Kar a kuskura a shiga cikin yaƙin Iran da Isra’ila — MDD
Published: 19th, June 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi kan kada a kuskura a shiga tsakanin yaƙin da Iran da Isra’ila ke fafatawa ta hanyar amfani da ƙarfin soji.
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi gargadi kan duk wani “shiga tsakani na soji”, a yankin Gabas ta Tsakiya, inda manyan abokan gaba Isra’ila da Iran ke musayar wuta a rana ta shida.
Ita ma ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta bukaci bangarorin biyu, da su kare fararen hula yayin da adadin mace-mace da jikkata ke ci gaba da karuwa.
Babbar sakatariyar ƙungiyar ta kasa da kasa, Agnes Callamard wadda ta yi wannan kira, ta buƙaci Iran da Isra’ila da su martaba haƙƙoƙin jama’a, tare da tabbatar da cewa ba fararen hula a ƙasashen biyu ne ake gasa wa tsakuwa a hannu sakamakon wannan rikici ba.
Rikicin dai ya fara ne a ranar Juma’a, lokacin da Isra’ila ta ƙaddamar da wani gagarumin harin bama-bamai wanda ya sanya Iran mayar da martani da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa.
Tuni dai jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana cewa ƙasarsa ba za ta amince da ƙarfa-ƙarfan zaman lafiya ba, yana mai gargaɗin Amurka cewa muddin ta kai musu hari, to za ta ɗanɗana kuɗarta.
Kalamansa na zuwa ne a yayin da Isra’ila ta ce ta kai hari kan wurare 40 a cikin Iran a wannan Larabar da suka haɗa da masana’antar ƙera makamai, yayin da ita ma Iran ta kadddamar da farmakin jirage marasa matuka kan Isra’ila.
A ɓangare guda, Rasha da Amurka na ganawa da juna da zummar lalubo zaren warware rikicin kamar yadda mataimakin Ministan Harkokin Wajen Rasha, Sergei Ryabkov ya bayyana.
Tun da farko ya gargaɗin cewa, muddin Amurka ta shiga cikin yaƙin kai-tsaye domin taimaka wa Isra’ila, to babu shakka hakan zai sake jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin ruɗani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iran Isra ila da Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila
Kafofin yaɗa labarai na cikin gida a Iran sun yi iƙirarin cewa ƙasar ta kai hari kan hedikwatar hukumar leƙen asiri ta ƙasar Isra’ila (Mossad).
Kamfanin dillancin labaran Iran (TASNIM) ya ruwaito cewa rundumar juyin juya hali na Iran (IRGC) ce ta kai harin a hedikwatar Mossad da ke Herzliya.
Kamfanin ya wallafa wasu jerin hotuna da ya ce suna nuna yadda hedikwatar ta Mossad ke ci da wutan ne bayan harin makamai masu linzami ne da Iran ta kai mata.
Kafar yaɗa labarai ta Tehran Times ta ruwaito cewa hare-haren na IRGC sun ƙona wani ɓangare na cibiyar Aman, wanda wani ɓangare ne na ginin hukumar leƙen asirin asirin sojin Isra’ila ta Aman, da ke Glilot.
An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran Sarki ya yi barazanar hana yin Musulunci a garinsa bayan dodanni sun kai wa Musulmi hariKawo yanzu dai ba a iya tantance sahihancin wannan iƙirarin na Iran ba daga kafofin yaɗa labarai da ke aiki a yankin; kuma hukumomin Isra’ila ba su ce uffan a kai ba.
A cewar hukumar kare haƙƙin ɗan’Adam a Iran (HRANA), fararen hula 224 ne suka mutu, yayin da 188 suka jikkata a hare-haren Isra’ila a ƙasar.
HRANA ta kuma bayyana cewa sojoji 109 ne suka mutu inda kuma 123 suka jikkata.