Aminiya:
2025-11-03@07:23:17 GMT

Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal

Published: 19th, June 2025 GMT

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce matsalar da ke addabar jam’iyyar PDP ba ta tsaya kan Atiku Abubakar kaɗai ba, face tana da nasaba da girman kai tsakanin shugabannin jam’iyyar.

Da yake magana da manema labarai a ranar Laraba, Gwamna Lawal ya ce: “Kowa yana da nasa matsalar; ba kan Atiku Abubakar kawai ba ne; ta wuce hakan.

An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano ’Yan bindiga sun kashe manoma 24 a Katsina

“Matsala ce daga cikin gida… Na ga matsalar tana da alaƙa da girman kai, ba a bar kowa a baya ba.”

Da aka tambaye shi ko yana daga cikin masu haddasa matsala a cikin jam’iyyar, ya amsa cewa yana ciki.

Gwamna Lawal, wanda shi ne gwamnan PDP na farko a Jihar Zamfara, ya ce yana da yaƙinin cewa har yanzu za a iya gudanar da zaɓe na gaskiya a Najeriya.

“E, har yanzu za a iya gudanar da zaɓe na gaskiya… Shi ya sa aka zaɓe ni a matsayin gwamnan Jihar Zamfara.”

PDP na fama da rikici tun bayan rashin nasararta a zaɓen 2023. Manyan ’yan jam’iyyar da dama sun sauya sheƙa zuwa APC, ciki har da gwamnoni daga jihohin Akwa Ibom da Delta. Wannan ya rage ƙarfin jam’iyyar a wasu yankuna.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya fara tuntubar wasu manyan ’yan siyasa irin su Peter Obi da Nasir El-Rufai don kafa haɗaka kafin zaɓen 2027.

Ya ce yana yin haka ne domin guje wa Najeriya komawa jam’iyya ɗaya.

Amma wasu jagororin PDP ba sa goyon bayan wannan ƙawancen.

Jigo a jam’iyyar, Bode George, ya ce yana da kyakkyawan fata cewa PDP za ta iya warware rikicinta na cikin gida kafin taron jam’iyyar karo na 100.

INEC ta ƙi aminta da babban taron PDP

A gefe guda kuma, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, (INEC), ta ƙi amincewa da gayyatar taronta saboda rashin cika sharuɗan da doka ta gindaya.

Gayyatar ta samu sa hannun mukaddashin shugaban jam’iyyar kaɗai, ba tare da na sakataren jam’iyyar ba, wanda doka ta buƙata.

Ana sa ran taron da aka tsara yi a ranar 30 ga watan Yuni, 2025 zai tattauna kan rikice-rikicen PDP na cikin gida, batun shugabanci, da kuma yadda za a ware tikitin takarar shugaban ƙasa na 2027, inda wasu ’yan jam’iyyar, musamman G5, ke buƙatar a bai wa Kudu damar yin takara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Lawal Siyasa taro Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Maganin Nankarwa (3)

Yawan shafa man kade a wurin ma yana rage ta sosai.

Daga karshe Ina kira ga mata da su daure da zarar sun haihu su fara neman hanyan magance wannan matsalar kuma ku sani cewa wannan hadin gargajiya ne babu Kemikal a cikinsa don haka yana daukar lokaci kafin a ga canji kamar, sati biyu idan ba ki ga canji ba sai ki dauki wani kuma.

Allah shi ne masani. Allah yasa mu dace.

Ga hanyoyi guda 5 da za’a iya magance su a saukake ba tare da amfani da mayuka masu illlata fata ba

Hanya ta 1: Dankalin Hausa

Dankali yana dauke da sinadarin sitaci da yake lausasa fata da kuma sinadarin da yake hana fata lalacewa wato antiodidant. Haka kuma dankali yana dauke da sinadarin bitamin C, potassium, thiamin, riboflabin, iron, zinc da sauran su.

Yanda ake amfani da shi:

A yanka Dankali sannan a shafa a hankali a kan Nankarwar. Sai a bar shi na tsawon mintuna 15 zuwa 20, sannan a wanke da ruwan dumi. A maimaita haka a kullum

Hanya ta 2: Alo bera

Ruwan da ke cikin Alo bera yana dauke da sinadarin Collagen wanda aka san shi da gyara fatar da ta lalace da kuma kara laushin ta, kyanta da kuma yarintar ta.

Yanda ake amfani da shi:

A karya itacen Alo bera guda sai a shafa ruwan a kan Nankarwa. A bar shi tsawon awa 2 zuwa uku sai a wanke da ruwa. A maimata hakan a kullum har sai an samu sakamako mai kyau.

Hanya ta 3: Man kadanya da koko Bota

Hadin man kadanya da koko Bota yana dauke da sinadarin bitamin E da kuma sinadaran da ke hana fata lalacewa

Yadda ake amfani da shi

Za’a samu Koko Bota karamin cokali 2, da man kadanya shima karamin cokali 2, sai sinadarin Bitamin E karamin cokali 1. Za’a narka man kadanya da kuma man koko Bota sai a kara bitamin E din a ciki a gauraya. Za’a dura gaba daya a cikin mazubi a ajiye ana shafawa a kan Nankarwar kullum.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Labarai Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar