takarar shugaban ƙasa na 2027, inda wasu ’yan jam’iyyar, musamman G5, ke buƙatar a bai wa Kudu damar yin takara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Lawal Siyasa taro Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
Da take aiwatar da rahotannin sirri cikin gaggawa, rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an ‘yansandan Nijeriya, Sojoji, jami’an kula da jama’a na jihar, da ’yan banga na yankin sun bi sawun barayin da suka tsere zuwa Dutsen Falale da ke yankin Kurfi-Safana inda aka yi musayar wuta mai tsanani, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan bindigar 12.
Sai dai kuma, yayin da yake yabawa wannan bajinta da jajircewa da jami’an tsaron suka yi, Dakta Mua’zu ya bayyana matukar alhininsa game da rasuwar wani dan banga mai suna Alhaji Danmalam wanda ya rasa ransa a fafatawar.
Bugu da kari, soja guda ya samu raunuka kuma a halin yanzu yana samun kulawa a Asibiti.
Alhaji Danmalam ya rasu ne sakamakon harbin bindiga a cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko da ke Charanchi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp