Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal
Published: 19th, June 2025 GMT
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce matsalar da ke addabar jam’iyyar PDP ba ta tsaya kan Atiku Abubakar kaɗai ba, face tana da nasaba da girman kai tsakanin shugabannin jam’iyyar.
Da yake magana da manema labarai a ranar Laraba, Gwamna Lawal ya ce: “Kowa yana da nasa matsalar; ba kan Atiku Abubakar kawai ba ne; ta wuce hakan.
“Matsala ce daga cikin gida… Na ga matsalar tana da alaƙa da girman kai, ba a bar kowa a baya ba.”
Da aka tambaye shi ko yana daga cikin masu haddasa matsala a cikin jam’iyyar, ya amsa cewa yana ciki.
Gwamna Lawal, wanda shi ne gwamnan PDP na farko a Jihar Zamfara, ya ce yana da yaƙinin cewa har yanzu za a iya gudanar da zaɓe na gaskiya a Najeriya.
“E, har yanzu za a iya gudanar da zaɓe na gaskiya… Shi ya sa aka zaɓe ni a matsayin gwamnan Jihar Zamfara.”
PDP na fama da rikici tun bayan rashin nasararta a zaɓen 2023. Manyan ’yan jam’iyyar da dama sun sauya sheƙa zuwa APC, ciki har da gwamnoni daga jihohin Akwa Ibom da Delta. Wannan ya rage ƙarfin jam’iyyar a wasu yankuna.
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya fara tuntubar wasu manyan ’yan siyasa irin su Peter Obi da Nasir El-Rufai don kafa haɗaka kafin zaɓen 2027.
Ya ce yana yin haka ne domin guje wa Najeriya komawa jam’iyya ɗaya.
Amma wasu jagororin PDP ba sa goyon bayan wannan ƙawancen.
Jigo a jam’iyyar, Bode George, ya ce yana da kyakkyawan fata cewa PDP za ta iya warware rikicinta na cikin gida kafin taron jam’iyyar karo na 100.
INEC ta ƙi aminta da babban taron PDPA gefe guda kuma, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, (INEC), ta ƙi amincewa da gayyatar taronta saboda rashin cika sharuɗan da doka ta gindaya.
Gayyatar ta samu sa hannun mukaddashin shugaban jam’iyyar kaɗai, ba tare da na sakataren jam’iyyar ba, wanda doka ta buƙata.
Ana sa ran taron da aka tsara yi a ranar 30 ga watan Yuni, 2025 zai tattauna kan rikice-rikicen PDP na cikin gida, batun shugabanci, da kuma yadda za a ware tikitin takarar shugaban ƙasa na 2027, inda wasu ’yan jam’iyyar, musamman G5, ke buƙatar a bai wa Kudu damar yin takara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Lawal Siyasa taro Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansu
Rundunar ’yan sandan Jihar Neja ta kama wasu mutane tara da ake zargi da shirin yin garkuwa da kansu tare da neman kuɗin fansa Naira miliyan 7.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Wasiu Abiodun ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, inda ya ce waɗanda ake zargin na da hannu a cikin shirin zamba na Ponzi, kuma ɗaya daga cikin tawagarsu ya shirya da wanda ake zargin ya samu kuɗin fansa daga abokan aikinsu.
An kama sojan bogi da ɓarayin mota 2 a Jigawa Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin ministaAn kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin mai suna Suleiman Dauda a Minna babban birnin jihar, inda daga bisani ya ambaci wasu mutum takwas da ake zargin yayin da ’yan sanda ke yi musu tambayoyi.
“A ranar 2 ga Satumba, 2025, da misalin ƙarfe 10 na dare, an samu rahoto a yankin Tudun-Wada na wani da ake zargi da yin garkuwa da mutane a kusa da unguwar Mandela da ke Minna, sannan kuma an kira shi ta wata baƙuwar lambar wayar salula ana neman kuɗin fansa Naira miliyan 7.
“A cikin binciken da ake yi, a ranar 3 ga Satumba 2025, an kama wani wanda ake zargi mai suna Suleiman Dauda da laifin aikata laifin, kuma bisa ga tambayoyi, an kama wasu mutum takwas a unguwar Mandela.
“A binciken da aka yi, an ƙwato katin wayar salula SIM guda 21 da satifiket 29 a hannun Suleiman, bisa zargin cewa yana yin rijistar katin SIM ne, ya kuma yarda cewa lambar waya salula da ake neman kuɗin fansa ya ba wanda aka aka yi garkuwan da shi.”
Duk da haka ya bayyana cewa, “Binciken da aka yi ya nuna cewa, waɗanda ake zargin sun fito ne daga wurare daban-daban a ciki da wajen jihar suna gudanar da shirin zamba na Ponzi, kuma an gano cewa ɗaya daga cikin tawagarsu ya shirya da wanda ake zargin ya karɓi kuɗin fansa daga abokan aikinsu.
Abiodun ya bayyana cewa ana ci gaba da gudanar da bincike da nufin ganowa tare da cafke wasu, yana mai cewa waɗanda ake zargin an gurfanar da su a gaban kotu.