A nasu ɓangaren, ƙungiyar kare haƙƙin Musulmi, MURIC, ta gargaɗi APC da Shugaba Tinubu da kada su sauya Shettima a matsayin mataimaki a 2027.

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce duk wani yunkuri na cire Shettima zai zama matakin da bai dace ba kuma ya kamata a nemi shawara daga manyan masu ruwa da tsaki kafin ɗaukar kowanne mataki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dortmund ta yi canjaras da Fluminense a Club World Cup

Borussia Dortmund ta soma buɗe wasanninta na gasar FIFA Club World Cup da canjaras a karon-battar da ta yi da kungiyar Fluminense ta Brazil a ranar Talata.

Ana dai ganin babbar kungiyar da ta zama gagarabadau a Rio de Janeiro Fluminense a matsayin mafi hatsari a rukunin F wanda ya kunshi har da kungiyar Ulsan HD ta Koriya ta Kudu.

Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump

An dai rika kai wa juna hari a yayin wasan da suka barje gumi a filin wasa na Metlife da ke East Rutherford a wajen birnin New York, sai dai mai tsaron ragar Dortmund, Gregor Kobel ya ceci kungiyarsa bayan wata kwallo da Jhon Arias ya nano masa daga nesa tun kafin tafiya hutun rabin lokaci.

Fluminense wadda tsohon dan wasan PSG da Chelsea, Thiago Silva mai shekaru 40 shi ne kyaftin dinta, ta yi kokarin samun damar Dortmund ana tsaka da kai ruwa na bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, amma Kobel ya rike kwallon da Agustin Canobbio ya yi yunkurin tarar numfashinsa.

Golan dai ya sake yin wata bajintar bayan ya tare kwallon da Everaldo ya yi sakada masa a kusurwar kasa, lamarin da haka a karkare wasan babu ci.

Fluminense dai ta samu gurbin zuwa gasar Club World Cup ta bana bayan nasarar lashe Copa Libertadores da ta yi a shekarar 2023.

Bajintar da Fluminense ta yi a karon-battar ta da manyan kungiyoyin da suka kasance zakaran gwajin dafi a nahiyyar Turai ya kara tabbatar da cewa tana iya tabuka abin a-zo-a-gani a gasar Club World Cup ta bana da aka sauyawa fasali.

Dortmund za ta yi fatan samun nasara a wasan gaba da za ta fafata da kungiyar Mamelodi Sundowns ta Afirka ta Kudu.

AFP

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’
  • Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
  • Tinubu na ƙaddamar da wasu ayyuka a Jihar Kaduna
  • Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
  • Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu
  • Dortmund ta yi canjaras da Fluminense a Club World Cup